Sashe 267
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 2 min read
Haka rayuwa taci gaba da garawa rasuwar Abba tasa suka qara hada kansu dukda daman a hade suke amma suka qara dunqulewa ya zamana komai zasuyi se sun shawarci juna ba duk abinda ya shige mata duhu su zata nema su warware mata, har yanzun kuma Kabir be barta aiki ba seta qara qarfafa kasuwancinta na turaren wuta daga baya ma da kansa yace ta ringa kaiwa Kasuwa ana zuba mata a shagunansa se gashi kuwa sun karbu kasuwa ta qara bude mata kuna babu mugunta ze bata kudinta daidai idan an siyar ta sake hada wasu ta kai shiyasa rashin sake mata hannu da wani tsantseninsa baya damunta tunda tana samun na kanta ba kuma ta da wata hidima akanta dan tun Sabir bata sake haihuwa ba su Mu'ayyda kuwa sedai tayi musu abu kawai a matsayinta na mahifiyarsu badan suna da buqata ba, tsakaninta da Ahalin Khalil kuwa abin se sambarka. Yaran su na zuwar mata dukda basa kwana sukanzo su wuni tareda sauran qannensu wani lokacin Humaira da kanta take kai su wani lokacin Driver ita dai batada qarfin guiwar da zata iya sake taka qafarta a cikin gidansu.
Bata sakeyin qawa ba a yanzu idan ka cire Rumasa'u ita kadai ce qawarta se Hadiza. Ta samu labarin Safina wai ta tafi Libiya neman kudi bayan da itama auranta ya mutu watanni kadan bayan na Umaimahn kusan shekararta biyar acan se gata an dawo da ita babu yanda take ciwo an rasa kalarsa suka hadu da Mshaifiyarta da itama take jinya duk an rasa kan abinda yake damunsu ita dai data ji labarin tayi mata addu'ar samun sauqi a gurin ubangiji dan bata fatan ko a lahira Allah ya sake hada fuskokinsu.
QARSHE
Bata sakeyin qawa ba a yanzu idan ka cire Rumasa'u ita kadai ce qawarta se Hadiza. Ta samu labarin Safina wai ta tafi Libiya neman kudi bayan da itama auranta ya mutu watanni kadan bayan na Umaimahn kusan shekararta biyar acan se gata an dawo da ita babu yanda take ciwo an rasa kalarsa suka hadu da Mshaifiyarta da itama take jinya duk an rasa kan abinda yake damunsu ita dai data ji labarin tayi mata addu'ar samun sauqi a gurin ubangiji dan bata fatan ko a lahira Allah ya sake hada fuskokinsu.
QARSHE