Sashe 247
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
GIDAN KHALIL
Rayuwa taci gaba da tafiyarwa da ma'auratan cikin aminci da yarda da Juna, cikin Humaira ya shiga watan haihuwa, da kyar da lallami Khalil ya janye qudurinsa na canza mata Asibiti tunda ya tabbatar da cewar a nan Asibitin da suke zuwa Noor tsohon saurayinta yake aiki. Tun ganinsu dashi na farko hankalinsa ya kasa kwanaciya, haka kawai gabansa ya ringa faduwa idan ya tuna irin farin cikin daya gani akan fuskarta a dalilin ganin Noor din daya tabbatar shita fara so kafin shi. Da sati ya zagayo zata koma Asibiti tare sukaje dukda tarin ayyukan da suke kansa haka ya share ya tare ya tsare har seda ta gama komai ya maida ita gida kafin ya wuce office, seda suka jera sati biyu yana kaita kullum sukaje kuma se yaga Noor din amma baya taba bari su hadu da Humairan.
Haka kawai ta tashi da rigima a cewarsa kenan wai bata jin dadi ita Asibiti zataje, takaici ya qumeshi, daman kwana sukayi suna rikicinta da bashida qarshe yanzu da cikin ya tsufa lamarin ta qara tabarbarewa yakeyi kullum cikin nemansa da magana take tana sane tun dare ya gaya mata zeje Katsina duba wani aiki amma safiya nayi ta shiga riqe qafa wai ciwo take mata bata iya tafiya dole yace ta shirya su tafi Asibitin. Har sun fito ze kaita Jamila ta kirashi Danta ya fado daga Bene kansa ya fashe gashi babu kowa a gidan Babansu baya nan ita kuma bata iya mota ba daman ta roqeshi akan ya tura mata Khalifa idan yana gida ta kira bata same shi ba.. Khalifan baya gari yana Dutse inda yake aiki a CBN dinsu dole ya bar Humairan ta tafi da Driver shi kuma ya wuce gidan Jamilan ya daukesu ita da yaron da yake ta kuka saboda yanda yaji jiki, seda sukaje Asibiti aka fada musu bayan fashewar kan ya samu karaya a Hannunsa na hagu da Targade a yatsun qafa.
Suna Asibitin amma hankalinsa yana kan Humaira, ya kira wayarta ta ringa qara bata dauka ba ya sake kira nan ma haka seya maida akalar kiran ga Manniru inda ya sanar dashi har sannan suna Asibitin basu fito ba. Ganin da yayi anyi stabilizing Amir, duk sun liqe masa ciwu kan har an bashi gado yasa shi cewa Jamilan zeje ya dawo
"Ai bama seka dawo ba kawai ka tafi aikinka tunda komai ya daidaita munyi waya da Babansu yana hanya ze zo shima nagod kwarai Allah ya qara zumunchi" Jamilan ta fada seya fita bayan ya sake yiwa Amir din fatan samun sauqi. Zuciyarsa cike da wasiwasin abinda ze hanata daukar wayarsa, ya saqa wancan ya kwance shaidan na son kawo masa wasi wasi yana kaucewa shi a haka ya qarasa Asibitin. Kai tsaye office din likitan da take gani ya wuce ta sanar masa da ta turata Lab ayi mata test ita dinma zaman jiran ta kawo mata result takeyi dan ta gama sallamar kowa ita kadai ta rage seya wuce Lab din zuciyarsa na bugawa da qarfi, daga inda yake tsaye yana kallonsu ta cikin Glass Noor din riqe da hannun Humaira ya daure sangalalen da farar roba yana shafa inda jijiyoyinta suke fuskarsa dauke da wani murmushi da Khalil ya fassara daban ita kuma ta shagwabe fuska harda kwalla a idonta irinta me tsoron Allura.
Daga wajen ya tsaya saboda yanda qafarsa tayi masa nauyi amma zuciya ta harziqo masa har wani rawa jikinsa ya dauka cikin zafin nama ya tura qofar Lab din ba tareda ya bi dokar hana mutane shiga dake rubuce a jikin qofar ba yana shiga beyi wata wata ba ya make hannun Noor dake shirin sokawa jijiyar daya nemo Allura dan ya debi jini da qarfin da Allah ya bashi, Allurar ta fadi qasa shi kuma ya miqe a razane dan jiyayi kamar ya kwada masa rodi a hannun saboda zafi ya ware ido yana kallon Khalil kamar yanda shima yake kallonsa tsoron yanayinsa ya shigeshi da kuma gargadin da Dr Al'amin mamallakin Asibitin ya kirashi takanas yayi masa akan Matar mutumin daya kira Khalil.
Ya kalli Humairan ya kalli Noor gaba daya sunyi tsilli tsilli kamar ace musu ket su fece da gudu, shi fargabar rasa aikinsa ceta cikashi wanda dashi yake riqeda mahaifiyarsa da qanwarsa dan tun bayan da aka raba musu gado Yayyensu da suke uba daya suka dena yi musu komai Mijin data aura kuwa daman dashi gara babu dole yayi nutsuwar dole ya koma makaranta ya saki Aikin Sojan daya kwallafa rai akai da rayuwar shaye shayen daya fara dalilin rasa Humairan ganin Rayuwar Mahaifiyarsa na nema shiga garari na rashin mataimaki, yana kuma gama karatun ya samu aiki a wannan Asibitin da taimakon wani Malaminsu da suke shiri sosai kuma abokin Dr Al'amin ne, ko sanda ya kirashi yayi masa kashedin kula Humaira seda ya kira Malamin ya zamar musu shaida yanzu idan labari ya komawa Director yasan korarsa kawai zeyi wannan tunanin ya sakashi kai guiwoyinsa qasa ya dage hannaye yana cewa
"Dan girman Allah kayi haquri kayi mun rai gasu nan ka tambaye su muna zaune ta shigo Lab din nan kuma duk sunyi sun kasa samun jijiyarta shiyasa ma karba wlh bada wata manufa nayi ba karka ce zaka hadani da Dr ni bani na gayyato ta ba da kanta tazo". Wani matsiyacin kallo Khalil din ya jefa masa ya sake kallonta ta sunkuyar da kai qasa ta kasa koda motsi a gurin seya ja tsaki ya juya kamar iska ya fice. Badan karya zubda mutunchinsa ba kuma duk inda akaje doka zata bashi rashin gaskiya dase ya nadawa yaron dukan tsiya a gurin. Da sauri kamar zata fadi tabi bayansa ganin ya nufi hanyar fita, ita kam yau ta shiga dari ma ba uku ba tsautsayine ya sakata zuwa Asibitin data sani ta daure ciwonta tayi zamanta kota bari seda daddare kamar yanda yace mata tun farko yanzu ta tabbata fassara daban zeyiwa Al'amarin saboda yanda yake tafiyar cikin fushi kafin ta fito harabar Asibitin fuce da motarsa babu bata lokaci ta shige itama Manniru yajata. Text ya shigo wayarsa ta bude hannunta na rawa tana ganin abinda yake ciki ta fashe da kuka kawia tana cewa Manniru Sharada ze kaita.
Hankalin Mama Hauwa ya tashi da ganin Humairan dan a safiyar ma sunyi waya kuma bata ce mata zatazo ba sannan gata ta shigo tana kuka ta ringa tambayarta meya faru ta kasa bata amsa se Kuka dan bata san me zata ce ba, tana gudun suyi mata gurguwar fahimta kamar yanda Khalil din yayi ganin taqi shiru kuma taqi magana Mama ta dauki waya tana cewa
"Bari na kira Hajiyar naji ko wani abun ne ya faru a gidan tunda kin kasa magan" se tayi saurin riqeta tana cikin kuka tace
"Aa Mama karki kirata zece nakai qararsa, sabani muka samu da Yah Khalil yace na taho gida Hajiyan ma bata sani ba". Salati Mama ta dauka bayandata ajiye wayar tana kallonta tace
"Yace ki taho gida? Me kika masa Humaira? Daman Sumayya ta gayamun kin saka jaraba a ranki gana daya kin kwarzabi rayuwarki kikayi haquri a sanda ma babu se yanzu rashin qoshi ze saka ki tayar da hankali to auran kike so ki kaso ki dawo gida kome?"
"Ni wlh Mama ba wannan bane, laifi na masa daban yayi fushi amma nasan yana hucewa ze zo ya daukeni" ta fada tana kauda fuska tareda tura baki gaba. Daman ita Anty Sumayya matsalarta kenan Hansfiri ba'a maganar sirri da ita Anty Unaizatu kuwa kunya tasa ta kasa buda mata sirrin tasan lafiya lau da babu Wanda zeji amma yanzu ace har kunnen Mama ba zatayi mamaki ha idan Yah Habib ya sani ma.
"Kyaci ubanki sakarya da bata da wayo, idan kikayi sagegeduwar da auran ya mutu ke kika sani kin ga kinyi tutar babu, kuma abinda kike rainawa wata idan ta samu godiya zatayi banda mafitina kina fama da kanki kina jaye jayen magana yanzu daya koroki ai shikenan" Maman ta sake fada kafin ta shige daki tana mita. Tunda Sumayya ta mata zancen har tace zata kira Humairan ta hanata a ganinta sunyi maganar sirri idan ta saka baki gana ba zata sake gaya masa cikinta ba.
Humaira kuwa dakinta nada ta shige itama ta kwanta kukan da tayi yasa kanta yake mata ciwo ta kira layinsa duka biyu a kashe ta tabbata kuma kashewa yayi alamar fushin nasa me yawane amma ai ya kamata ya bata dama ta kare kanta ba wai kawai ya yanke hukunci daga abinda ya gani ba.
Har Magriba tana gidan cike da zullumi dan har sannan wayar Khalil a kashe take sannan nabu wanda ya biyo sahunta. Ruqayya ta kirata tun da yamma akan Aryaan da Imaan sun dawo makaranta sunata rigimar nemanta tace ta rarrashe su tana gidan Mama idan Dadynsu ya tashi ze biyo ya dauketa se ce mata tayi ai ga Dadyn a gida tun gurin sha biyu ya dawo gabamta ya fadi kenan daga Asibitin gidan ya wuce lallai abun Azimun ne ita take daukarsa wasa. A sanyaye tayiwa Ruqayyan Sallama akan zata kirashi yanzu. Mama dake tsaye a bakin qofa da Hijabin data idar da sallah ta qarasa ciki tana kallonta tace
"Laifin me kika masa idan na sasanci ne ayi tun wuri ki tattara ki komadan bazaki kwanar mun a gida ba idanba haka ba kuma sedai ki tafi gidan Unaiza tunda tun Asali daman ita take zugaki ko kashe auranki, se kace ba gara nako Mijin ma da nata ba".
Rayuwa taci gaba da tafiyarwa da ma'auratan cikin aminci da yarda da Juna, cikin Humaira ya shiga watan haihuwa, da kyar da lallami Khalil ya janye qudurinsa na canza mata Asibiti tunda ya tabbatar da cewar a nan Asibitin da suke zuwa Noor tsohon saurayinta yake aiki. Tun ganinsu dashi na farko hankalinsa ya kasa kwanaciya, haka kawai gabansa ya ringa faduwa idan ya tuna irin farin cikin daya gani akan fuskarta a dalilin ganin Noor din daya tabbatar shita fara so kafin shi. Da sati ya zagayo zata koma Asibiti tare sukaje dukda tarin ayyukan da suke kansa haka ya share ya tare ya tsare har seda ta gama komai ya maida ita gida kafin ya wuce office, seda suka jera sati biyu yana kaita kullum sukaje kuma se yaga Noor din amma baya taba bari su hadu da Humairan.
Haka kawai ta tashi da rigima a cewarsa kenan wai bata jin dadi ita Asibiti zataje, takaici ya qumeshi, daman kwana sukayi suna rikicinta da bashida qarshe yanzu da cikin ya tsufa lamarin ta qara tabarbarewa yakeyi kullum cikin nemansa da magana take tana sane tun dare ya gaya mata zeje Katsina duba wani aiki amma safiya nayi ta shiga riqe qafa wai ciwo take mata bata iya tafiya dole yace ta shirya su tafi Asibitin. Har sun fito ze kaita Jamila ta kirashi Danta ya fado daga Bene kansa ya fashe gashi babu kowa a gidan Babansu baya nan ita kuma bata iya mota ba daman ta roqeshi akan ya tura mata Khalifa idan yana gida ta kira bata same shi ba.. Khalifan baya gari yana Dutse inda yake aiki a CBN dinsu dole ya bar Humairan ta tafi da Driver shi kuma ya wuce gidan Jamilan ya daukesu ita da yaron da yake ta kuka saboda yanda yaji jiki, seda sukaje Asibiti aka fada musu bayan fashewar kan ya samu karaya a Hannunsa na hagu da Targade a yatsun qafa.
Suna Asibitin amma hankalinsa yana kan Humaira, ya kira wayarta ta ringa qara bata dauka ba ya sake kira nan ma haka seya maida akalar kiran ga Manniru inda ya sanar dashi har sannan suna Asibitin basu fito ba. Ganin da yayi anyi stabilizing Amir, duk sun liqe masa ciwu kan har an bashi gado yasa shi cewa Jamilan zeje ya dawo
"Ai bama seka dawo ba kawai ka tafi aikinka tunda komai ya daidaita munyi waya da Babansu yana hanya ze zo shima nagod kwarai Allah ya qara zumunchi" Jamilan ta fada seya fita bayan ya sake yiwa Amir din fatan samun sauqi. Zuciyarsa cike da wasiwasin abinda ze hanata daukar wayarsa, ya saqa wancan ya kwance shaidan na son kawo masa wasi wasi yana kaucewa shi a haka ya qarasa Asibitin. Kai tsaye office din likitan da take gani ya wuce ta sanar masa da ta turata Lab ayi mata test ita dinma zaman jiran ta kawo mata result takeyi dan ta gama sallamar kowa ita kadai ta rage seya wuce Lab din zuciyarsa na bugawa da qarfi, daga inda yake tsaye yana kallonsu ta cikin Glass Noor din riqe da hannun Humaira ya daure sangalalen da farar roba yana shafa inda jijiyoyinta suke fuskarsa dauke da wani murmushi da Khalil ya fassara daban ita kuma ta shagwabe fuska harda kwalla a idonta irinta me tsoron Allura.
Daga wajen ya tsaya saboda yanda qafarsa tayi masa nauyi amma zuciya ta harziqo masa har wani rawa jikinsa ya dauka cikin zafin nama ya tura qofar Lab din ba tareda ya bi dokar hana mutane shiga dake rubuce a jikin qofar ba yana shiga beyi wata wata ba ya make hannun Noor dake shirin sokawa jijiyar daya nemo Allura dan ya debi jini da qarfin da Allah ya bashi, Allurar ta fadi qasa shi kuma ya miqe a razane dan jiyayi kamar ya kwada masa rodi a hannun saboda zafi ya ware ido yana kallon Khalil kamar yanda shima yake kallonsa tsoron yanayinsa ya shigeshi da kuma gargadin da Dr Al'amin mamallakin Asibitin ya kirashi takanas yayi masa akan Matar mutumin daya kira Khalil.
Ya kalli Humairan ya kalli Noor gaba daya sunyi tsilli tsilli kamar ace musu ket su fece da gudu, shi fargabar rasa aikinsa ceta cikashi wanda dashi yake riqeda mahaifiyarsa da qanwarsa dan tun bayan da aka raba musu gado Yayyensu da suke uba daya suka dena yi musu komai Mijin data aura kuwa daman dashi gara babu dole yayi nutsuwar dole ya koma makaranta ya saki Aikin Sojan daya kwallafa rai akai da rayuwar shaye shayen daya fara dalilin rasa Humairan ganin Rayuwar Mahaifiyarsa na nema shiga garari na rashin mataimaki, yana kuma gama karatun ya samu aiki a wannan Asibitin da taimakon wani Malaminsu da suke shiri sosai kuma abokin Dr Al'amin ne, ko sanda ya kirashi yayi masa kashedin kula Humaira seda ya kira Malamin ya zamar musu shaida yanzu idan labari ya komawa Director yasan korarsa kawai zeyi wannan tunanin ya sakashi kai guiwoyinsa qasa ya dage hannaye yana cewa
"Dan girman Allah kayi haquri kayi mun rai gasu nan ka tambaye su muna zaune ta shigo Lab din nan kuma duk sunyi sun kasa samun jijiyarta shiyasa ma karba wlh bada wata manufa nayi ba karka ce zaka hadani da Dr ni bani na gayyato ta ba da kanta tazo". Wani matsiyacin kallo Khalil din ya jefa masa ya sake kallonta ta sunkuyar da kai qasa ta kasa koda motsi a gurin seya ja tsaki ya juya kamar iska ya fice. Badan karya zubda mutunchinsa ba kuma duk inda akaje doka zata bashi rashin gaskiya dase ya nadawa yaron dukan tsiya a gurin. Da sauri kamar zata fadi tabi bayansa ganin ya nufi hanyar fita, ita kam yau ta shiga dari ma ba uku ba tsautsayine ya sakata zuwa Asibitin data sani ta daure ciwonta tayi zamanta kota bari seda daddare kamar yanda yace mata tun farko yanzu ta tabbata fassara daban zeyiwa Al'amarin saboda yanda yake tafiyar cikin fushi kafin ta fito harabar Asibitin fuce da motarsa babu bata lokaci ta shige itama Manniru yajata. Text ya shigo wayarsa ta bude hannunta na rawa tana ganin abinda yake ciki ta fashe da kuka kawia tana cewa Manniru Sharada ze kaita.
Hankalin Mama Hauwa ya tashi da ganin Humairan dan a safiyar ma sunyi waya kuma bata ce mata zatazo ba sannan gata ta shigo tana kuka ta ringa tambayarta meya faru ta kasa bata amsa se Kuka dan bata san me zata ce ba, tana gudun suyi mata gurguwar fahimta kamar yanda Khalil din yayi ganin taqi shiru kuma taqi magana Mama ta dauki waya tana cewa
"Bari na kira Hajiyar naji ko wani abun ne ya faru a gidan tunda kin kasa magan" se tayi saurin riqeta tana cikin kuka tace
"Aa Mama karki kirata zece nakai qararsa, sabani muka samu da Yah Khalil yace na taho gida Hajiyan ma bata sani ba". Salati Mama ta dauka bayandata ajiye wayar tana kallonta tace
"Yace ki taho gida? Me kika masa Humaira? Daman Sumayya ta gayamun kin saka jaraba a ranki gana daya kin kwarzabi rayuwarki kikayi haquri a sanda ma babu se yanzu rashin qoshi ze saka ki tayar da hankali to auran kike so ki kaso ki dawo gida kome?"
"Ni wlh Mama ba wannan bane, laifi na masa daban yayi fushi amma nasan yana hucewa ze zo ya daukeni" ta fada tana kauda fuska tareda tura baki gaba. Daman ita Anty Sumayya matsalarta kenan Hansfiri ba'a maganar sirri da ita Anty Unaizatu kuwa kunya tasa ta kasa buda mata sirrin tasan lafiya lau da babu Wanda zeji amma yanzu ace har kunnen Mama ba zatayi mamaki ha idan Yah Habib ya sani ma.
"Kyaci ubanki sakarya da bata da wayo, idan kikayi sagegeduwar da auran ya mutu ke kika sani kin ga kinyi tutar babu, kuma abinda kike rainawa wata idan ta samu godiya zatayi banda mafitina kina fama da kanki kina jaye jayen magana yanzu daya koroki ai shikenan" Maman ta sake fada kafin ta shige daki tana mita. Tunda Sumayya ta mata zancen har tace zata kira Humairan ta hanata a ganinta sunyi maganar sirri idan ta saka baki gana ba zata sake gaya masa cikinta ba.
Humaira kuwa dakinta nada ta shige itama ta kwanta kukan da tayi yasa kanta yake mata ciwo ta kira layinsa duka biyu a kashe ta tabbata kuma kashewa yayi alamar fushin nasa me yawane amma ai ya kamata ya bata dama ta kare kanta ba wai kawai ya yanke hukunci daga abinda ya gani ba.
Har Magriba tana gidan cike da zullumi dan har sannan wayar Khalil a kashe take sannan nabu wanda ya biyo sahunta. Ruqayya ta kirata tun da yamma akan Aryaan da Imaan sun dawo makaranta sunata rigimar nemanta tace ta rarrashe su tana gidan Mama idan Dadynsu ya tashi ze biyo ya dauketa se ce mata tayi ai ga Dadyn a gida tun gurin sha biyu ya dawo gabamta ya fadi kenan daga Asibitin gidan ya wuce lallai abun Azimun ne ita take daukarsa wasa. A sanyaye tayiwa Ruqayyan Sallama akan zata kirashi yanzu. Mama dake tsaye a bakin qofa da Hijabin data idar da sallah ta qarasa ciki tana kallonta tace
"Laifin me kika masa idan na sasanci ne ayi tun wuri ki tattara ki komadan bazaki kwanar mun a gida ba idanba haka ba kuma sedai ki tafi gidan Unaiza tunda tun Asali daman ita take zugaki ko kashe auranki, se kace ba gara nako Mijin ma da nata ba".