Sashe 144
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Me ya hadaku?" Alhaji Garba ya jefo masa tambayar, ya sakeyin shiru kafin ya nisa yace
"Laifi tayi mun kuma daman ta dade tana mun abu ina tarata shiyasa yanzu na bata hutu ko zatayi hankali ta dena abubuwan da takeyi" Khalil din ya fada kamar baya so se Alhaji Garba yayi murmushi yace
"Zuwa yau da Magriba idan kana da lokaci kazo nayi magana da Kawunku Alhaji Abubakar se muje can gurin iyayen nata tareda kai a sasanta, zaman aure ko ina haquri akeyi Ibrahimu su mata duk daya suke wani lokacin in sukayi maka abu seka rasa hukuncin da zaka dauka akansu amma haka ake shanyewa aci gaba da zama. Kayi haquri ta dawo dakinta kodan halin da take ciki an rigada an fara tara zuri'a be kamata ace shekarun da aka kwashe ana zaune qalau ba se yanzu ne da girma ya fara hawanku matsaloli zasu fara bullowa, mutane da magana yanzu se kaji wani abu na daban ace ka fara wulaqanta matarka saboda ka samu budin rayuwa baza'a binciki kai me takeyi maka ba".
Kamar ze rusa kuka haka ya amsawa Alhaji Garban badan yana so ba sedanbaze iya musu dashi ba. Haka sukayi sallama yana ayyana ko sunje Umaimah ba zata dawo masa gida a yanzu ba, a gaban iyayennata ze fadi abinda tayi masa ai sun san ya dade yana shanye takaicinta idan kuma za'a masa Adalci yanzu daya ce ta tafi baza'a takura masa ya dawo da ita ba.
Gida ya wuce ya tarar da Hajiya na fama da Rigimar Bibi data dawo daga gidan Jamila jiya tana ta kukan ina Mummynta, Mu'ayyad dai daman tunda ya tambayi tana ina akace tana gidan Mama yaci gaba da sabgarsa Bibin ce me rigima Hajiya nata lallabata taqi Khalil na shigowa tace
"Yawwa, gatan tunda taje ta buga qofarku ba'a bude ba ta tasa kukan Mummy bayanda ba'ayi da ita tayi shiru ba taqi haqura ko za'akai mata ita can gidan ne?"
"Babu inda zataje" ya fada yana kamo hannun Bibin ta fada jikinsa tana Dady zanje Mummy akaini gurin Mummy"
"Zakisha Ice cream?" Ya fada yana goge mata hawaye, dake sarkin son zaqi ce nan ta daga kai da sauri tana cewa
"Harda Chocolate da Pizza, Mummy J is not letting me eat some chocolate"
"Oh Mummy J bata kyauta ba, maza kije Raziqa tayi miki wanka muje mu siyo yanzu" Khalil ya fada yana jan kumatunta ta kusa yi murmushinta me kyau kafin ta falla da gudu Hajiya na cewa tayi a hankali.
Kallonta ta mayar kan Khalil da gaba daya ya rame a yan kwanakin nan tace
"Khalil baka cin abinci ne ko kaga yanda ka zabge kuwa"
Murmushi kawai yayi yaqi ce mata komai, seta sake cewa
"Yanzu dai ai ranka yayi sanyi ya kamata kaje ka dawo da matarka haka babu dadi ka barta a gida ga ciwo nasan iyayen sun zuba ido ne suga gudun ruwanmu kafin su biyo ba'asin abinda ya samu yarsu dan kwana biyu idan na kira mahaifiyarta ma naji jikin yanda take amsa mun nasan suna cike damu".
"Baban Qoqi ya kirani, yace sunyi magana da Baba Habu wai yau zamuje can gidan amma ni gaskiya Hajiya ki kirashi kice yayi haquri ya qaramun lokaci" Khalil ya fada se Hajiya ta kama baki tace
"Au magana na fika iyawa kome dakai ka kasa gaya masa hakan seni kake so na fada? Ok so kake ka janyo mun bakin duniya ace ni na saka ka kori matarka ko? To ahir dinka ka kuma fita a ido na. Har wani abin duniya daka rasa yafi ta a gurinka da zaka dauki fushi ka hana ranka sakat saboda shi, rabo ne bana ka ba kuma koda ba'ayi hakan ba bazaka samu na se Allah ya kawo wani sanadin da ze saka ka rasa ballantana ka zauna kanayiwa mutane baqin rai in ka haqura ka dangana se kaga Allahn ya maida maka da wanda yafi haka"
"Da se ta bari wani silar ya gifta ai base ta zubar mun da mutunchi taja mun bala'i ba, Hajiya na fuskanci baki san girman Asarar da Umaimah ta jawo mun ba ko? Kinsan qarfin Dr Sabitu a cikin gwamnati kuwa? Kinsan abinda ze iya yi?
Hajiya yau idan yaga dama yace a rufe company na take za'ayi haka babu me tambayarsa dalili ko yanzu dukda Uncle Mus'ab da wasu abokanansu sun shiga ciki an sasanta kina zaton har zuciyarsa ya haqura ne musamman da ita yar tasa da yake komai saboda ita yanzu haka fa tana Asibiti bata da lafiya saboda ance na fasa auranta.
Ni kadai nasan damuwar da nake ciki Hajiya amma idan na rasa komai dani da itan daku duk tare zamu zauna musha wahalar" ya fada yana miqewa cikin sabon bacin ran daya taso masa. A rutsin nan banda wannan babbar kwangilar seda ya rasa wasu guda biyu daya har sun fara ginin ma mutumin ya kirashi yace ya dakata ashe wai Surukin Dr Sabitun ne yana auren yar yayanshi, to idan aka ci gaba da haka ai yana cikin cakwakiya banda qungurmar Asarar record din Ayyukansa na baya wasu tun kafin ya shiga Jami'a yake zanensu yana ajiyewa seda ya nutsu yaga ashe ba iya waccen folder ta taba ba wannan Ifrituwar matar ta goge komai ai wallahi idan ya maidota nan da shekara daya ma ya mata Adalci adai abinda tayi masa.
"In sha Allahu bazamu shiga wahala ba babu kuma abinda ze iyayi maka ai Allah ne yakeyi bashi ba kuma dashi muka dogara. Kayi haquri kawai ita jarabawar ubangiji babu ta inda bata fa bawa idan kuma kayi haquri se kaga ka tsallake ta, yanzu dai kuje din kuma duk yabda iyayenka sukace kayi karka musa musu kaji ko" Hajiya ta fada Khalil kuwa tafiya yaci gaba dayi yana jinta kawai, Indai Umaimah ce ai gata gatanan, sedai Allah ya kiyaye randa zata hado su kawai.
UMAIMAH
Seda ta kwana biyu a gidan kafin ta iya fara hadiyar abinci da kyau saboda yanda wuyanta ya daure dan ba qaramar shaqa Khalil din yayi mata ba. Sau daya Mama tayi mata tambayar meya hadasu ta saka mata kuka dan bata san me zatace ba. Idan tayi qarya kuma gaskiya ta fito daga baya ita ce a ciki haka in ta fadi gaskiyar ma ba fita zatayi ba dan qila qarasa shaqeta Maman zatayi kawai dan bata manta kashedin datayi mata lokacin case din Hadiza ba, taja mata kunne ta gargadeta tace mata yau ko cikin gidanta Khalil ya dakko mace ya kawo koda wasa karta kuskura ta ce zata dauki wani hukunci a hannunta, ta gaya mata kota kira yan uwanta karta yarda tayi amfani da tunanin da kwakwalwarta take bata to yanzu idan taji akan Macen ta sake wannan aika aikar ai qarasata zatayi kowa ya huta.
Anty Laure ce take kareta duk sanda aka tada maganar jin meya hadasu ita zata shiga zayyano qarya da gaskiyar abinda take hasashe, tace Kule kulen mata yakeyi dan kullum seta ganshi yana waya yana dariya ko yayi wanka ya fice da daddare tsabar sharri cewa tayi sau biyu tana tsintar dan kunnen Mace akan Dan Table din da yake ajiye muqullin mota da yake a bakin qofar palour qasan wai yana ajiyesu tare be sani ba, ita ta gama concluding neman mata yakeyi shine ta gane sukayi rigima ya shaqeta Umaimah dai in tana bada labarinta sedai ta sunkuyar dakai, jira take ta sake jin dama dama ta neme shi ta bashi haquri salin Alin ba se wani yaji abinda ta aikata ba.
Kwananta biyar Baba Abdullahi yazo gidan da safe Abba ya kirawo shi, tana zaune gaban Murhun gawayi Anty na soya musu qosai dan ranar Kunun gyada da qosai tace tana sha'awa Baba Abdullahin ya shigo ta gaishe shi yace
"Ke me kike a gidan nan da sassafe haka, badai nan kika kwana ba?"
Qasa kawai tayi dakai suka gaisa da Anty ya wuce bayan tace masa Abban yana ciki shi yake jira.
Anty ta hada abin kari ta tafi kai musu tana cewa Umaimah
"Kince se me zafi gashi nan a gabanki kuma kin bari yana hucewa".
Umaimah ko gaba daya Kosan ne ya fita a ranta, bata so Abba ya kira Baba Abdullahi ba tasan yanzu Asirinta ze tonu bayan yau take shirin ta kira Khalil ta lallaba abunta yazo su tafi salin Alin babu wanda yaji amma yanzu Abba ya rusa komai, Baba Abdullahi da taratsinsa zuwa zeyi yace zeyi masifa in jayi an dake tan daga nan kuma liqi ya balle.
A cikin palour Abba kuwa fada Baba Abdullahi yakeyi kamar ze hadiye harshensa yake cewa
"Wallahi Yaya bana jin dadin abinda kake mun musamman akan Umaimah, yanzu haka kwanaki yasa aka kulle yarinya a Cell kamar mara galihu ba'a gayamun ba, aka gama wannan ya jingineta a gida sama da wata biyar harta haihu yarinya tayi wayo sannan ta koma kawai dan kun nuna masa bata da gata in ba haka ba a ina ka taba ganin ana wannan abun da yakeyi?
Shikenan daga ta masa abu seya korota gida se sanda ya mula yace ta koma who does that?
Dan ubansa haka ake aure? Ko kuwa saboda an tsani yarinya ba'a bin ba'asi duk sanda suka samu matsala sedai a dora mata laifi ai qarfe daya baya Amo shi kadai amma kun rigada kun nuna masa bata da wani gata yayi yanda yaga dama da ita ai dole yanzu gashi nan anzo gabar da ya fara dukanta yana shaqeta, tunda yasan ko kasheta yayi qarshe ita za'a dorawa laifi ace ita ta nemi halakashi in the process of self defence ya kasheta ko to wallahi bazata sabu ba, ni ina son abata in ku duk bakwaso zan kuma kwato mata haqqinta daga nan police station zanje in aka bi mata kadin Shaqeta da yayi sannan yazo muji matsayar auran na gaji ya sallameta kawai ai ba rasa masu auranta zatayi ba yarinya da kyanta da komai bazata zauna baqin cikin Miji ya kasheta ba bayan ta gama shan naku.
"Laifi tayi mun kuma daman ta dade tana mun abu ina tarata shiyasa yanzu na bata hutu ko zatayi hankali ta dena abubuwan da takeyi" Khalil din ya fada kamar baya so se Alhaji Garba yayi murmushi yace
"Zuwa yau da Magriba idan kana da lokaci kazo nayi magana da Kawunku Alhaji Abubakar se muje can gurin iyayen nata tareda kai a sasanta, zaman aure ko ina haquri akeyi Ibrahimu su mata duk daya suke wani lokacin in sukayi maka abu seka rasa hukuncin da zaka dauka akansu amma haka ake shanyewa aci gaba da zama. Kayi haquri ta dawo dakinta kodan halin da take ciki an rigada an fara tara zuri'a be kamata ace shekarun da aka kwashe ana zaune qalau ba se yanzu ne da girma ya fara hawanku matsaloli zasu fara bullowa, mutane da magana yanzu se kaji wani abu na daban ace ka fara wulaqanta matarka saboda ka samu budin rayuwa baza'a binciki kai me takeyi maka ba".
Kamar ze rusa kuka haka ya amsawa Alhaji Garban badan yana so ba sedanbaze iya musu dashi ba. Haka sukayi sallama yana ayyana ko sunje Umaimah ba zata dawo masa gida a yanzu ba, a gaban iyayennata ze fadi abinda tayi masa ai sun san ya dade yana shanye takaicinta idan kuma za'a masa Adalci yanzu daya ce ta tafi baza'a takura masa ya dawo da ita ba.
Gida ya wuce ya tarar da Hajiya na fama da Rigimar Bibi data dawo daga gidan Jamila jiya tana ta kukan ina Mummynta, Mu'ayyad dai daman tunda ya tambayi tana ina akace tana gidan Mama yaci gaba da sabgarsa Bibin ce me rigima Hajiya nata lallabata taqi Khalil na shigowa tace
"Yawwa, gatan tunda taje ta buga qofarku ba'a bude ba ta tasa kukan Mummy bayanda ba'ayi da ita tayi shiru ba taqi haqura ko za'akai mata ita can gidan ne?"
"Babu inda zataje" ya fada yana kamo hannun Bibin ta fada jikinsa tana Dady zanje Mummy akaini gurin Mummy"
"Zakisha Ice cream?" Ya fada yana goge mata hawaye, dake sarkin son zaqi ce nan ta daga kai da sauri tana cewa
"Harda Chocolate da Pizza, Mummy J is not letting me eat some chocolate"
"Oh Mummy J bata kyauta ba, maza kije Raziqa tayi miki wanka muje mu siyo yanzu" Khalil ya fada yana jan kumatunta ta kusa yi murmushinta me kyau kafin ta falla da gudu Hajiya na cewa tayi a hankali.
Kallonta ta mayar kan Khalil da gaba daya ya rame a yan kwanakin nan tace
"Khalil baka cin abinci ne ko kaga yanda ka zabge kuwa"
Murmushi kawai yayi yaqi ce mata komai, seta sake cewa
"Yanzu dai ai ranka yayi sanyi ya kamata kaje ka dawo da matarka haka babu dadi ka barta a gida ga ciwo nasan iyayen sun zuba ido ne suga gudun ruwanmu kafin su biyo ba'asin abinda ya samu yarsu dan kwana biyu idan na kira mahaifiyarta ma naji jikin yanda take amsa mun nasan suna cike damu".
"Baban Qoqi ya kirani, yace sunyi magana da Baba Habu wai yau zamuje can gidan amma ni gaskiya Hajiya ki kirashi kice yayi haquri ya qaramun lokaci" Khalil ya fada se Hajiya ta kama baki tace
"Au magana na fika iyawa kome dakai ka kasa gaya masa hakan seni kake so na fada? Ok so kake ka janyo mun bakin duniya ace ni na saka ka kori matarka ko? To ahir dinka ka kuma fita a ido na. Har wani abin duniya daka rasa yafi ta a gurinka da zaka dauki fushi ka hana ranka sakat saboda shi, rabo ne bana ka ba kuma koda ba'ayi hakan ba bazaka samu na se Allah ya kawo wani sanadin da ze saka ka rasa ballantana ka zauna kanayiwa mutane baqin rai in ka haqura ka dangana se kaga Allahn ya maida maka da wanda yafi haka"
"Da se ta bari wani silar ya gifta ai base ta zubar mun da mutunchi taja mun bala'i ba, Hajiya na fuskanci baki san girman Asarar da Umaimah ta jawo mun ba ko? Kinsan qarfin Dr Sabitu a cikin gwamnati kuwa? Kinsan abinda ze iya yi?
Hajiya yau idan yaga dama yace a rufe company na take za'ayi haka babu me tambayarsa dalili ko yanzu dukda Uncle Mus'ab da wasu abokanansu sun shiga ciki an sasanta kina zaton har zuciyarsa ya haqura ne musamman da ita yar tasa da yake komai saboda ita yanzu haka fa tana Asibiti bata da lafiya saboda ance na fasa auranta.
Ni kadai nasan damuwar da nake ciki Hajiya amma idan na rasa komai dani da itan daku duk tare zamu zauna musha wahalar" ya fada yana miqewa cikin sabon bacin ran daya taso masa. A rutsin nan banda wannan babbar kwangilar seda ya rasa wasu guda biyu daya har sun fara ginin ma mutumin ya kirashi yace ya dakata ashe wai Surukin Dr Sabitun ne yana auren yar yayanshi, to idan aka ci gaba da haka ai yana cikin cakwakiya banda qungurmar Asarar record din Ayyukansa na baya wasu tun kafin ya shiga Jami'a yake zanensu yana ajiyewa seda ya nutsu yaga ashe ba iya waccen folder ta taba ba wannan Ifrituwar matar ta goge komai ai wallahi idan ya maidota nan da shekara daya ma ya mata Adalci adai abinda tayi masa.
"In sha Allahu bazamu shiga wahala ba babu kuma abinda ze iyayi maka ai Allah ne yakeyi bashi ba kuma dashi muka dogara. Kayi haquri kawai ita jarabawar ubangiji babu ta inda bata fa bawa idan kuma kayi haquri se kaga ka tsallake ta, yanzu dai kuje din kuma duk yabda iyayenka sukace kayi karka musa musu kaji ko" Hajiya ta fada Khalil kuwa tafiya yaci gaba dayi yana jinta kawai, Indai Umaimah ce ai gata gatanan, sedai Allah ya kiyaye randa zata hado su kawai.
UMAIMAH
Seda ta kwana biyu a gidan kafin ta iya fara hadiyar abinci da kyau saboda yanda wuyanta ya daure dan ba qaramar shaqa Khalil din yayi mata ba. Sau daya Mama tayi mata tambayar meya hadasu ta saka mata kuka dan bata san me zatace ba. Idan tayi qarya kuma gaskiya ta fito daga baya ita ce a ciki haka in ta fadi gaskiyar ma ba fita zatayi ba dan qila qarasa shaqeta Maman zatayi kawai dan bata manta kashedin datayi mata lokacin case din Hadiza ba, taja mata kunne ta gargadeta tace mata yau ko cikin gidanta Khalil ya dakko mace ya kawo koda wasa karta kuskura ta ce zata dauki wani hukunci a hannunta, ta gaya mata kota kira yan uwanta karta yarda tayi amfani da tunanin da kwakwalwarta take bata to yanzu idan taji akan Macen ta sake wannan aika aikar ai qarasata zatayi kowa ya huta.
Anty Laure ce take kareta duk sanda aka tada maganar jin meya hadasu ita zata shiga zayyano qarya da gaskiyar abinda take hasashe, tace Kule kulen mata yakeyi dan kullum seta ganshi yana waya yana dariya ko yayi wanka ya fice da daddare tsabar sharri cewa tayi sau biyu tana tsintar dan kunnen Mace akan Dan Table din da yake ajiye muqullin mota da yake a bakin qofar palour qasan wai yana ajiyesu tare be sani ba, ita ta gama concluding neman mata yakeyi shine ta gane sukayi rigima ya shaqeta Umaimah dai in tana bada labarinta sedai ta sunkuyar dakai, jira take ta sake jin dama dama ta neme shi ta bashi haquri salin Alin ba se wani yaji abinda ta aikata ba.
Kwananta biyar Baba Abdullahi yazo gidan da safe Abba ya kirawo shi, tana zaune gaban Murhun gawayi Anty na soya musu qosai dan ranar Kunun gyada da qosai tace tana sha'awa Baba Abdullahin ya shigo ta gaishe shi yace
"Ke me kike a gidan nan da sassafe haka, badai nan kika kwana ba?"
Qasa kawai tayi dakai suka gaisa da Anty ya wuce bayan tace masa Abban yana ciki shi yake jira.
Anty ta hada abin kari ta tafi kai musu tana cewa Umaimah
"Kince se me zafi gashi nan a gabanki kuma kin bari yana hucewa".
Umaimah ko gaba daya Kosan ne ya fita a ranta, bata so Abba ya kira Baba Abdullahi ba tasan yanzu Asirinta ze tonu bayan yau take shirin ta kira Khalil ta lallaba abunta yazo su tafi salin Alin babu wanda yaji amma yanzu Abba ya rusa komai, Baba Abdullahi da taratsinsa zuwa zeyi yace zeyi masifa in jayi an dake tan daga nan kuma liqi ya balle.
A cikin palour Abba kuwa fada Baba Abdullahi yakeyi kamar ze hadiye harshensa yake cewa
"Wallahi Yaya bana jin dadin abinda kake mun musamman akan Umaimah, yanzu haka kwanaki yasa aka kulle yarinya a Cell kamar mara galihu ba'a gayamun ba, aka gama wannan ya jingineta a gida sama da wata biyar harta haihu yarinya tayi wayo sannan ta koma kawai dan kun nuna masa bata da gata in ba haka ba a ina ka taba ganin ana wannan abun da yakeyi?
Shikenan daga ta masa abu seya korota gida se sanda ya mula yace ta koma who does that?
Dan ubansa haka ake aure? Ko kuwa saboda an tsani yarinya ba'a bin ba'asi duk sanda suka samu matsala sedai a dora mata laifi ai qarfe daya baya Amo shi kadai amma kun rigada kun nuna masa bata da wani gata yayi yanda yaga dama da ita ai dole yanzu gashi nan anzo gabar da ya fara dukanta yana shaqeta, tunda yasan ko kasheta yayi qarshe ita za'a dorawa laifi ace ita ta nemi halakashi in the process of self defence ya kasheta ko to wallahi bazata sabu ba, ni ina son abata in ku duk bakwaso zan kuma kwato mata haqqinta daga nan police station zanje in aka bi mata kadin Shaqeta da yayi sannan yazo muji matsayar auran na gaji ya sallameta kawai ai ba rasa masu auranta zatayi ba yarinya da kyanta da komai bazata zauna baqin cikin Miji ya kasheta ba bayan ta gama shan naku.