Sashe 250
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Nima ban sani ba na Fitsari dai ta bani dana jini kamar protein dai naji tace" Humairan ta bashi amsa seya fita yana ce mata
"Bari na kira Dr Al'amin in yaso da yamma se muje idan ya zauna. Asibitin ma canza shi zamuyi bazan iya jurewa kuna haduwa dashi na zuciyata zata iya tarwatsewa" ya fice daga dakin.
Seda ya kira Dr Al'amin din, be gaya masa abinda ya faru ba dan dukda baya qaunar Noor baze so ya zama sanadin rasa aikinsa ba dan Dr Al'amin ya masa bayanin nauyin da yake kansa, da ace babu yar tsama a tsakaninsu ma tsab shi me iya taimaka masa ne. Dr ne ya masa bayanin Dr Huriya wadda Humairan ta gani jiya ta sanar masa da sunzo amma sun tafi basu kai mata Test result ba, yana taso ya kirashi ya shafa'a yace masa
"Da daddare kuzo Khalil ayi gwajin ina ga ma in zaka yarda ayi mata CS kawai a cire babyn yafi sauqi"
"CS kuma Dr, da akwai wata matsala ne?" Khalil ya tambaya hankalinsa na tashi daya tuna cikin Imaan da shima yace sedai ayiwa Umaimah CS" cikin son kwantar masa sa hankali Dr Al'amin yace
"Aa fa babu wani Abu Khalil kawai dai babyn ne nake ganin yanada girma, zata iya haifarsa amma zata dan ji jiki kaga idan akayi mata aikin za'a sauqaqa amma shawara ce idan ka yarda itama ta yarda shikenan". Hankalin sa ya dan kwanta sukayi sallama, da daddaren kuwa ya kaita ya kasa ya tsare a Lab din har akayi test din Noor bama ya nan shi ya tashi tuntuni. Dr ya dan rubuta mata magunguna da zasu rage mata ciwon kan da tace tana yana damunta basu bar Asibitin ba seda aka basu appointment na CS din da tace ta yarda ayi mata dan tunda yace mata Babyn yayi girma zata dan sha wahala ta tsorata, Aryaan ma data haifa 2.8kg taji jiki balle wannan da yake cewa ze iya kaiwa 4kg ina zata iya gara a cire kawai Allah ya raba su lafiya. Sati daya ya basu satin na zagayowa kuwa sukaje ko Hajiya be sanarwa da za'ayi aikin ba se bayan da aka ciro mata Qaton Babynta fari tas dashi shima aka kaita dakin Hutu kafin ya kira Hajiya ya gaya mata. Ta ringa fada kamar zata aro baki Mama dai da taji tace ai auna arziqi tunda anyi aikin lafiya an gama. Haka tayi kwana uku cikin kyakykyawar kulawa kafin aka sallameta ta wuce gidan Mama kamar yanda Hajiya tace. Sau daya suka hadu da Noor yaje karbar Sample a ward din da take kansa a qasa ya kasa ko kallon qofar dakin nasu da yake a bude sosai Mama taje tayi musu Tijara a gida Ummansa har kuka tayi tana roqon ya fita a sabgar Humaira ya barsu su zauna lafiya ya ringa rantse mata akan shi wlh babu wani abu tsakaninsu tun tuni ya cire komai, ko a baya hankali be gama masa jiki bane shiyasa yake wasu tunanuka amma yanzu babu komai game da ita a ransa illah mutunchi tunda dai shiya hadasu ba rashin mutunchi ba.
Yanda yake sunkuyar dakai Maman da kanta ta kirashi ya shiga dakin, ta bashi dan da biyu tana cewa
"Ga danku kaga na farin can" ta nuna masa Aryaan dake cinyar Jamila yana shan Yoghurt tace
"Kana ganinsu kasan namijin gaske ya haifesu" shidai yayi yaqe ya musu Addu'ar Allah ya raya ya kama gabansa, to shi ko qaddara ta fito da Humaira ai yasan ba sa'ar auransa bace dan bashida abinda ze riqeta dashi ta saba da rayuwar jin dadi me zatayi dashi da har yanzu neman madafa yakeyi babu abinda ya ajiye.
Ranar Suna yaro yaci sunan Mukhtar sunan Mahaifin Mansur Amininsa kuma Mijin Mama mariqiyar Humaira kenan. Har kuka Maman tayi da wannan kara daya musu, kullum burin Mansur kenan a haifar masa Namiji ya saka sunan Mahaifinsa yayansa biyar yanzu duk mata Khalil be gaya musu sunan yaron ba har se ranar sunan da Safe dan data dameshi da tambaya cewa yayi kawai ta samar masa Laqabi se ranar suna zataji, aiko Yayan Mama sunji dadin wannan kara a gidan Hajiya kuwa ana fadar sunan Jalilah tayi tsallen Arbarka tace qarya yake, sunan Abban Umaimah ya saka. Hajiya ta riqe baki tana cewa
"Jalilah jidalinki yawa ne dashi, yanzu sunan ma se kin janyo magana akai"
"To idan qarya nakeyi Hajiya ya fada mana, babu wani sunan Baba me Mota daya saka (haka suke kiransa da suna yara) sunan tsohon sirikinsa ya saka ze wani fake da haka"
"Toh Jalilah ko sunan Abba na saka ai babu aibu a ciki dan Abba uba nane kuma ya isa da nayi masa takwara, karki tunzurani idan ta sake haihuwa na sake maimaita Mukhtar" ya fada mata kaitsaye ta tafa hannaye tana cewa
"Eh lallai Allah ya tsamoka Khalil a kwale kwalen Asiri kake yawo babu kuma wani ka sake sakawa daman shi ka saka kuma sena zuga Humairan akan me za'a saka mata sunan uban kishiya, kishiyar ma yar iska mara mutunchi"
"Kiyita rage mata zunubi kina jibgawa kanki" ya fada yana ficewa dan inya zauna se sun haura sauran yan uwan kuwa dariya suke musu kawai dramar tagwayen bata qarewa su basu ganin sun girma sun haura Arba'in inji Jamila amma kullum kamar wasu yan sha takwas, mita ta dira akan me za'a saka sunanda Hajiya ta gaji tace
"Ke dai in baki sararawa kanki ba ciwon damuwa ne ze kasheki kafin lokacinki yayi, ni banga dalilin dorawa kai damuwar wani ba taka ba. Umaimar nan fa baki isa ki kankareta daga cikinmu ba, yaya uku ta haifawa dan uwanki gasu nan duk inda akaje aka dawo fa an hadu babu yanda za'ayi a rabu kuma Alhaji Sabo Dattijo ne kuma in ma shiya saka banga laifinsa ba dan ya masa abinda uba yakewa Dansa haba ki rage wannan zazzafar qiyayyar taki Yayanta suna girmamaki karki bari su fahimci qin da kikewa uwarsu ba zasuji dadi ba kuma kema zasu iya qinki a dalilin haka dan duk yanda uwa take Yayanta suna sonta.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*
Page 85
Sha tara ta arqizi iyalan gidan Alhaji Sabo suka hada na kayan barka bisa karamchin da suka ce an musu na maida sunan mahaifinsu. Mama da Anty suka shirya Khalifa ya kaisu gidan Hajiya, Mama ta ringa kallon gidan abubuwan da suka faru a ranar data saka qafarta na qarshe na dawo mata shekaru kusan biyar kenan kota layin bata sake biyowa ba se yau din nan tunanin yanda zata sake kallon idon Hajiya takeyi a haka akayi musu iso cikin falon Hajiyar daya sake qawatuwa fiye da da.
Hajiya rasa inda zata sakasu tayi saboda murna, tasa aka ringa kawo musu abubuwan motsa baki yanda take haba haba dasu duk yasa kunya ta sake dabaibayesu jikinsu ya qarara sanyaya da lamarin karamchi irin nata. Tabbas Umaimah tayi asarar Sirikar kirki da samun irinta keda matuqar wahala a wannan zamani. Seda ta gama cika musu gaba da abubuwan ciye ciye kafin ta zauna suka shiga gaisawa. Da suka tado zancen baya ma hade fuska tayi ta nuna musu ita a gurinta komai ya wyce, ashe qullatarsu sukayi shiyasa suka yanke zumunchi dasu Mama da Anty suka hau rantse rantsen ba haka bane yanda suka rude yasa tayi dariya tace
"Komai ya wuce wlh kuma kamar yanda nasha fada miki nayiwa Umaimaha uzuri ba halinta bane kuskure aka samu tareda zugar shaidan data mugayen qawaye amma komai ya wuce sedai muyi fatan hakan ya zama Alkhairi a rayuwarsu gaba daya, Allah kuma ya fito mata da wani Mijin idan kuma da rabon daidaitawa se kiga an koma".
Daga Anty har Maman kasa amsa mata maganar qarshen sukayi dan basu da tabbacin har zuci tayita seta sako musu wata hirar tun suna dararewa har suka saki jiki akayi ta labarin duniya. Duk abinda aka ajiye musu Mama dai Lemo kadai tasha se Dubulan Anty kuwa ta zage taci abinda ya mata dan daman ita bata iya fulako ba. Sun jima kafin Hajiya ta shirya tace suje can gidan su Humairan suga Baby tunda bata dawo ba, a compound suka hadu da Khalil daya dawo daga Abuja saukarsa kenan ya shigo gidan suka hadu ya ringa sunkuyar da kai qasa kamar ze kwanta musu saboda ladabi ya gaida su Maman, ta amsa tana murmushi Anty ce tadan jashi da wasan data saba yi masa kafin suka masa barka suka tafi.
A mota Mama ta yiwa Hajiya zancen Bibi daya tsaya mata a rai danma suna makaranta shiyasa zancenya kwanta mata tun suna zaune se a motar ta tuna.
"Wlh Hajiya muna iyakar qoqarinmu, tabarar takwarata ai da ba'a kwabarta da abin seyafi haka dukda laifin Ubanne kuma shima ina tsawatar masa akan abinda yakeyi sam be kamata ba dan har yan uwan sun fara nuna rashin jin dadinsu dan idan abu ya hadosu tofa ko itace mara gaskiya ze shigar mata seda naci mutumchinsa akan haka na kuma gaya masa ze raba kan yayansa ne sa kansa. Ga wata yar banzar qawa da take da ita a makaranta da take qara dora mata karatun iyashege duk wani abun rashin kirki da kika ga tayi zakiji a gurinta ta koyo ga magana kamar Goyon tsohuwa, nidai na gayawa Uban ya canza mata makaranta tunda daman Idan sun gama Jarabawar zangon nan yace Sakandire zata shiga to ya kaita wata makarantar dan barin yaranka da irin qawar nan tata hadarine, kana tarbiyya suna warware maka kullum cikin tura mata mugayen aqidun qin matar ubanta da Yan dan uwanta takeyi, karkiso kiga yanda take hantarar yaron nan Auwalu da duka tun uwar tana kawaici har takai ta fara magana to yanzu dai abin yayi sauqi tunda Hasanar uban ta zaneta kwanaki da cewa ma tayi zata dauketa yaqi to nima ban matsa ba dan Azabar Jalilah tayi yawa, nata yayanma suka samu suka ballo bason koma mata suke ba dan ta fiya jaraba amma iya qoqari munayi Hajiya sedai mu qara".
"Bari na kira Dr Al'amin in yaso da yamma se muje idan ya zauna. Asibitin ma canza shi zamuyi bazan iya jurewa kuna haduwa dashi na zuciyata zata iya tarwatsewa" ya fice daga dakin.
Seda ya kira Dr Al'amin din, be gaya masa abinda ya faru ba dan dukda baya qaunar Noor baze so ya zama sanadin rasa aikinsa ba dan Dr Al'amin ya masa bayanin nauyin da yake kansa, da ace babu yar tsama a tsakaninsu ma tsab shi me iya taimaka masa ne. Dr ne ya masa bayanin Dr Huriya wadda Humairan ta gani jiya ta sanar masa da sunzo amma sun tafi basu kai mata Test result ba, yana taso ya kirashi ya shafa'a yace masa
"Da daddare kuzo Khalil ayi gwajin ina ga ma in zaka yarda ayi mata CS kawai a cire babyn yafi sauqi"
"CS kuma Dr, da akwai wata matsala ne?" Khalil ya tambaya hankalinsa na tashi daya tuna cikin Imaan da shima yace sedai ayiwa Umaimah CS" cikin son kwantar masa sa hankali Dr Al'amin yace
"Aa fa babu wani Abu Khalil kawai dai babyn ne nake ganin yanada girma, zata iya haifarsa amma zata dan ji jiki kaga idan akayi mata aikin za'a sauqaqa amma shawara ce idan ka yarda itama ta yarda shikenan". Hankalin sa ya dan kwanta sukayi sallama, da daddaren kuwa ya kaita ya kasa ya tsare a Lab din har akayi test din Noor bama ya nan shi ya tashi tuntuni. Dr ya dan rubuta mata magunguna da zasu rage mata ciwon kan da tace tana yana damunta basu bar Asibitin ba seda aka basu appointment na CS din da tace ta yarda ayi mata dan tunda yace mata Babyn yayi girma zata dan sha wahala ta tsorata, Aryaan ma data haifa 2.8kg taji jiki balle wannan da yake cewa ze iya kaiwa 4kg ina zata iya gara a cire kawai Allah ya raba su lafiya. Sati daya ya basu satin na zagayowa kuwa sukaje ko Hajiya be sanarwa da za'ayi aikin ba se bayan da aka ciro mata Qaton Babynta fari tas dashi shima aka kaita dakin Hutu kafin ya kira Hajiya ya gaya mata. Ta ringa fada kamar zata aro baki Mama dai da taji tace ai auna arziqi tunda anyi aikin lafiya an gama. Haka tayi kwana uku cikin kyakykyawar kulawa kafin aka sallameta ta wuce gidan Mama kamar yanda Hajiya tace. Sau daya suka hadu da Noor yaje karbar Sample a ward din da take kansa a qasa ya kasa ko kallon qofar dakin nasu da yake a bude sosai Mama taje tayi musu Tijara a gida Ummansa har kuka tayi tana roqon ya fita a sabgar Humaira ya barsu su zauna lafiya ya ringa rantse mata akan shi wlh babu wani abu tsakaninsu tun tuni ya cire komai, ko a baya hankali be gama masa jiki bane shiyasa yake wasu tunanuka amma yanzu babu komai game da ita a ransa illah mutunchi tunda dai shiya hadasu ba rashin mutunchi ba.
Yanda yake sunkuyar dakai Maman da kanta ta kirashi ya shiga dakin, ta bashi dan da biyu tana cewa
"Ga danku kaga na farin can" ta nuna masa Aryaan dake cinyar Jamila yana shan Yoghurt tace
"Kana ganinsu kasan namijin gaske ya haifesu" shidai yayi yaqe ya musu Addu'ar Allah ya raya ya kama gabansa, to shi ko qaddara ta fito da Humaira ai yasan ba sa'ar auransa bace dan bashida abinda ze riqeta dashi ta saba da rayuwar jin dadi me zatayi dashi da har yanzu neman madafa yakeyi babu abinda ya ajiye.
Ranar Suna yaro yaci sunan Mukhtar sunan Mahaifin Mansur Amininsa kuma Mijin Mama mariqiyar Humaira kenan. Har kuka Maman tayi da wannan kara daya musu, kullum burin Mansur kenan a haifar masa Namiji ya saka sunan Mahaifinsa yayansa biyar yanzu duk mata Khalil be gaya musu sunan yaron ba har se ranar sunan da Safe dan data dameshi da tambaya cewa yayi kawai ta samar masa Laqabi se ranar suna zataji, aiko Yayan Mama sunji dadin wannan kara a gidan Hajiya kuwa ana fadar sunan Jalilah tayi tsallen Arbarka tace qarya yake, sunan Abban Umaimah ya saka. Hajiya ta riqe baki tana cewa
"Jalilah jidalinki yawa ne dashi, yanzu sunan ma se kin janyo magana akai"
"To idan qarya nakeyi Hajiya ya fada mana, babu wani sunan Baba me Mota daya saka (haka suke kiransa da suna yara) sunan tsohon sirikinsa ya saka ze wani fake da haka"
"Toh Jalilah ko sunan Abba na saka ai babu aibu a ciki dan Abba uba nane kuma ya isa da nayi masa takwara, karki tunzurani idan ta sake haihuwa na sake maimaita Mukhtar" ya fada mata kaitsaye ta tafa hannaye tana cewa
"Eh lallai Allah ya tsamoka Khalil a kwale kwalen Asiri kake yawo babu kuma wani ka sake sakawa daman shi ka saka kuma sena zuga Humairan akan me za'a saka mata sunan uban kishiya, kishiyar ma yar iska mara mutunchi"
"Kiyita rage mata zunubi kina jibgawa kanki" ya fada yana ficewa dan inya zauna se sun haura sauran yan uwan kuwa dariya suke musu kawai dramar tagwayen bata qarewa su basu ganin sun girma sun haura Arba'in inji Jamila amma kullum kamar wasu yan sha takwas, mita ta dira akan me za'a saka sunanda Hajiya ta gaji tace
"Ke dai in baki sararawa kanki ba ciwon damuwa ne ze kasheki kafin lokacinki yayi, ni banga dalilin dorawa kai damuwar wani ba taka ba. Umaimar nan fa baki isa ki kankareta daga cikinmu ba, yaya uku ta haifawa dan uwanki gasu nan duk inda akaje aka dawo fa an hadu babu yanda za'ayi a rabu kuma Alhaji Sabo Dattijo ne kuma in ma shiya saka banga laifinsa ba dan ya masa abinda uba yakewa Dansa haba ki rage wannan zazzafar qiyayyar taki Yayanta suna girmamaki karki bari su fahimci qin da kikewa uwarsu ba zasuji dadi ba kuma kema zasu iya qinki a dalilin haka dan duk yanda uwa take Yayanta suna sonta.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*
Page 85
Sha tara ta arqizi iyalan gidan Alhaji Sabo suka hada na kayan barka bisa karamchin da suka ce an musu na maida sunan mahaifinsu. Mama da Anty suka shirya Khalifa ya kaisu gidan Hajiya, Mama ta ringa kallon gidan abubuwan da suka faru a ranar data saka qafarta na qarshe na dawo mata shekaru kusan biyar kenan kota layin bata sake biyowa ba se yau din nan tunanin yanda zata sake kallon idon Hajiya takeyi a haka akayi musu iso cikin falon Hajiyar daya sake qawatuwa fiye da da.
Hajiya rasa inda zata sakasu tayi saboda murna, tasa aka ringa kawo musu abubuwan motsa baki yanda take haba haba dasu duk yasa kunya ta sake dabaibayesu jikinsu ya qarara sanyaya da lamarin karamchi irin nata. Tabbas Umaimah tayi asarar Sirikar kirki da samun irinta keda matuqar wahala a wannan zamani. Seda ta gama cika musu gaba da abubuwan ciye ciye kafin ta zauna suka shiga gaisawa. Da suka tado zancen baya ma hade fuska tayi ta nuna musu ita a gurinta komai ya wyce, ashe qullatarsu sukayi shiyasa suka yanke zumunchi dasu Mama da Anty suka hau rantse rantsen ba haka bane yanda suka rude yasa tayi dariya tace
"Komai ya wuce wlh kuma kamar yanda nasha fada miki nayiwa Umaimaha uzuri ba halinta bane kuskure aka samu tareda zugar shaidan data mugayen qawaye amma komai ya wuce sedai muyi fatan hakan ya zama Alkhairi a rayuwarsu gaba daya, Allah kuma ya fito mata da wani Mijin idan kuma da rabon daidaitawa se kiga an koma".
Daga Anty har Maman kasa amsa mata maganar qarshen sukayi dan basu da tabbacin har zuci tayita seta sako musu wata hirar tun suna dararewa har suka saki jiki akayi ta labarin duniya. Duk abinda aka ajiye musu Mama dai Lemo kadai tasha se Dubulan Anty kuwa ta zage taci abinda ya mata dan daman ita bata iya fulako ba. Sun jima kafin Hajiya ta shirya tace suje can gidan su Humairan suga Baby tunda bata dawo ba, a compound suka hadu da Khalil daya dawo daga Abuja saukarsa kenan ya shigo gidan suka hadu ya ringa sunkuyar da kai qasa kamar ze kwanta musu saboda ladabi ya gaida su Maman, ta amsa tana murmushi Anty ce tadan jashi da wasan data saba yi masa kafin suka masa barka suka tafi.
A mota Mama ta yiwa Hajiya zancen Bibi daya tsaya mata a rai danma suna makaranta shiyasa zancenya kwanta mata tun suna zaune se a motar ta tuna.
"Wlh Hajiya muna iyakar qoqarinmu, tabarar takwarata ai da ba'a kwabarta da abin seyafi haka dukda laifin Ubanne kuma shima ina tsawatar masa akan abinda yakeyi sam be kamata ba dan har yan uwan sun fara nuna rashin jin dadinsu dan idan abu ya hadosu tofa ko itace mara gaskiya ze shigar mata seda naci mutumchinsa akan haka na kuma gaya masa ze raba kan yayansa ne sa kansa. Ga wata yar banzar qawa da take da ita a makaranta da take qara dora mata karatun iyashege duk wani abun rashin kirki da kika ga tayi zakiji a gurinta ta koyo ga magana kamar Goyon tsohuwa, nidai na gayawa Uban ya canza mata makaranta tunda daman Idan sun gama Jarabawar zangon nan yace Sakandire zata shiga to ya kaita wata makarantar dan barin yaranka da irin qawar nan tata hadarine, kana tarbiyya suna warware maka kullum cikin tura mata mugayen aqidun qin matar ubanta da Yan dan uwanta takeyi, karkiso kiga yanda take hantarar yaron nan Auwalu da duka tun uwar tana kawaici har takai ta fara magana to yanzu dai abin yayi sauqi tunda Hasanar uban ta zaneta kwanaki da cewa ma tayi zata dauketa yaqi to nima ban matsa ba dan Azabar Jalilah tayi yawa, nata yayanma suka samu suka ballo bason koma mata suke ba dan ta fiya jaraba amma iya qoqari munayi Hajiya sedai mu qara".