Sashe 67
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mama ce kan gaba suka shiga gidan, Abu na zaune gaban murhu daya turnuqr da uban hayaqi tana fifitawa saboda jiqewar da itacen yayi sakamakon ruwan saman da akayi a safiyar ga wani rafkeken madambaci akai da alama dambu takeyi se yara biyu maza da Mace daya suna wasa da ruwan da aka tara a babban baho daga gefenta. Daya daga cikinsu ya jefa dan uwansa a ciki ruwan yayi fallatsi har inda Abun take
"Wane dan abu ta kazan uban ne ya watso mun ruwa, wai ku wadanne irin shaidanun yara mara sa jin magane ma dan ubanku ba tun dazu nace ku bar wasan ruwan nan ba shegu masu kunne qashi wallahi duk wanda sanyi ya kama sedai ya mutu amma kwandalata bazan kashe gurin siyan magani ba" Abu ta fada cikin masifa yaran duk sukayi tsuru suna kallonta.
Labulen daki aka daga wani dogo baqin mutum ya leqo yana cewa
"Wai Zainab sau nawa zan miki magana akan tsinewa yaran nan ke ace baki da aiki s zaginsu dayi musu mugun baki se kace bake kika haife su ba"
"To ina ruwanka kasan me sukayi mun ne kana cikin daki saboda mutuwar zuciya ni ina nan ina fafutukar yanda zanyi na rufawa kaina asiri s an zage su ne zaka fito kace zakayi magana aikin banza zaku wuce daga nan ku bani guri ko se na tarar daku" ta qarasa atsawace tana zare musu ido. Gaba dayan su suka zabura, cikin tsautsayi daya daga ciki ta ture robar da Abu ta zuba zogale ya zube cikin jar qasar data sha ruwa a tsakar gidan.
"Na shiga uku yanzu dan ubanki kika zubarmun shegiya me kama da yayan Allah bani toh wallahi kiyi maza kije duk inda zaki ki samo mun wani idan ba haka ba yau na riqeki se na miki dukan mutuwa" Abu ta fada tana miqewa ko kafin ta qarasa yarinyar ta arta da gudu tayi waje, bata haqura ba ta bita nan idonta ya sauka kan Mama da Umaimah da sukayi mutuwar tsaye tun shigowarsu ganin wannan balahira ta Abu.
Dafe qirji tayi se kuma me ta tuna cikin iya bariki ta shiga washe baki tana cewa
"Hajiya sannunku da zuwa, kuyi haquri banji shigowarku ba"
Wani kallon banza Mama tayi mata, Umaimah kuwa kallonta kawai takeyi a ranta tana tuna irin qarairayinda Maman Nihal ta ringayi mata.
"Hajiya ku qaraso mana" muryar Abu ta dawo da ita daga tunanin data tafi se Mama tayi saurin tareta da cewa
"Me qaraso ina malama karki bata mana lokaci ki shiga ki dakko mana abinda ya kawo mu ba surutu muka zo yi ba"
"Yi haquri Hajiya kinga yau ruwa ya saka dambun be sauka da wuri ba" Abu ta fada Mama tayi saurin tareta da cewa
"Ke ki fita a ido na, idan baki sanni ba ita ma wannan zaki ce zakice baki santa ba ko kuwa wani wasan kwaikwayon zaki sake yi mana a nan? To tun wuri ki shiga hankalinki idan ba do kike na tara miki gajiya ba a nan barauniyar banza kawai".
"Haba Hajiya ya daga magana zaki nemi kici mun mutunci har cikin gidana meye hadina dake a ina na san ku da zaki zo kina kirana da barauniya yanzu idan na kai zancen nan gurin hukuma ai s an bimun haqqina" Abu ta fada taba bata fuska tana rufe baki kuwa Mama ta kwashe ta da mari tana cewa
"Idan baki kai mu gurin hukuma ba baki qaunar Allah, ke kuma da kika tsaya a nan zaki matso ne ko kuwa sena ci ubanki kema, a shegen kwashe kwashenki ai yau ga abinda kika dauko barauniya har cikin gida"
"Wallahi bazan yarda ba se an bi mun kadin marina da kirana da barauniya da kikeyi haka kawai ban san ku ba kuzo daga sama daga abin Arziqi ki hau dukana, Salisu bazaka fito ba kana kallo anzo har gida ana cimun mutunchi" Abu ta fada tana kururuwa se Umaimah ta kalleta tace
"Amma Maman Nihal kinji kunya wallahi ban taba zatonki da qarya ba ashe daman kin shiga jikinane saboda ki damfareni da a zatonki kinci banza kenan kin gudar mun da sarqa sedai kinyi batan basira da kika kaini inda aka sanki, yanzun ma can mukaje kuma Matar da kike qarya da sunanta ta saka aka rako mu har nan".
Tsilli tsilli tayi da ido jin magnganun Umaimah amma saboda iya bariki seta kwasa tayi dakinta tana kwalawa Mijinta me suna Salisu kira tace
"Salisu ka fito kana ina kana ji matan nan sunzo zasu daura mun sharrin sata wallahi bazan yarda ba ka fito ka kirawo mun yan sanda a bimun kadin sharrin da suka mun"
"Idan ke baki kira yan sanda ba ni yanzu zan kira su tunda bazaki fito da ita ta laluma ba" Mama ta fada tana danna wayarta, Aminu ta kira a taqaice tace ya turo mata yan sanda ya kira Salman ze bashi Address din gidan da take, yana tambayarta meya faru ta kashe tana jaddada masa ya turo su ba'a wuci minti sha biyar ba kuwa sega jiniyar yan sanda ta karade unguwar Abu ta dafe qirji amma qi fadi ya hanata cewa komai se Mijinta ne ya fito yana tambayar Maman ya akayi tace idan sunje can yaji komai.
Matan yan sanda biyu ne suka shiga gidan da sallam Mama ta nuna musu Abu dake shirin fadawa daki data gansu tace gata nan suka cafketa kuwa suka tasata a gaba haka suka sakata a mota su Mama suka bisu a baya tareda mijin Abun. A station Sanda Yaya Aminu ya isa station din aka shigar dasu office din DPO fafur taqi yarda da tuhumar da ake mata ta kafe akan ita bata sansu ba sharri suke mata.
Umaimah ta bada wayarta duk wani hirar su da Maman Nihal din tana ciki ga hotunanta nan da voice messages muryarta ce amma dukda haka ta musanta ita ba ita bace, ran DPO ya baci ya saka mata nan su jefata a Cell, su tuhumeta seta fadi gaskiya haka kuwa suka sameta suka ringa jibgarta musamman suna jin haushin zaginsu data ringayi a hanyar tahowa, seda taga suna neman hallakata da duka kafin tace zata fadi gaskiya aka fito da ita fuskarta tasha maruka ta kumbura suka koma Office din DPO, Mama ta maka mata harara Umaimah dai na gefe kanta a qasa dan itama ba tsira tayi a gurin Maman ba masifa take mata tana zaginta.
Khalil daya je gida da safen aka ce sun fita ne ya qaraso dan ya kirata ta gaya masa inda suke bayan ya zo Yaya Aminu ya fita ya shigo dashi office din. Abu na sheshsheqar kuka ta zayyana musu yanda suka hadu da Umaimah da duk abinda ya faru tsakaninsu, ta qarasa da cewa
"Kiyi haquri wallahi sharrin shaidan ne, kuma ni banyi niyyar guduwar miki da abu ba tsautsayine ya fada akai na rasa ta yanda zan gaya miki shiyasa amma wallahi ba gudu nayi ba"
Tsaki Mama tayi tace
"Can ke kika san tsautsayi ni sarqa kawai na sani ki fadi inda take salin alin kowa ya kama gabansa".
Rantse rantse ta ringayi akan ita ba satar sarqar tayi ba, takamaimai kuma taqi fadan inda take da DPO ya gaji yace ze cike mata FIR a tura su kotu can Alqali ya san yanda zeyi dasu nan idonta ya sake raina fata jin zancen kotu, ta riqe qafar Umaimah tana roqonta Mama ta hadasu su dukata qunduma musu zagi tace
"Babu kotun da zamuje anan zata fito da ita dan ko munjr qarshe gidan yari za'a turata sarqa kuwa seta Allah yanzun ma bata daku bane idan kuka lallasata zata fadi inda ta kaita ko ni ku bani kulkin na daka yar banza".
Murmushi DPO yayi yace
"Ayi haquri Hajiya, Officer kuje ku cike mata takaddar kawai ku turasu kotun zefi sauqi" kuka Abu ta fasa ganin dagaske fa kotu za'a kaita tasan kuma daga nan se gidan yari, Salisu Mijinta ne ya kalleta yace
"Yanzu Abu bazaki fadi inda kika kai musu abinsu ba kinfi so a kaiki kotun da kudin su zakiji koda na tara ga zaman gidan yari? Ina jiya naji kina zancen da kudinki a hannun Alhaji Auwalu yana juya miki ga daukar Adashin da aka kawo miki dazu da safe idan kin hada ko basu isa ba ai zaki rage wani abun".
Wata uwar harara ta galla masa kamar idonta ze fado tace
"Salisu kaji tsoron Allah daman ashe labe kake mun a gidan uwar wa kaji nace inada kudi ana juyamun saboda kawai ka sakani a wata masifar ko bayan wadda nake ciki"
"Shikenan kiyi yanda kike so amma nidai babu ruwana daga nan gida zanyi su kaiki ko ina ne sedai ki rube a can amma babu wanda zan gayawa ballantana a fito dake tunda haka kika zaba" ya fada yana miqewa tsaye, se kuma tayi qasa da kai, muryarta na rawar kuka tace
"Ranka ya dade a bani wayata toh na danyi kiraye kiraye ko zan samu na hado kudin"
"Ranka ya dade wannan matar bata da mutunchi wallahi kana ji mijinta ya fada tana da kudi tunda babu sarqa seta bada kudinta dan wallahi seta biya kudin nan" Mama ta fada se DPO ya kalli Matan yan sanda yace su maida ita, suyi ta dukanta har seta magantu kar su saurara mata Abu na ganin sunyo kanta ta fasa kuka tana roqon su tsaya, daya daga ciki ta kai mata mangari, ta dafe haqarqarinta jij Azabar zafi na ratsata suka fara janta tace a tsaya zata fadi inda kudin suke.
"Wane dan abu ta kazan uban ne ya watso mun ruwa, wai ku wadanne irin shaidanun yara mara sa jin magane ma dan ubanku ba tun dazu nace ku bar wasan ruwan nan ba shegu masu kunne qashi wallahi duk wanda sanyi ya kama sedai ya mutu amma kwandalata bazan kashe gurin siyan magani ba" Abu ta fada cikin masifa yaran duk sukayi tsuru suna kallonta.
Labulen daki aka daga wani dogo baqin mutum ya leqo yana cewa
"Wai Zainab sau nawa zan miki magana akan tsinewa yaran nan ke ace baki da aiki s zaginsu dayi musu mugun baki se kace bake kika haife su ba"
"To ina ruwanka kasan me sukayi mun ne kana cikin daki saboda mutuwar zuciya ni ina nan ina fafutukar yanda zanyi na rufawa kaina asiri s an zage su ne zaka fito kace zakayi magana aikin banza zaku wuce daga nan ku bani guri ko se na tarar daku" ta qarasa atsawace tana zare musu ido. Gaba dayan su suka zabura, cikin tsautsayi daya daga ciki ta ture robar da Abu ta zuba zogale ya zube cikin jar qasar data sha ruwa a tsakar gidan.
"Na shiga uku yanzu dan ubanki kika zubarmun shegiya me kama da yayan Allah bani toh wallahi kiyi maza kije duk inda zaki ki samo mun wani idan ba haka ba yau na riqeki se na miki dukan mutuwa" Abu ta fada tana miqewa ko kafin ta qarasa yarinyar ta arta da gudu tayi waje, bata haqura ba ta bita nan idonta ya sauka kan Mama da Umaimah da sukayi mutuwar tsaye tun shigowarsu ganin wannan balahira ta Abu.
Dafe qirji tayi se kuma me ta tuna cikin iya bariki ta shiga washe baki tana cewa
"Hajiya sannunku da zuwa, kuyi haquri banji shigowarku ba"
Wani kallon banza Mama tayi mata, Umaimah kuwa kallonta kawai takeyi a ranta tana tuna irin qarairayinda Maman Nihal ta ringayi mata.
"Hajiya ku qaraso mana" muryar Abu ta dawo da ita daga tunanin data tafi se Mama tayi saurin tareta da cewa
"Me qaraso ina malama karki bata mana lokaci ki shiga ki dakko mana abinda ya kawo mu ba surutu muka zo yi ba"
"Yi haquri Hajiya kinga yau ruwa ya saka dambun be sauka da wuri ba" Abu ta fada Mama tayi saurin tareta da cewa
"Ke ki fita a ido na, idan baki sanni ba ita ma wannan zaki ce zakice baki santa ba ko kuwa wani wasan kwaikwayon zaki sake yi mana a nan? To tun wuri ki shiga hankalinki idan ba do kike na tara miki gajiya ba a nan barauniyar banza kawai".
"Haba Hajiya ya daga magana zaki nemi kici mun mutunci har cikin gidana meye hadina dake a ina na san ku da zaki zo kina kirana da barauniya yanzu idan na kai zancen nan gurin hukuma ai s an bimun haqqina" Abu ta fada taba bata fuska tana rufe baki kuwa Mama ta kwashe ta da mari tana cewa
"Idan baki kai mu gurin hukuma ba baki qaunar Allah, ke kuma da kika tsaya a nan zaki matso ne ko kuwa sena ci ubanki kema, a shegen kwashe kwashenki ai yau ga abinda kika dauko barauniya har cikin gida"
"Wallahi bazan yarda ba se an bi mun kadin marina da kirana da barauniya da kikeyi haka kawai ban san ku ba kuzo daga sama daga abin Arziqi ki hau dukana, Salisu bazaka fito ba kana kallo anzo har gida ana cimun mutunchi" Abu ta fada tana kururuwa se Umaimah ta kalleta tace
"Amma Maman Nihal kinji kunya wallahi ban taba zatonki da qarya ba ashe daman kin shiga jikinane saboda ki damfareni da a zatonki kinci banza kenan kin gudar mun da sarqa sedai kinyi batan basira da kika kaini inda aka sanki, yanzun ma can mukaje kuma Matar da kike qarya da sunanta ta saka aka rako mu har nan".
Tsilli tsilli tayi da ido jin magnganun Umaimah amma saboda iya bariki seta kwasa tayi dakinta tana kwalawa Mijinta me suna Salisu kira tace
"Salisu ka fito kana ina kana ji matan nan sunzo zasu daura mun sharrin sata wallahi bazan yarda ba ka fito ka kirawo mun yan sanda a bimun kadin sharrin da suka mun"
"Idan ke baki kira yan sanda ba ni yanzu zan kira su tunda bazaki fito da ita ta laluma ba" Mama ta fada tana danna wayarta, Aminu ta kira a taqaice tace ya turo mata yan sanda ya kira Salman ze bashi Address din gidan da take, yana tambayarta meya faru ta kashe tana jaddada masa ya turo su ba'a wuci minti sha biyar ba kuwa sega jiniyar yan sanda ta karade unguwar Abu ta dafe qirji amma qi fadi ya hanata cewa komai se Mijinta ne ya fito yana tambayar Maman ya akayi tace idan sunje can yaji komai.
Matan yan sanda biyu ne suka shiga gidan da sallam Mama ta nuna musu Abu dake shirin fadawa daki data gansu tace gata nan suka cafketa kuwa suka tasata a gaba haka suka sakata a mota su Mama suka bisu a baya tareda mijin Abun. A station Sanda Yaya Aminu ya isa station din aka shigar dasu office din DPO fafur taqi yarda da tuhumar da ake mata ta kafe akan ita bata sansu ba sharri suke mata.
Umaimah ta bada wayarta duk wani hirar su da Maman Nihal din tana ciki ga hotunanta nan da voice messages muryarta ce amma dukda haka ta musanta ita ba ita bace, ran DPO ya baci ya saka mata nan su jefata a Cell, su tuhumeta seta fadi gaskiya haka kuwa suka sameta suka ringa jibgarta musamman suna jin haushin zaginsu data ringayi a hanyar tahowa, seda taga suna neman hallakata da duka kafin tace zata fadi gaskiya aka fito da ita fuskarta tasha maruka ta kumbura suka koma Office din DPO, Mama ta maka mata harara Umaimah dai na gefe kanta a qasa dan itama ba tsira tayi a gurin Maman ba masifa take mata tana zaginta.
Khalil daya je gida da safen aka ce sun fita ne ya qaraso dan ya kirata ta gaya masa inda suke bayan ya zo Yaya Aminu ya fita ya shigo dashi office din. Abu na sheshsheqar kuka ta zayyana musu yanda suka hadu da Umaimah da duk abinda ya faru tsakaninsu, ta qarasa da cewa
"Kiyi haquri wallahi sharrin shaidan ne, kuma ni banyi niyyar guduwar miki da abu ba tsautsayine ya fada akai na rasa ta yanda zan gaya miki shiyasa amma wallahi ba gudu nayi ba"
Tsaki Mama tayi tace
"Can ke kika san tsautsayi ni sarqa kawai na sani ki fadi inda take salin alin kowa ya kama gabansa".
Rantse rantse ta ringayi akan ita ba satar sarqar tayi ba, takamaimai kuma taqi fadan inda take da DPO ya gaji yace ze cike mata FIR a tura su kotu can Alqali ya san yanda zeyi dasu nan idonta ya sake raina fata jin zancen kotu, ta riqe qafar Umaimah tana roqonta Mama ta hadasu su dukata qunduma musu zagi tace
"Babu kotun da zamuje anan zata fito da ita dan ko munjr qarshe gidan yari za'a turata sarqa kuwa seta Allah yanzun ma bata daku bane idan kuka lallasata zata fadi inda ta kaita ko ni ku bani kulkin na daka yar banza".
Murmushi DPO yayi yace
"Ayi haquri Hajiya, Officer kuje ku cike mata takaddar kawai ku turasu kotun zefi sauqi" kuka Abu ta fasa ganin dagaske fa kotu za'a kaita tasan kuma daga nan se gidan yari, Salisu Mijinta ne ya kalleta yace
"Yanzu Abu bazaki fadi inda kika kai musu abinsu ba kinfi so a kaiki kotun da kudin su zakiji koda na tara ga zaman gidan yari? Ina jiya naji kina zancen da kudinki a hannun Alhaji Auwalu yana juya miki ga daukar Adashin da aka kawo miki dazu da safe idan kin hada ko basu isa ba ai zaki rage wani abun".
Wata uwar harara ta galla masa kamar idonta ze fado tace
"Salisu kaji tsoron Allah daman ashe labe kake mun a gidan uwar wa kaji nace inada kudi ana juyamun saboda kawai ka sakani a wata masifar ko bayan wadda nake ciki"
"Shikenan kiyi yanda kike so amma nidai babu ruwana daga nan gida zanyi su kaiki ko ina ne sedai ki rube a can amma babu wanda zan gayawa ballantana a fito dake tunda haka kika zaba" ya fada yana miqewa tsaye, se kuma tayi qasa da kai, muryarta na rawar kuka tace
"Ranka ya dade a bani wayata toh na danyi kiraye kiraye ko zan samu na hado kudin"
"Ranka ya dade wannan matar bata da mutunchi wallahi kana ji mijinta ya fada tana da kudi tunda babu sarqa seta bada kudinta dan wallahi seta biya kudin nan" Mama ta fada se DPO ya kalli Matan yan sanda yace su maida ita, suyi ta dukanta har seta magantu kar su saurara mata Abu na ganin sunyo kanta ta fasa kuka tana roqon su tsaya, daya daga ciki ta kai mata mangari, ta dafe haqarqarinta jij Azabar zafi na ratsata suka fara janta tace a tsaya zata fadi inda kudin suke.