Sashe 32
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A fusace ta miqe bata damu da lallen ta da be gama shan iska ba ta yayibi mayafi da jakarta tayi waje Nuratu taja tsaki ta koma ta ci gaba da wanke lallenta a ranta tana takaicin halin qanwar tata da duk inda akaje seta siyar da Hali, tana guje mata taje cikin dangin miji tayi musu wannan haukan tabbas babu inda auranta zeje dan babu Namijin da ze yarda ta ringa wulaqanta masa yan uwa haka.
A waje kuwa a fusace Umaimah ta qarasa inda ta Hango motar Khalil, bawan Allah daya sha gayunsa ya fito da murmushi amma ganin fuskarta a dinke kamar Hadirin August yasa ya tsaya daga inda yake harta qaraso
"Mu tafi" ta fada tana qoqarin kama murfin motar yayi saurin bude mata yana cewa
"Easy Babe, wa kuma ya bata miki rai haka"
"Duk ba kai kaja ba, akan me zaka kirani bayan kasan ina cikin mutane su kuma mayu daga jin muryarka har wata ta riqe abinda ka fada" tayi maganar cikin fada kamar meyi da dan cikinta. Sakato Khalil yayi yana binta da ido, ikon Allah yanzu kuma kiran da yayi mata ne ya zama laifi gaskiya yarinyar nan ya yarda saitin kanta na gocewa.
Ganin ta dage tana surfa masa masifa dan har masu wucewa sun fara kallo su yasa ya dakatar da ita, cikin tsawa ya kira sunanta Yace
"Kirawo Nuratu mu wuce"
Yanda ya hada fuska babu wasa sam yasa dole ta juya ba taredata musa ba amma da taso suyi tafiyarsu ne su barta idan yaso ta hau Napep ko ta kira nata Mijin yazo ya daukota tunda tafison me lalle akanta.
Kafin ta qarasa shiga gurin Nuratun ta fito da wata ma'aikaciya a bayanta ta ruqo mata Paper Bags masu tambarin salon din guda biyu seta juyo tana ci gaba da kumbure kumbure ta tsaya a kusada Khalil daya harde hannu biyu a qirji kawai yana binta da kallo, ran Nuratu babu dadi ta bude baya ta shiga yarinyar ta miqa mata Jakunkunan ta karba tareda godiya kafin ta juya har tayi gaba ta waiwayo ta kalli Umaimah da Khalil, ita Umaimah daman idonta akan yarinyar yake shi kuma Khalil yana nazarin Umaiman yarinyar na juyawa kuwa tayi missing step ta tafi taga taga zata fadi Allah ya taimaketa dafe bango
"Mayya dama kin fadi kin karya haqori gobe kya sake kallon Mijin wata" Umaimah ta fada, cikin jin haushi yarinyar ta mayar mata tace
"Ni ba mayya bace kuma na kalle shi din tunda ai Namiji ne badan ke kadai akayi ba"
"Kan babbar bala'i, me kika ce?" Umaimah ta zabura tayi kan yarinyar, Tsawa Khalil ya buga mata, ba ita ba hatta da Nuratu dake cikin mota tana kallon ikon Allah seda ta razana,
"Get in side" ya fada yana nuna mata qofar motar, dole ta shige dan a yanda taga bacin rai a idonsa tabbas yana iya kai mata mangari. Seda ya kulle mata qofar kafin ya zagaya bangaren sa ya tada motar, da gudu ya figeta suka fice daga gurin zuciyarsa na tafasa wannan wane irin zubar da qima ne? Yanzu daya barta se tace zata kama yarinyar da kokawa kome? Anya ma Umaimah nada hankali kuwa?
Haka ya ringa tunani a zuciyarsa yana sharara gudu dasu a titi kamar masu tafiya Lagos Nuratu na baya tana zare ido da addu'ar Allah ya sauke su lafiya ita kuma hamshaqiyar ta hada kai da guiwa tana kukan baqin ciki biyu, maganar da yarinyar ta fada mata ga wanda akayi saboda shi ya banzatar da ita ko a kwalar rigarsa be nuna yasan tana kukan ba.
Yana tsaida Mota a qofar gidan su Nuratu ta kwashi komatsan ta tana hamdala tayi waje, Umaimah ta dago zata fara masa qorafi ya dakatar da ita da cewa
"Fita malama"
"Khalil ni kake kora daga motar ka?" Ta fada cikin mamaki tana nuna kanta, se ya kalle ta da idonsa da suka chanza kala saboda bacin rai yace
"Haka nace, Umaimah ba fita daga mota ta ba idan har bazaki dena wannan halin jahilcin ba zan fitar dake daga rayuwata ne gaba daya ba iya mota ba.
Yanzu ke abinda kike yi yayi kama da na me hankali wadda tasan me takeyi? Kishi hauka ne? Ko kuwa a zamanin Jahiliyya muke da zaki doshi wata a cikin mutane zakiyi dambe saboda bakida nutsuwa, waye ze kalli actions dinki yace kin taba zama a ajin koyar da karatu.
Toh wallahi bari kiji, ba jibi za'a daura mana aure ba ko a safiyar ranar ne kika kuskura kika maimaita something stupid as this maganar aurena dake ta tashi, kar kuma kiyi tunanin idan an daura mana aure kinci banza kenan, Umaimah idan baki shiga hankalinki ba you better get ready to deal with the othersidenof me da bazaki taba son na bayyana miki shi ba danba ke kadai ce saitin ki yake gocewa ba, idan kuma kika bari nawa saitin ya goce kece zaki sha wahala fitar mun daga mota".
Tunda ya fara magana ta daskare a gurin, Jahilci, rashin hankali, rashin nutsuwa duk ita kadai Khalil ya jefa da wadannan kalmomin saboda tayi kishi akan sa, saboda ta nunawa duniya muhimmancinsa a gurinta?
Dakyar ta iya bude baki saboda yanda kukan gaske ya taso mata dan ashe dazu na samun guri kawai tayi tana kallonsa tace
"Saboda ina kishinka kake kirana da Jahila Khalil?"
"To hell with the kishi fitar mun a mota Umaimah kafin kisa na aimata abinda ni dake zamu zo muna regretting, get out of my fucking car" ya fada cikin daga murya jikinsa na rawa jijiyoyin kansa sun fito rudu rudu ai bata jira komai ba ta fice a sittin dan ta tabbata ya kai matakin qarshe a fushi, yanda ya figi motarsa ya bar layin ya qara dugunzuma mata hankali idan wani abu ya same shi fa itace sila.
Wayarta ta fara lalubawa a jikinta taji babu se sannan ta tuna ta bar jakar a motar a garin sauri, jiki a sanyaye ta shige gida majalisar munafukan unguwarsu suka rakata da ido tana shiga suka fara tattara analysis na tunanin abinda ya faru dan basuji komai ba.
Can dakunan dake bayan gidan su ta nufa falle daddaya ne wanda sune dakunan gidan daga baya da Abban ya samu hali ya qaro wani fili shine yayi musu wani gini suka koma ciki wannan aka barshi a BQ saboda amfanin taro kamar yanzun, dakin da suka koma ciki ta bude ta shiga, babu kowa a ciki tasan Nuratu nacan tana bada kanun labarai seta maida qofar ta saka sakata ta haye kan katifa kawai ta saki Kuka, seda tayi iya yinta taji sanyi a zuciyarta kafin ta tashi ta shiga wanka ta wanke lallen da Allah ya sota garin ana iska sosai be jaguke ba.
Tunanin halin da Khalil yake ciki takeyi, ina ya tafi? Me yake yi yanzu gashi babu waya bare ta kirashi ta bashi haquri kuna bata so ta shiga cikin gidan yanzu tasan se sun cinyeta a danya. Bubbuga qofa taji anayi da kiran sunanta, seda ta kasa kunne kafin ta gane muryar Rumasa'u ce da Halima se wasu da bata tantance su waye ba.
Bude qofar tayi suka shigo kusan su biyar kaya kaya suka fara mata cari
"Amma Umaimah baki da kirki, yanzu ace sedai muji labarin auranki a gari? Toh gani tunda bani da zuciya na taso gari ya gari tundaga Maiduguri nazo" Fannah da sam Umaimah batayi tsammanin ganinta ba ta fada, qarin mamakin ta qaton cikin da ta gani a jikin Fannah haihuwa ko yaushe amma ta iya yiwo wannan takakkiyar. Halima tace ta sauke goyon yarinyarta Umaiman ta karbe ta tace
"Ki rabu da ita ni ban taba ganin inda laifin wani ya shafi wani ba a rayuwa, saboda kin samu matsala Nabila da Fauziyya shikenan se ki dauki gaba damu, mu menene namu a ciki? Mutanen nan fa ke kika kwaso mana su kika kawo su group dinmu amma da taku ta hado ku se kika mana kudin goro duk kina toshe lambarmu. Ni wallahi naji dadin abinda ya faru sosai ko babu komai mun rabu da alaqaqai dan duk wani abu mara kyau su suke qara saka mu a ciki musamman ke da kike daukar shawararsu kamar me gashi da Allah yaso ki da rahma kun rabu kin samu miji zakiyi aure na tabbatar da ace har yanzu kuna tare wallahi bazasu barki ba, se sun san yanda sukayi suka lalata maganar kamar yanda suka saba tunzuraki kina lalata auranki".
Yanzu dai komai ya wuce ayi haquri, sannan ke kuma Katinan da kika bani sunyi kadan akwai wadanda sukace zasu zo dan haka seki qaro wasu na gaya musu mu hadu a gurin kawai goben" Ruma ta katse musu cece kucen.
Umaimah da duk jiki yayi la'asar, tunaninta yana can kan sanin halin da Khalil yake ciki tayi murmushin yaqe kawai, se kuma ta miqe ta ajiye Baby Ayra tana kallon Ruman tace "Dan aramun wayarki nayi kira"
"Gaskiya bazaki cinye mun kati ba dan ke kina da me saka miki ki kirashi yanzu ya turo na samu nima kimun transfer" Ruman ta fada tana miqa mata wayar.
Fita tayi tacan gefe inda babu hayaniyar mutane ta shiga kiran layin Khalil, seda tayi kira uku ba'a daga ba, harta haqura se dabara ta fado mata. Text ta rubuta masa ta tura
"Rumasa'u ce Aminiyar Umaimah, daman ta bani number kane tace muyi magana akan motocin da zaka turo mana gobe na tafiya gurin Kamu" tana turawa ta dakata, ba'afi minti biyu ba kuqa se gashi ya biyo bayan kiran tana dagawa ta fashe masa kuka ba tareda tayi magana ba.
PROMO
PROMO
PROMO
BEFORE 4K NOW 2500
3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
KITURA SHEDAR BIYA 👇🏻
08162859027
AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA
INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK DATTIN MARA CIWON MARA CIWON JIKI HANA HAIHUWA RASHIN NI IMA RASHIN JIN SHA AWA FITAR FARIN RUWA KAIKAYI KURAJEN PP DA NA JIKI JIN ZAFI YAYIN SADUWA FITAR FARIN RUWA MAI WARI BASUR KOMAI DADEWARSHI CIWON NONO
A waje kuwa a fusace Umaimah ta qarasa inda ta Hango motar Khalil, bawan Allah daya sha gayunsa ya fito da murmushi amma ganin fuskarta a dinke kamar Hadirin August yasa ya tsaya daga inda yake harta qaraso
"Mu tafi" ta fada tana qoqarin kama murfin motar yayi saurin bude mata yana cewa
"Easy Babe, wa kuma ya bata miki rai haka"
"Duk ba kai kaja ba, akan me zaka kirani bayan kasan ina cikin mutane su kuma mayu daga jin muryarka har wata ta riqe abinda ka fada" tayi maganar cikin fada kamar meyi da dan cikinta. Sakato Khalil yayi yana binta da ido, ikon Allah yanzu kuma kiran da yayi mata ne ya zama laifi gaskiya yarinyar nan ya yarda saitin kanta na gocewa.
Ganin ta dage tana surfa masa masifa dan har masu wucewa sun fara kallo su yasa ya dakatar da ita, cikin tsawa ya kira sunanta Yace
"Kirawo Nuratu mu wuce"
Yanda ya hada fuska babu wasa sam yasa dole ta juya ba taredata musa ba amma da taso suyi tafiyarsu ne su barta idan yaso ta hau Napep ko ta kira nata Mijin yazo ya daukota tunda tafison me lalle akanta.
Kafin ta qarasa shiga gurin Nuratun ta fito da wata ma'aikaciya a bayanta ta ruqo mata Paper Bags masu tambarin salon din guda biyu seta juyo tana ci gaba da kumbure kumbure ta tsaya a kusada Khalil daya harde hannu biyu a qirji kawai yana binta da kallo, ran Nuratu babu dadi ta bude baya ta shiga yarinyar ta miqa mata Jakunkunan ta karba tareda godiya kafin ta juya har tayi gaba ta waiwayo ta kalli Umaimah da Khalil, ita Umaimah daman idonta akan yarinyar yake shi kuma Khalil yana nazarin Umaiman yarinyar na juyawa kuwa tayi missing step ta tafi taga taga zata fadi Allah ya taimaketa dafe bango
"Mayya dama kin fadi kin karya haqori gobe kya sake kallon Mijin wata" Umaimah ta fada, cikin jin haushi yarinyar ta mayar mata tace
"Ni ba mayya bace kuma na kalle shi din tunda ai Namiji ne badan ke kadai akayi ba"
"Kan babbar bala'i, me kika ce?" Umaimah ta zabura tayi kan yarinyar, Tsawa Khalil ya buga mata, ba ita ba hatta da Nuratu dake cikin mota tana kallon ikon Allah seda ta razana,
"Get in side" ya fada yana nuna mata qofar motar, dole ta shige dan a yanda taga bacin rai a idonsa tabbas yana iya kai mata mangari. Seda ya kulle mata qofar kafin ya zagaya bangaren sa ya tada motar, da gudu ya figeta suka fice daga gurin zuciyarsa na tafasa wannan wane irin zubar da qima ne? Yanzu daya barta se tace zata kama yarinyar da kokawa kome? Anya ma Umaimah nada hankali kuwa?
Haka ya ringa tunani a zuciyarsa yana sharara gudu dasu a titi kamar masu tafiya Lagos Nuratu na baya tana zare ido da addu'ar Allah ya sauke su lafiya ita kuma hamshaqiyar ta hada kai da guiwa tana kukan baqin ciki biyu, maganar da yarinyar ta fada mata ga wanda akayi saboda shi ya banzatar da ita ko a kwalar rigarsa be nuna yasan tana kukan ba.
Yana tsaida Mota a qofar gidan su Nuratu ta kwashi komatsan ta tana hamdala tayi waje, Umaimah ta dago zata fara masa qorafi ya dakatar da ita da cewa
"Fita malama"
"Khalil ni kake kora daga motar ka?" Ta fada cikin mamaki tana nuna kanta, se ya kalle ta da idonsa da suka chanza kala saboda bacin rai yace
"Haka nace, Umaimah ba fita daga mota ta ba idan har bazaki dena wannan halin jahilcin ba zan fitar dake daga rayuwata ne gaba daya ba iya mota ba.
Yanzu ke abinda kike yi yayi kama da na me hankali wadda tasan me takeyi? Kishi hauka ne? Ko kuwa a zamanin Jahiliyya muke da zaki doshi wata a cikin mutane zakiyi dambe saboda bakida nutsuwa, waye ze kalli actions dinki yace kin taba zama a ajin koyar da karatu.
Toh wallahi bari kiji, ba jibi za'a daura mana aure ba ko a safiyar ranar ne kika kuskura kika maimaita something stupid as this maganar aurena dake ta tashi, kar kuma kiyi tunanin idan an daura mana aure kinci banza kenan, Umaimah idan baki shiga hankalinki ba you better get ready to deal with the othersidenof me da bazaki taba son na bayyana miki shi ba danba ke kadai ce saitin ki yake gocewa ba, idan kuma kika bari nawa saitin ya goce kece zaki sha wahala fitar mun daga mota".
Tunda ya fara magana ta daskare a gurin, Jahilci, rashin hankali, rashin nutsuwa duk ita kadai Khalil ya jefa da wadannan kalmomin saboda tayi kishi akan sa, saboda ta nunawa duniya muhimmancinsa a gurinta?
Dakyar ta iya bude baki saboda yanda kukan gaske ya taso mata dan ashe dazu na samun guri kawai tayi tana kallonsa tace
"Saboda ina kishinka kake kirana da Jahila Khalil?"
"To hell with the kishi fitar mun a mota Umaimah kafin kisa na aimata abinda ni dake zamu zo muna regretting, get out of my fucking car" ya fada cikin daga murya jikinsa na rawa jijiyoyin kansa sun fito rudu rudu ai bata jira komai ba ta fice a sittin dan ta tabbata ya kai matakin qarshe a fushi, yanda ya figi motarsa ya bar layin ya qara dugunzuma mata hankali idan wani abu ya same shi fa itace sila.
Wayarta ta fara lalubawa a jikinta taji babu se sannan ta tuna ta bar jakar a motar a garin sauri, jiki a sanyaye ta shige gida majalisar munafukan unguwarsu suka rakata da ido tana shiga suka fara tattara analysis na tunanin abinda ya faru dan basuji komai ba.
Can dakunan dake bayan gidan su ta nufa falle daddaya ne wanda sune dakunan gidan daga baya da Abban ya samu hali ya qaro wani fili shine yayi musu wani gini suka koma ciki wannan aka barshi a BQ saboda amfanin taro kamar yanzun, dakin da suka koma ciki ta bude ta shiga, babu kowa a ciki tasan Nuratu nacan tana bada kanun labarai seta maida qofar ta saka sakata ta haye kan katifa kawai ta saki Kuka, seda tayi iya yinta taji sanyi a zuciyarta kafin ta tashi ta shiga wanka ta wanke lallen da Allah ya sota garin ana iska sosai be jaguke ba.
Tunanin halin da Khalil yake ciki takeyi, ina ya tafi? Me yake yi yanzu gashi babu waya bare ta kirashi ta bashi haquri kuna bata so ta shiga cikin gidan yanzu tasan se sun cinyeta a danya. Bubbuga qofa taji anayi da kiran sunanta, seda ta kasa kunne kafin ta gane muryar Rumasa'u ce da Halima se wasu da bata tantance su waye ba.
Bude qofar tayi suka shigo kusan su biyar kaya kaya suka fara mata cari
"Amma Umaimah baki da kirki, yanzu ace sedai muji labarin auranki a gari? Toh gani tunda bani da zuciya na taso gari ya gari tundaga Maiduguri nazo" Fannah da sam Umaimah batayi tsammanin ganinta ba ta fada, qarin mamakin ta qaton cikin da ta gani a jikin Fannah haihuwa ko yaushe amma ta iya yiwo wannan takakkiyar. Halima tace ta sauke goyon yarinyarta Umaiman ta karbe ta tace
"Ki rabu da ita ni ban taba ganin inda laifin wani ya shafi wani ba a rayuwa, saboda kin samu matsala Nabila da Fauziyya shikenan se ki dauki gaba damu, mu menene namu a ciki? Mutanen nan fa ke kika kwaso mana su kika kawo su group dinmu amma da taku ta hado ku se kika mana kudin goro duk kina toshe lambarmu. Ni wallahi naji dadin abinda ya faru sosai ko babu komai mun rabu da alaqaqai dan duk wani abu mara kyau su suke qara saka mu a ciki musamman ke da kike daukar shawararsu kamar me gashi da Allah yaso ki da rahma kun rabu kin samu miji zakiyi aure na tabbatar da ace har yanzu kuna tare wallahi bazasu barki ba, se sun san yanda sukayi suka lalata maganar kamar yanda suka saba tunzuraki kina lalata auranki".
Yanzu dai komai ya wuce ayi haquri, sannan ke kuma Katinan da kika bani sunyi kadan akwai wadanda sukace zasu zo dan haka seki qaro wasu na gaya musu mu hadu a gurin kawai goben" Ruma ta katse musu cece kucen.
Umaimah da duk jiki yayi la'asar, tunaninta yana can kan sanin halin da Khalil yake ciki tayi murmushin yaqe kawai, se kuma ta miqe ta ajiye Baby Ayra tana kallon Ruman tace "Dan aramun wayarki nayi kira"
"Gaskiya bazaki cinye mun kati ba dan ke kina da me saka miki ki kirashi yanzu ya turo na samu nima kimun transfer" Ruman ta fada tana miqa mata wayar.
Fita tayi tacan gefe inda babu hayaniyar mutane ta shiga kiran layin Khalil, seda tayi kira uku ba'a daga ba, harta haqura se dabara ta fado mata. Text ta rubuta masa ta tura
"Rumasa'u ce Aminiyar Umaimah, daman ta bani number kane tace muyi magana akan motocin da zaka turo mana gobe na tafiya gurin Kamu" tana turawa ta dakata, ba'afi minti biyu ba kuqa se gashi ya biyo bayan kiran tana dagawa ta fashe masa kuka ba tareda tayi magana ba.
PROMO
PROMO
PROMO
BEFORE 4K NOW 2500
3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
KITURA SHEDAR BIYA 👇🏻
08162859027
AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA
INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK DATTIN MARA CIWON MARA CIWON JIKI HANA HAIHUWA RASHIN NI IMA RASHIN JIN SHA AWA FITAR FARIN RUWA KAIKAYI KURAJEN PP DA NA JIKI JIN ZAFI YAYIN SADUWA FITAR FARIN RUWA MAI WARI BASUR KOMAI DADEWARSHI CIWON NONO