Sashe 33
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
SHIRYE NAKE ZANYI MAKU PROMO SABODA WA ANDA BASU SHA BA SU ZO SU DA DANA MAGANIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID DUK LABARIN DA AKE BAKU GASKENA MAGANINA KANKAT NE KOBAKISHA KOMAI BA YA ISHEKI
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 16
Khalil
Bayan daya bar qofar gidan rasa inda ze nufa yayi haka yayita yawo a titi dan baya so ya koma gida a yanayin da yake ciki, tambaya ce ze shata a gurin Hajiya ga gidan kuma ya fara cika da yan uwa da sukazo se kace wani bikin mace a fadar sa zasu taho tun ana sauran kwana uku bayan babu abinda za'ayi.
Mansur ne ya fado masa a rai, da safe sunyi waya ya gaya masa yana off se da dare ze shiga Asibiti dan haka ya karkata kan motar ya nufi gidan su Mansur.
A tsakar gida ya tarar da Mamansu tana aikace aikave suka gaisa a mutunce dan tamkar Hajiyar sa haka ya dauketa saboda Amincinsu da Mansur tun Primary gashi yanzu sun wuce Aminai ma sedai a kirasu yan uwa.
"Ango Ango, ya shirye shirye? Bamu dade dayin waya da Hajiyan ba ai nake tambayarta ko akwai abinda za'ayi tace Aa se gobe ne za'a rage girkin daurin aure, gashi dai abin Allah nan Dan uwanka kullum yake tasaka gaba a gidan nan ashe ma seka rigashi yin auran Allah dai ya sanya Alkhairi yasa mutuwa ce zata raba" Hajiyar su Mansur ta fada, Khalil dake ta faman sunkuyar da kai dan karta ga idon sa da yayi ja ya amsa qasaqasa kafin ya wuce can inda dakin Mansur yake.
Buga qofar ya shigayi Mansur dake bacci ya farka yana tambayar waye
"Malam zoka bude mun qofa" Ya fada muryarsa a cunkushe, Mansur din na jin shine ya taso ya bude yana cewa
"Me kuma ya kawo ka? Dan Allah ku barni na huta. Kana kallo kwana biyu na jera straight ina call morning to Evening saboda na samu off muyi hidimar biki shine yanzu zaka biyo ni ka hanani bacci me zan maka" Mansur ya shiga Mita shidai Khalil be kula shi ba kai tsaye toilet ya nufa ya kunna famfo ya ringa zuba ruwa akansa seda yaji ya samu nutsuwa kafin ya dauro Alwala ya fito lokacin Mansur harya koma baccinsa.
Kan kujerar dake dakin ya samu ya zauna yai shiru lokaci lokaci ya buga tsaki, ji yake yi zuciyar sa na zugashi akan ya fasa auran nan. Wannan yarinyar babu alamar samun zaman lafiya da nutsuwa a tattare da ita gara tun yana da sauaran dama ya raba kansa da alaqaqai ya huta saboda idab ya rigada ya aureta Saki is the last thing da ze iya aikatawa.
Bashi da burin ya auri mace ya saki kai duk girman laifin da zata masa sedai ya nemi wata hanyar ya hukuntata amma banda saki saboda shi ya saka a ransa idan yayi aure to se dai idan shi ya mutu ko matar ta mutu amma babu rabuwa shi yasa ya dade yana laluben wadda halinsu ze zo daya su zauna suyi haquri da junansu amma qarshe ga inda ya qare.
Tsaki me qarfi ya qaraja Mansur ya miqe zaune tareda jifansa da Pillown daya tashi saga kai yace
"Dallah Malam tashi ka fita, kaje palour Mama ka zauna kazo se uban tsaki kake wa mutane ka duk ka cika mun kunne na kasa bacci".
Shiru Khalil yayi masa ya gyara zaman sa akan kujerar ya harde qafa yana girgizasu, se Mansur ya dawo gefen gadon yana kallonsa yace
"Talk to me Man me yake damunka why are you upset?"
"Mansur waccen yarinyar ce gaba daya so nake nima nayi going crazy kamarta. Shikenan abinta ya zama kamar wani season film ko da yaushe i should be anticipating new episode kullum da kalar sabon haukan da zatayimun display" Khalil ya fada cikin bacin rai.
Dafa kafadar sa Mansur yayi yana bubbugawa ba tareda yayi magana ba se Khalil din yaci gaba da cewa
"Daga na kirata tana Salon lafiya lau muka gama magana the next thing naje daukan su kawai ta hau kaina da bala'i sannan saboda bata da hankali zata cakumi wata yarinya da dambe a gaban mutane kawai dan yarinyar ta kalle ni"
"Dambe?" Mansur ya fada yana bude ido dariya nason kufce masa ya danne se Khalil ya maka masa harara yace
"Na zama laughing stuff kenan, ina gaya maka matsala kana neman kayi mun dariya ko bayan duk kai ka qara jefani a halin da nake ciki, sanda na nemi shawarar ka daka qarfafamun guiwa ai da yanzu ba wannan maganar akeyi ba".
"Yanzun ma Khalil lokaci be qure ba you can call the wedding off na tabbata kuma babu me ganin laifinka tunda kowa yasan halinta. Bari na saka rigata ma ba se nayi wanka ba kawai ka tashi kawai muje mu gaya musu ka fasa, su riqe komai mun bar musu ma Allah ze bamu kudin da zamu hada wasu dan gaskiya nima na fara tsorata da halinta, dambe fa? Ni rabonda naga Mata na dambe tun zamanin muna zuwa Ma'ahad Islamiyya" Mansur ya qarasa yana yar dariya ganin yanda Khalil ya zaro masa idanu se kace bashi ne ya tayar da maganar ya fasa din ba.
"You must be mad Mansur, jibi fa ne daurin auranmukake cewa na fasa so kake na bata mata suna ko yaya? Sannan duk wadannan mutanen daka je kayo gayyar daurin aure me zaka koma ka gaya musu?"
"To Khalil me kake so ayi, kasan ni me sonka da Alkhairi ne. Bazan so ka auri matar da zata ringa saka ka a damuwa ba kullum shiyasa kuma da tun wancan lokacin kayi mun bayani sosai qila dana fahimceka nayi supporting abinda kazo dashi amma yanzun ma lokaci be qure ba, zamu iya fasawa kawai kowa ya huta" Mansur dinya sake fada kamar gaske, se Khalil ya juya kai yayi shiru kamar baze ce komai ba can kuma ya juya ya kalle shi yace
"I love her Mansur, i just hate thia bad side of her. Da zata zauna a yanda na fara ganinta har na fada sonta we would be the happiest couples because we are madw for each other"
"Toh Romeo ai shikenan kana sonta tana sonka the soyayya will hold the bond karka damu she will change for better data shiga gidanka" Mansur ya fada kafin ya komawarsa kan gadon ya kwanta daidai nan aka buga qofar dakin Mansur din ya bada damar shigowa wata yar farar yarinya ta shiga da sallama ta gaishe su kafin ta ajiye Try din da aka doro kayan abinci akai tana cewa
"Gashi Mama tace a kawowa Yaya Khalil"
"Lallai Mama wato Khalil ta aikowa abinci bayan ni ina zaune nan ko abincin safe baa kawo mun ba" Mansur ya fada yana jan kwanukan gabansa, se yarinyar tayi yar dariya tace
"Lah Yaya ai bamu san kana nan bane ni ta tambaya ma nace baka dawo ba shi yasa amma bari na koma na qaro muku toh idan wannan baze isa ba" ta juya zata fita Khalil ya dakatar da ita dacewa
"Barshi duk cinsa wannanya ishe mu danni bada yawa zanci ba"
"Toh Yaya" ta fada kafin ta juya ta fita.
"A ina Mama ta samo yarinya" Khalil ya fada yana gutsirar Funkason da aka kawo musu.
"Yar gidan Kawu Sani ce na Jama'are, kasan Mamansu ta sake aure yayarta Muhsina ma anyi mata aure se ita kadai tana hannun Inna Sadiya to ruqon Tsofaffin nan babu wani da ze ringa sakawa yaro ido ba dadi shiyasa Mama ta dakkota tunda nan din ita kadai ce yanzu ta samu yar tayin zama" Mansur ya fada yana cin abincinsa. Se Khalil ya gyada kai yace
"Oh rayuwar fa kenan duk ka gama haqilonka ma akan macen ka mutu watanni kadan ta auri wani su cinye abinda ka tara tare, jifa gaba daya Kawu banjin ya shekara biyu da rasuwa duk Kururuwar nan data ringayi ranar jana'iza wai har ta sake wani auran".
"Hmmm ka bari kawai Abokina abin takaicin ma a cikin gidan fa take zaune anyi magana wai ai rabonta ana yayanta ne kuma ze ringa biyan haya shine saboda dan Akuya ne wai baze riqe mata Yarinyar nan guda daya ba ita kuma inaga Asirce ta yayi ko yaya ta tattarata ta mayarwa da Inna Sadiyan, toh muna dai zuba ido kowa dai yasan abinda yasa ya aureta kudin kuma na qarewa gayyar zata watse, yanzu ma shirin shiga Kotu suje da Kawu Labaran akan ta dawo da komai na yaran tunda tayi aure"
"Allah ya rufa Asiri" Khalil ya fada yana rufe baki wayarsa ta fara qara ganin besan number ba yasa ya shareta suka ci gaba da cin abincin suna yan hirarrakinsu.
Ganin ana ta kira anqi haqura ya saka Mansur cewa
"Ka daga mana ka sani ko cikin mutanen mu ne wani yake kira"
"Kyale su kawai ko waye ya yi text in na gane na kira ko kai ka daga kaji waye".
Jan wayar Mansur yayi yana dannawa kuwa sega Text ya shigo ya bude ya karanta yace wa Khalil
"Ka gani ba Aminiyar Amaryace, se taje ta gaya mata ka mata wulaqanci ka qara wani laifin tukunna"
Tsaki Khalil yayi yace
"Seka kira kaji me suke so, in kudi ne wallahi sisi bazan bayar ba dan na bata komai dama muna yar dadi ne sena qara mata amma yanzu kuwa tayiwa kanta"
"Allah ya taimaki Angon Umaimah" Mansur ya fada cikin shaqiyanci kafin ya danna kiran layin.
Kukan da Umaimah ta fasa tana daga wayar ya saka shi kallon Khalil kafin ya janye wayar daga kunnensa ua sakata a speaker ya ajiye a gaban Khalil.
Kuka take bilhaqqi harda sheshsheqa, Khalil ya daya tsame hannu daga cikin abincin ya dafe kansa saboda yanda yake jin sautin kukan nata, tabashi Mansur yayi yana masa alamar ya daga, ya cije baki kamar baya so ya dauki wayar ya cire ta daga speaker ya saka a kunne
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 16
Khalil
Bayan daya bar qofar gidan rasa inda ze nufa yayi haka yayita yawo a titi dan baya so ya koma gida a yanayin da yake ciki, tambaya ce ze shata a gurin Hajiya ga gidan kuma ya fara cika da yan uwa da sukazo se kace wani bikin mace a fadar sa zasu taho tun ana sauran kwana uku bayan babu abinda za'ayi.
Mansur ne ya fado masa a rai, da safe sunyi waya ya gaya masa yana off se da dare ze shiga Asibiti dan haka ya karkata kan motar ya nufi gidan su Mansur.
A tsakar gida ya tarar da Mamansu tana aikace aikave suka gaisa a mutunce dan tamkar Hajiyar sa haka ya dauketa saboda Amincinsu da Mansur tun Primary gashi yanzu sun wuce Aminai ma sedai a kirasu yan uwa.
"Ango Ango, ya shirye shirye? Bamu dade dayin waya da Hajiyan ba ai nake tambayarta ko akwai abinda za'ayi tace Aa se gobe ne za'a rage girkin daurin aure, gashi dai abin Allah nan Dan uwanka kullum yake tasaka gaba a gidan nan ashe ma seka rigashi yin auran Allah dai ya sanya Alkhairi yasa mutuwa ce zata raba" Hajiyar su Mansur ta fada, Khalil dake ta faman sunkuyar da kai dan karta ga idon sa da yayi ja ya amsa qasaqasa kafin ya wuce can inda dakin Mansur yake.
Buga qofar ya shigayi Mansur dake bacci ya farka yana tambayar waye
"Malam zoka bude mun qofa" Ya fada muryarsa a cunkushe, Mansur din na jin shine ya taso ya bude yana cewa
"Me kuma ya kawo ka? Dan Allah ku barni na huta. Kana kallo kwana biyu na jera straight ina call morning to Evening saboda na samu off muyi hidimar biki shine yanzu zaka biyo ni ka hanani bacci me zan maka" Mansur ya shiga Mita shidai Khalil be kula shi ba kai tsaye toilet ya nufa ya kunna famfo ya ringa zuba ruwa akansa seda yaji ya samu nutsuwa kafin ya dauro Alwala ya fito lokacin Mansur harya koma baccinsa.
Kan kujerar dake dakin ya samu ya zauna yai shiru lokaci lokaci ya buga tsaki, ji yake yi zuciyar sa na zugashi akan ya fasa auran nan. Wannan yarinyar babu alamar samun zaman lafiya da nutsuwa a tattare da ita gara tun yana da sauaran dama ya raba kansa da alaqaqai ya huta saboda idab ya rigada ya aureta Saki is the last thing da ze iya aikatawa.
Bashi da burin ya auri mace ya saki kai duk girman laifin da zata masa sedai ya nemi wata hanyar ya hukuntata amma banda saki saboda shi ya saka a ransa idan yayi aure to se dai idan shi ya mutu ko matar ta mutu amma babu rabuwa shi yasa ya dade yana laluben wadda halinsu ze zo daya su zauna suyi haquri da junansu amma qarshe ga inda ya qare.
Tsaki me qarfi ya qaraja Mansur ya miqe zaune tareda jifansa da Pillown daya tashi saga kai yace
"Dallah Malam tashi ka fita, kaje palour Mama ka zauna kazo se uban tsaki kake wa mutane ka duk ka cika mun kunne na kasa bacci".
Shiru Khalil yayi masa ya gyara zaman sa akan kujerar ya harde qafa yana girgizasu, se Mansur ya dawo gefen gadon yana kallonsa yace
"Talk to me Man me yake damunka why are you upset?"
"Mansur waccen yarinyar ce gaba daya so nake nima nayi going crazy kamarta. Shikenan abinta ya zama kamar wani season film ko da yaushe i should be anticipating new episode kullum da kalar sabon haukan da zatayimun display" Khalil ya fada cikin bacin rai.
Dafa kafadar sa Mansur yayi yana bubbugawa ba tareda yayi magana ba se Khalil din yaci gaba da cewa
"Daga na kirata tana Salon lafiya lau muka gama magana the next thing naje daukan su kawai ta hau kaina da bala'i sannan saboda bata da hankali zata cakumi wata yarinya da dambe a gaban mutane kawai dan yarinyar ta kalle ni"
"Dambe?" Mansur ya fada yana bude ido dariya nason kufce masa ya danne se Khalil ya maka masa harara yace
"Na zama laughing stuff kenan, ina gaya maka matsala kana neman kayi mun dariya ko bayan duk kai ka qara jefani a halin da nake ciki, sanda na nemi shawarar ka daka qarfafamun guiwa ai da yanzu ba wannan maganar akeyi ba".
"Yanzun ma Khalil lokaci be qure ba you can call the wedding off na tabbata kuma babu me ganin laifinka tunda kowa yasan halinta. Bari na saka rigata ma ba se nayi wanka ba kawai ka tashi kawai muje mu gaya musu ka fasa, su riqe komai mun bar musu ma Allah ze bamu kudin da zamu hada wasu dan gaskiya nima na fara tsorata da halinta, dambe fa? Ni rabonda naga Mata na dambe tun zamanin muna zuwa Ma'ahad Islamiyya" Mansur ya qarasa yana yar dariya ganin yanda Khalil ya zaro masa idanu se kace bashi ne ya tayar da maganar ya fasa din ba.
"You must be mad Mansur, jibi fa ne daurin auranmukake cewa na fasa so kake na bata mata suna ko yaya? Sannan duk wadannan mutanen daka je kayo gayyar daurin aure me zaka koma ka gaya musu?"
"To Khalil me kake so ayi, kasan ni me sonka da Alkhairi ne. Bazan so ka auri matar da zata ringa saka ka a damuwa ba kullum shiyasa kuma da tun wancan lokacin kayi mun bayani sosai qila dana fahimceka nayi supporting abinda kazo dashi amma yanzun ma lokaci be qure ba, zamu iya fasawa kawai kowa ya huta" Mansur dinya sake fada kamar gaske, se Khalil ya juya kai yayi shiru kamar baze ce komai ba can kuma ya juya ya kalle shi yace
"I love her Mansur, i just hate thia bad side of her. Da zata zauna a yanda na fara ganinta har na fada sonta we would be the happiest couples because we are madw for each other"
"Toh Romeo ai shikenan kana sonta tana sonka the soyayya will hold the bond karka damu she will change for better data shiga gidanka" Mansur ya fada kafin ya komawarsa kan gadon ya kwanta daidai nan aka buga qofar dakin Mansur din ya bada damar shigowa wata yar farar yarinya ta shiga da sallama ta gaishe su kafin ta ajiye Try din da aka doro kayan abinci akai tana cewa
"Gashi Mama tace a kawowa Yaya Khalil"
"Lallai Mama wato Khalil ta aikowa abinci bayan ni ina zaune nan ko abincin safe baa kawo mun ba" Mansur ya fada yana jan kwanukan gabansa, se yarinyar tayi yar dariya tace
"Lah Yaya ai bamu san kana nan bane ni ta tambaya ma nace baka dawo ba shi yasa amma bari na koma na qaro muku toh idan wannan baze isa ba" ta juya zata fita Khalil ya dakatar da ita dacewa
"Barshi duk cinsa wannanya ishe mu danni bada yawa zanci ba"
"Toh Yaya" ta fada kafin ta juya ta fita.
"A ina Mama ta samo yarinya" Khalil ya fada yana gutsirar Funkason da aka kawo musu.
"Yar gidan Kawu Sani ce na Jama'are, kasan Mamansu ta sake aure yayarta Muhsina ma anyi mata aure se ita kadai tana hannun Inna Sadiya to ruqon Tsofaffin nan babu wani da ze ringa sakawa yaro ido ba dadi shiyasa Mama ta dakkota tunda nan din ita kadai ce yanzu ta samu yar tayin zama" Mansur ya fada yana cin abincinsa. Se Khalil ya gyada kai yace
"Oh rayuwar fa kenan duk ka gama haqilonka ma akan macen ka mutu watanni kadan ta auri wani su cinye abinda ka tara tare, jifa gaba daya Kawu banjin ya shekara biyu da rasuwa duk Kururuwar nan data ringayi ranar jana'iza wai har ta sake wani auran".
"Hmmm ka bari kawai Abokina abin takaicin ma a cikin gidan fa take zaune anyi magana wai ai rabonta ana yayanta ne kuma ze ringa biyan haya shine saboda dan Akuya ne wai baze riqe mata Yarinyar nan guda daya ba ita kuma inaga Asirce ta yayi ko yaya ta tattarata ta mayarwa da Inna Sadiyan, toh muna dai zuba ido kowa dai yasan abinda yasa ya aureta kudin kuma na qarewa gayyar zata watse, yanzu ma shirin shiga Kotu suje da Kawu Labaran akan ta dawo da komai na yaran tunda tayi aure"
"Allah ya rufa Asiri" Khalil ya fada yana rufe baki wayarsa ta fara qara ganin besan number ba yasa ya shareta suka ci gaba da cin abincin suna yan hirarrakinsu.
Ganin ana ta kira anqi haqura ya saka Mansur cewa
"Ka daga mana ka sani ko cikin mutanen mu ne wani yake kira"
"Kyale su kawai ko waye ya yi text in na gane na kira ko kai ka daga kaji waye".
Jan wayar Mansur yayi yana dannawa kuwa sega Text ya shigo ya bude ya karanta yace wa Khalil
"Ka gani ba Aminiyar Amaryace, se taje ta gaya mata ka mata wulaqanci ka qara wani laifin tukunna"
Tsaki Khalil yayi yace
"Seka kira kaji me suke so, in kudi ne wallahi sisi bazan bayar ba dan na bata komai dama muna yar dadi ne sena qara mata amma yanzu kuwa tayiwa kanta"
"Allah ya taimaki Angon Umaimah" Mansur ya fada cikin shaqiyanci kafin ya danna kiran layin.
Kukan da Umaimah ta fasa tana daga wayar ya saka shi kallon Khalil kafin ya janye wayar daga kunnensa ua sakata a speaker ya ajiye a gaban Khalil.
Kuka take bilhaqqi harda sheshsheqa, Khalil ya daya tsame hannu daga cikin abincin ya dafe kansa saboda yanda yake jin sautin kukan nata, tabashi Mansur yayi yana masa alamar ya daga, ya cije baki kamar baya so ya dauki wayar ya cire ta daga speaker ya saka a kunne