Sashe 161
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Humaira da shaf ta shagala ta manta da wani zancen Yarjejeniya a tsakaninsu, tana zaune a kusada Mama suke wayar seta tashi dan bata so taji abinda zata fada masa. Daman tunda ta fahimci yawan maganar da sukeyi da Ibrahim din take mata tsiya. Noor kansa yanzu ba wani bashi lokaci take kamar da ba da yawanci ita take nacin kiransa ko tace yazo yanzu da ta samu wani yasa idan ya kirata mara ba idan be kira ba shikenan ita da kanta ta gane banbancin soyayyar yarintar da ake ta fahimtar dacita data babban mutum.
Ita da Noor ko yaya tayi masa abu ya ringa fada da Masifa kenan se tayi ta bashi haquri amma Ibrahim ko lallabata yake kamar kwai baya son bacin ranta ko kadan. Ko waya suke yaji muryarta wani iri ya ringa tambayar meya sameta ko me take so kenan ita kuma daman tana son ayita lelenta seta shagwabe tayi ta masa sangarta yana biye mata abinda bata samu a gurin Noor.
Seda ta kwanta akan Gadonta kafin ta bashi amsa da cewa
"Toh ai da sauran lokaci har zuwa gobe, sannan nima bazan fadi maka sakamakon ba se na ganka ido da ido wannan ne qarashen cin jarabawar dan bazanyi cinikin biri a sama ba. Kai ka sanni kasan komai a kaina amma ni sunanka kawai na sani ko Yaya Khalil dana tambaya hotonka cewa yayi kace karya nuna mun. Toh gobe kazo na ganka sannan se na yanke hukunci".
Murmushi yayi a ransa yana cewa " Ashe tana da wayo" a fili kuwa yace mata
"Shikenan, amma ina so kiyi mun wani alqawari, koda ace kin ganni in har a zuciyarki da farko kin yarda da soyayyata karki canza"
"Ban gane ba?"
"Ina nufin idan kika ganni karkice saboda matsayina a gurinki zaki qini, in har dagaske kin kamu da sona karki bari wani abu ya canza miki ra'ayi..." Maganar ce ta maqale saboda ganin Umaimah da yayi tsaye akansa. Yayi nisa cikin shauqin soyayya da sam beji zuwanta ba. Kashe wayar yayi ya miqe zaune yana kallonta. Duk wata dakiya da Mazantaka dayasan yana dasu seda ya tattaro ya yafa dukda yanda zuciyarsa take bugawa da irin kallon da take jifansa dashi amma haka ya dake, dakyar ya iya bude baki yace mata
"Wani abun kike buqata, me yasa baki kirani a waya nazo dakaina ba kika hawo bene bayan likita ya hanaki?"
"Kira nawa zanyi maka Munafuki? Gara da baka daga ba ai saboda Allah naso na yana so nazo na tarar da cin Amanar da kakeyi mun yasa shiyasa baka dauki wayar ba. To wallahi ka dauka yanda kake iqirarin ta fada soyayyarka ka dauka cewa ta fada a ramin masifa da bala'i ne dan koma wacece kake magana da ita senaga bayanta wallahi" Umaimah ta fada tana huce kamar wadda ta hadiyi Maciji.
Wani kallo ya watsa mata kafin ya miqe tsaye yana kallonta shima yace.....
"Kin san yanda kika huda zuciyata ba tareda sallama ba kika shiga? Toh haka tayi mun. Ki saka a ranki keda ita matsayinku daya a zuciyata kuma ki saka ran shigowarta cikin gidan nan bada dadewa ba" yana gama fadar haka ya wuce ya bar Umaimah da mamaki ya sa ta kasa rufe bakinta. Seda ya shige daki kafin ta dawo hayyacinta babu bata lokaci tabi bayansa tana cewa
"Wallahi baka isa ba Khalil qarya kakeyi babu wata mace da zaka iya so bayan ni ballantana har ka kawota cikin gidanka, duk kuwa wadda tayi kuskuren shiga rayuwarka ta fara qirga kwanakin da suka rage mata a duniya"
'Bam' ya bugo qofar dakinsa ya rufe daidai ta tura kai zata shiga har seda ya bugeta. Ihu ta fasa ta shiga buga qofar da qarfin gaske tana zage zage amma ko Gezau Khalil dake cire kayan jikinsa beyi ba. Wanka ya shige dan fita ma yake so yayi daga gidan, gara yaje gurin Humairanshi ya ganta ko zeji sanyi a ransa Umaimah ko idan taga dama ta qona gidan saboda Masifa amma a wannan karon babu gudu babu ja da baya yaga matar aure.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 60
"Wallahi baka isa ka fita daga gidan nan ba yau" Umaimah da tayi caraf ta riqe rigar Khalil ta fada. Kallonta yayi yanda ta birkice gaba daya kamar wadda ta shiga hauka shida yaji shiru ta dena bugun qofar ma ya zata sauka tayi ashe tana tsaye. Qoqarin zame rigarsa ya shigayi a hankali dan baya son abinda ze saka ya jajjigata saboda jikinta amma ina ita bata duba hakan ba sake cukuikuye shi takeyi tana zabga Masifa wanda shi bama gane abinda take fada yake ba. Ganin tana neman bata masa lokaci yasa ya daka mata tsaawar da ta saka ta sakinsa babu shiri taja baya, da hannu ya nunata yace
"Ki kiyaye ni Umaimah" se ya ja tsaki ya barta a tsaye, wayarsa da muqullin mota ya dauka ya fice, kafin ta sakko qasan se jin tashin motarsa tayi alamar ya bar gidan gaba daya ma. Bata damu da yana yin da take ciki ba ta fice zuwa bangaren Hajiya tana rusa kuka kamar wadda aka aikowa da saqon mutuwar Mama. Hajiya dake kishingide kan kujera bata jima da dawowa daga Asibiti ba jikine ya motsa mata daren jiya kwana tayi da ciwon kai seda taje aka ce hawan jininta ne ya tashi gama shan maganinta kenan tana hutawa Umaiman ta fado seda qirjin Hajiya ya buga ganin yana yinta ta tabbatar da ba lafiya ba.
A qasa ta zube tana kuka kamar ranta ze fita, Hajiya ta rude tambayarta take meya faru amma ta kasa bude baki tayi magana sema qara qaimi take gurin Kukan tana dafe kai da ciki ita dai Hajiya ganin ba zatayi magana ba ya sa ta wawuro wayarta ta shiga kiran Khalil.
Yana tafe tuqi yake cike da nishadi saboda zejr yaga rabin ransa. Kiran Hajiya ya shigo wayarsa ko ba'a fada ba yasan Umaimah ce dan haka ya amsa wayar ya saka a Speaker yaci gaba da tuqinsa. Muryar Hajiya yaji tana cewa
"Khalil lafiya? Me ya faru? Meya samu Umaimah take irin wannan kukan ko mutuwa aka mata?"
A tausashe ya kira sunan Hajiyar jin yanda take magana yasan hankalinta a tashe yake dan haka yace
"Hajiya, kinga dazun nan muka dawo daga Asibiti kuma sunce ki samu hutu karki bari wani abu ya dameki. Dan Allah ki tafi sama ki kwanta ki qyale Umaimah, babu abinda akayi mata, damuwarta ce ta motsa take so se ta dagawa kowa hankali ki rabu da ita kawai gani nan dawowa gidan nima na fita abu zanyi yanzu zan dawo ba dadewa zanyi ba. Dan Allah Hajiya karki biye mata ki shiga daki ki kwanta saboda jikinki".
"Amma Babana meya faru har haka kaga kaga irin kukan da takeyi kuwa...?" Hajiya ta sake fada se yayi saurin katseta ga kuka me hade da ihun da Umaiman takeyi ya dame shi yace
"Na sani Hajiya nidai ina roqonki karki damu kanki ki barta yanzu zan dawo koma menene zanji dashi"
"Shikenan, seka dawo din amma kayi sauri" ta fada kafin ya kashe wayar. Tagumi ta rafka tana kallon Umaiman dake rusa kuka duk ta hada zufa saboda masifa, Ajiyar zuciya tayi ta miqe sakyar tana kallonta tace
"Kiyi haquri kiyi shiru Khalil din yana hanya bari na shiga ciki idan yazo se naji abinda ya hadaku" tana gama fada ta wuce sama dakyar take takawa saboda kanta dam sara mata ga jiri haka ta ringa kama qarfen Benen harta haye.
Umaimah data tsayar da kukanta kamar anyi ruwan sama an dauke tabi Hajiyar da kallo baki sake saboda tsabar mamamkin abinda tayi mata.
"Bantan uban nan" ta fada a fili kafin ta yunqura ta miqe. Fita tayi ta koma part dinsu, a falon ta ringa safa da marwa tana lissafin abinda zatayi, wato hade mata kao zasuyi shida uwarsa, ke nan ma tasan da zancen auren da yake iqirarin zeyi? to wallahi ko sama da qasa zasu hade ba'a isa ayi mata abinda ake shirin yi ba, daga shi har Hajiyan daidai take dasu. Zabura tayi ta shige daki, Ruqayya dake goge goge tana satar kallonta a fili tace
"Allah ya kyauta' dan tunda aka fara rigimar tana jinsu har sanda Khalil din ya fita Umaiman ta bishi, da ace uwar dakin nata me fahimtace da tayi mata magana akan abubuwa da yawa da takeyi da basu dace ba. Ta girmi Umaimah nesa ba kusa ba da ta fita ilimin zaman duniya shiyasa take ganin baiken Umaimah akan irin abubuwan da takeyi.
Khalil
Yana fita daga gidan ya kira Humairah a zuwan Ibrahim akan gashi nan a hanya. Ce mata yayi tafiya ta kamashi yau da daddare dan haka baze iya jira har gobe ba kafin yaji amsarta ta tanadeshi kawai yana tafe. Suna gama wayar sega kiranta a dayan Layinsa, seda yayi dariya son ransa har kiran ya katse kafin ya bita. Haka take, duk sanda Ibrahim ya rikita qaramar kwakwalwarta seta kirashi neman mafaka yanzun ma tana dagawa tace
"Yah Khalil abokinka ne, wai kaji yanzu ze zo bayan kuma se gobe ne kwana bakwai din zata cika"
"Eh munyi magana dashi wani aikine ya taso masa ze tafi Lagos yau shiyasa yace ze zo dan idan ya tafi ze dade be dawo na shiyasa. Nima naso muzo tare amma ban samu dama ba ina wani abu duk yanda kukayi dashi zanji dukda ma dai nasan mun rigada mun cinye jarabawar ai" ya bata amsa se tayi shiru kafin a sanyaye tace
"Toh Allah ya kawo shi lafiya, amma dai ni da ya bari ma kawai seya dawo din"
Ita da Noor ko yaya tayi masa abu ya ringa fada da Masifa kenan se tayi ta bashi haquri amma Ibrahim ko lallabata yake kamar kwai baya son bacin ranta ko kadan. Ko waya suke yaji muryarta wani iri ya ringa tambayar meya sameta ko me take so kenan ita kuma daman tana son ayita lelenta seta shagwabe tayi ta masa sangarta yana biye mata abinda bata samu a gurin Noor.
Seda ta kwanta akan Gadonta kafin ta bashi amsa da cewa
"Toh ai da sauran lokaci har zuwa gobe, sannan nima bazan fadi maka sakamakon ba se na ganka ido da ido wannan ne qarashen cin jarabawar dan bazanyi cinikin biri a sama ba. Kai ka sanni kasan komai a kaina amma ni sunanka kawai na sani ko Yaya Khalil dana tambaya hotonka cewa yayi kace karya nuna mun. Toh gobe kazo na ganka sannan se na yanke hukunci".
Murmushi yayi a ransa yana cewa " Ashe tana da wayo" a fili kuwa yace mata
"Shikenan, amma ina so kiyi mun wani alqawari, koda ace kin ganni in har a zuciyarki da farko kin yarda da soyayyata karki canza"
"Ban gane ba?"
"Ina nufin idan kika ganni karkice saboda matsayina a gurinki zaki qini, in har dagaske kin kamu da sona karki bari wani abu ya canza miki ra'ayi..." Maganar ce ta maqale saboda ganin Umaimah da yayi tsaye akansa. Yayi nisa cikin shauqin soyayya da sam beji zuwanta ba. Kashe wayar yayi ya miqe zaune yana kallonta. Duk wata dakiya da Mazantaka dayasan yana dasu seda ya tattaro ya yafa dukda yanda zuciyarsa take bugawa da irin kallon da take jifansa dashi amma haka ya dake, dakyar ya iya bude baki yace mata
"Wani abun kike buqata, me yasa baki kirani a waya nazo dakaina ba kika hawo bene bayan likita ya hanaki?"
"Kira nawa zanyi maka Munafuki? Gara da baka daga ba ai saboda Allah naso na yana so nazo na tarar da cin Amanar da kakeyi mun yasa shiyasa baka dauki wayar ba. To wallahi ka dauka yanda kake iqirarin ta fada soyayyarka ka dauka cewa ta fada a ramin masifa da bala'i ne dan koma wacece kake magana da ita senaga bayanta wallahi" Umaimah ta fada tana huce kamar wadda ta hadiyi Maciji.
Wani kallo ya watsa mata kafin ya miqe tsaye yana kallonta shima yace.....
"Kin san yanda kika huda zuciyata ba tareda sallama ba kika shiga? Toh haka tayi mun. Ki saka a ranki keda ita matsayinku daya a zuciyata kuma ki saka ran shigowarta cikin gidan nan bada dadewa ba" yana gama fadar haka ya wuce ya bar Umaimah da mamaki ya sa ta kasa rufe bakinta. Seda ya shige daki kafin ta dawo hayyacinta babu bata lokaci tabi bayansa tana cewa
"Wallahi baka isa ba Khalil qarya kakeyi babu wata mace da zaka iya so bayan ni ballantana har ka kawota cikin gidanka, duk kuwa wadda tayi kuskuren shiga rayuwarka ta fara qirga kwanakin da suka rage mata a duniya"
'Bam' ya bugo qofar dakinsa ya rufe daidai ta tura kai zata shiga har seda ya bugeta. Ihu ta fasa ta shiga buga qofar da qarfin gaske tana zage zage amma ko Gezau Khalil dake cire kayan jikinsa beyi ba. Wanka ya shige dan fita ma yake so yayi daga gidan, gara yaje gurin Humairanshi ya ganta ko zeji sanyi a ransa Umaimah ko idan taga dama ta qona gidan saboda Masifa amma a wannan karon babu gudu babu ja da baya yaga matar aure.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 60
"Wallahi baka isa ka fita daga gidan nan ba yau" Umaimah da tayi caraf ta riqe rigar Khalil ta fada. Kallonta yayi yanda ta birkice gaba daya kamar wadda ta shiga hauka shida yaji shiru ta dena bugun qofar ma ya zata sauka tayi ashe tana tsaye. Qoqarin zame rigarsa ya shigayi a hankali dan baya son abinda ze saka ya jajjigata saboda jikinta amma ina ita bata duba hakan ba sake cukuikuye shi takeyi tana zabga Masifa wanda shi bama gane abinda take fada yake ba. Ganin tana neman bata masa lokaci yasa ya daka mata tsaawar da ta saka ta sakinsa babu shiri taja baya, da hannu ya nunata yace
"Ki kiyaye ni Umaimah" se ya ja tsaki ya barta a tsaye, wayarsa da muqullin mota ya dauka ya fice, kafin ta sakko qasan se jin tashin motarsa tayi alamar ya bar gidan gaba daya ma. Bata damu da yana yin da take ciki ba ta fice zuwa bangaren Hajiya tana rusa kuka kamar wadda aka aikowa da saqon mutuwar Mama. Hajiya dake kishingide kan kujera bata jima da dawowa daga Asibiti ba jikine ya motsa mata daren jiya kwana tayi da ciwon kai seda taje aka ce hawan jininta ne ya tashi gama shan maganinta kenan tana hutawa Umaiman ta fado seda qirjin Hajiya ya buga ganin yana yinta ta tabbatar da ba lafiya ba.
A qasa ta zube tana kuka kamar ranta ze fita, Hajiya ta rude tambayarta take meya faru amma ta kasa bude baki tayi magana sema qara qaimi take gurin Kukan tana dafe kai da ciki ita dai Hajiya ganin ba zatayi magana ba ya sa ta wawuro wayarta ta shiga kiran Khalil.
Yana tafe tuqi yake cike da nishadi saboda zejr yaga rabin ransa. Kiran Hajiya ya shigo wayarsa ko ba'a fada ba yasan Umaimah ce dan haka ya amsa wayar ya saka a Speaker yaci gaba da tuqinsa. Muryar Hajiya yaji tana cewa
"Khalil lafiya? Me ya faru? Meya samu Umaimah take irin wannan kukan ko mutuwa aka mata?"
A tausashe ya kira sunan Hajiyar jin yanda take magana yasan hankalinta a tashe yake dan haka yace
"Hajiya, kinga dazun nan muka dawo daga Asibiti kuma sunce ki samu hutu karki bari wani abu ya dameki. Dan Allah ki tafi sama ki kwanta ki qyale Umaimah, babu abinda akayi mata, damuwarta ce ta motsa take so se ta dagawa kowa hankali ki rabu da ita kawai gani nan dawowa gidan nima na fita abu zanyi yanzu zan dawo ba dadewa zanyi ba. Dan Allah Hajiya karki biye mata ki shiga daki ki kwanta saboda jikinki".
"Amma Babana meya faru har haka kaga kaga irin kukan da takeyi kuwa...?" Hajiya ta sake fada se yayi saurin katseta ga kuka me hade da ihun da Umaiman takeyi ya dame shi yace
"Na sani Hajiya nidai ina roqonki karki damu kanki ki barta yanzu zan dawo koma menene zanji dashi"
"Shikenan, seka dawo din amma kayi sauri" ta fada kafin ya kashe wayar. Tagumi ta rafka tana kallon Umaiman dake rusa kuka duk ta hada zufa saboda masifa, Ajiyar zuciya tayi ta miqe sakyar tana kallonta tace
"Kiyi haquri kiyi shiru Khalil din yana hanya bari na shiga ciki idan yazo se naji abinda ya hadaku" tana gama fada ta wuce sama dakyar take takawa saboda kanta dam sara mata ga jiri haka ta ringa kama qarfen Benen harta haye.
Umaimah data tsayar da kukanta kamar anyi ruwan sama an dauke tabi Hajiyar da kallo baki sake saboda tsabar mamamkin abinda tayi mata.
"Bantan uban nan" ta fada a fili kafin ta yunqura ta miqe. Fita tayi ta koma part dinsu, a falon ta ringa safa da marwa tana lissafin abinda zatayi, wato hade mata kao zasuyi shida uwarsa, ke nan ma tasan da zancen auren da yake iqirarin zeyi? to wallahi ko sama da qasa zasu hade ba'a isa ayi mata abinda ake shirin yi ba, daga shi har Hajiyan daidai take dasu. Zabura tayi ta shige daki, Ruqayya dake goge goge tana satar kallonta a fili tace
"Allah ya kyauta' dan tunda aka fara rigimar tana jinsu har sanda Khalil din ya fita Umaiman ta bishi, da ace uwar dakin nata me fahimtace da tayi mata magana akan abubuwa da yawa da takeyi da basu dace ba. Ta girmi Umaimah nesa ba kusa ba da ta fita ilimin zaman duniya shiyasa take ganin baiken Umaimah akan irin abubuwan da takeyi.
Khalil
Yana fita daga gidan ya kira Humairah a zuwan Ibrahim akan gashi nan a hanya. Ce mata yayi tafiya ta kamashi yau da daddare dan haka baze iya jira har gobe ba kafin yaji amsarta ta tanadeshi kawai yana tafe. Suna gama wayar sega kiranta a dayan Layinsa, seda yayi dariya son ransa har kiran ya katse kafin ya bita. Haka take, duk sanda Ibrahim ya rikita qaramar kwakwalwarta seta kirashi neman mafaka yanzun ma tana dagawa tace
"Yah Khalil abokinka ne, wai kaji yanzu ze zo bayan kuma se gobe ne kwana bakwai din zata cika"
"Eh munyi magana dashi wani aikine ya taso masa ze tafi Lagos yau shiyasa yace ze zo dan idan ya tafi ze dade be dawo na shiyasa. Nima naso muzo tare amma ban samu dama ba ina wani abu duk yanda kukayi dashi zanji dukda ma dai nasan mun rigada mun cinye jarabawar ai" ya bata amsa se tayi shiru kafin a sanyaye tace
"Toh Allah ya kawo shi lafiya, amma dai ni da ya bari ma kawai seya dawo din"