Sashe 263
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Al'amarin ya dakeshi matuqa da har ya kasa jurewa seda kwanta Asibiti magashiyyan kowa ya gane halin da yake ciki. Beji neman auran ba kamar na wancan karon da daga baya yaji ance an fasa se kawai ji yayi wai ta daura aure badan a bakin Hajiya yaji ba da tabbas qaryatawa zeyi. Ya dinga rama a tsaye abinci se an masa dole zeci ya dena fita aiki na kusan sati biyu tun Humaira na fushi tana ganin abun kamar cin fuska harta ajiye komai ta fahimci yana da buqatar tallafi, ita shaidace akan son da yakewa Umaimah amma tambayar da takewa kanta me ya hanashi dawo da ita duk tsahon lokacin nan se yanzu da tayi aure ze nemi kashe kansa a tsaye da tunani? Hajiya kanta ta shiga damuwa, ta ringa ce masa
"Me yasa Babana, kasan kana son dawo da matarka duk tsahon lokacin nan meyasa baka maido ta ba?"
"Hajiya ni bani da ra'ayin dawo da ita" ya bata amsa cike da dacin zuciya, Jalilah datazo dubashi tayi caraf tace
"Qarya kakeyi kuma sedai so ya kashe ka wlh badai ka sake zama da Umaimahba mara zuciya kawai wato kai nan da lambu lambu kayi kana jira lokaci ya qara turawa ka maidota ko to ko bayan ran Hajiya baka isa ba balle yanzu da take a raye"
"Kiyi mun shiru Jalilah ni na gaya miki haka?" Hajiyar ta daka mata tsawa kafinta juya kan Khalil daya rintse ido saboda yanda kansa yake sarawa idan ana magana da qarfi tace
"Kayi qwauran baki Babana da kuma ni bana adawa da dawowar Matarka, idanhar dan abinda tayi mun ne wlh na dade da yafe mata tuntuni idan da ka nuna mun kana ra'ayin dawo da ita tuni dana shige maka gaba kuma ko yanzu zanci gaba dayi maka addu'a idan har da Alkhairi a zamanku Allah ya kawo dalilin da zata dawo gareka"
A ransa ya amsa da "Amin" Jalila kuwa a fili ta furta
"In sha Allahu babu, ba zata sake dawowa zuri'armu ba data samu ta auru dakyar taje can ta qarata muda ita sedai dan zuri'ar dake tsakani amma da babu abinda ze sake hadamu".
Sati biyu aka saka tariyar Umaiman, ana saura kwana hudu ta tare yaje gidansu cikin matuqar qarfin hali. Ba Umaimah ba hatta su Mama sunyi matuqar mamakin ganin Khalil din da kuma yanayinsa daya nuna baya jin dadi har seda Mama ta tambayeshi yayi murmushi kawai yace mata rashin lafiya yayi ya kasa dauke idonsa daga kan Umaimah data sha gyaran Amarare tayi bulbul tana sheqi daya tuna matar wani ce a yanzu seya sadda kansa qasa wani abu me daci da maiqo yana taso masa. Shirun da Khalil din yayi ya saka Mama tashi ta basu guri, da alama zuwannata ne bayan tsayin shekaru yau ya waiwayi Umaiman kenan qila daman irin wannan lokacin yake jira.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*
*DUKKAN YABO DA GODIYA SUN TABBATA GA ALLAH SWT DAYA BANI IKON KAMMALA WANNAN LITTAFI, INA FATAN ALLAH YASA MU'AMFANA DA DARUSSAN DA SUKE CIKI, INDA MUKA KUSKURE UBANGIJI KA YAFE MU DARAJAR ANNABI DA ALQU'ANI* 🤲🏼🤲🏼
*AMINCIN ALLAH YA TABBATA A GAREKU MASOYAN RUBUTUN UMMU-MAHEER, UBANGIJI YA SOKU, YA JIBANCI LAMURANKU, NAGODE DA TARIN QAUNAR DA KUKA NUNAMUN KUNE QARFIN GUIWATA KUNA DOMINKU NAKEYI. WANDA NA BATAWA A TSAYIN LOKACIN DA NAKE RUBUTUN NAN INA NEMAN AFUWARSU, A BANGARENA NA YAFE DUK WADDA TA ZAGENI NA YAFE MATA 🥲🥲 ALLAH YA YAFE MANA BAKI DAYA SE MUN SAKE HADUWA A SABON LITTAFI NA DA ZEZO IDAN ALLAH YA YARDA*
*MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER*
*Last page*
Bayan Mama ta fita sun kwashi kusan minti biyar kafin ya nisa a hankali ya kira sunanta, tsigar jikinta suka zuba dalilin saukar muryarsa da lafazin da yayi amfani dashi gurin kiran sunanta se ta shiga a'uziyya a zuciyarta tana kiran sunayen Allah. Cikin sanyi ya shiga ce mata
"Umaimah, da farko zan fara da tayaki murna bisa auran da kika daura, Allah ya sanya Alkhairi ya kuma kade duk wata fitina da abin qi a gidan aurenki ya sanya Albarka da farin ciki a rayuwarku sannan se abu na biyu ina roqon a tsayin zaman mu idan nayi miki wani abu na kuskure ki yafe mun" kuka ta fashe dashi jin abinda ya fada, idan ba dai son ya qara mata laifi ba wace magana ce kuma wai ta yafe masa ita me yayi mata sedai idan so yake yace baze yafe mata ba kawai yafi ya fito kai tsaye akan wannan alayenda yakeyi.
"Ki dena kuka dan Allah, ko ba zaki iya yafe mun ba?" Ya fada muryarsa a karye seta dago da sauri ta kalleshi, idanunta sun gaza boye tarin qaunarsa da kewarsa dake cinta ya kauda nasa idon daga kallonta yana tunatar da kansa matar wani ce cikin kukan tace
"Bakayi mun komai ba Khalil, Allah ne shaida ka kasance Mijin kwarai kuma uba na gari gurin Yayansa, ni na zalunceka kuma naga sakayyar hakan akaina haqqinka yana ta dawainiya dani, ka tausayamun ka yafe mun ko zan samu nutsuwa a sabuwar rayuwar da zan shiga" ta fada cikin tsananin kuka. Yaqe yayi yadan kalleta yace
"Na dade da yafe miki Umaimah, abinda kikayi mun tsakanina dake ban riqeki ba, daga randa Hajiya ta furta ta yafe duk abinda kikayi mata nima na yafe fushin tabata da kikayi"
"Hajiya ta yafe mun?" Ta tambayeshi cikin tsananin mamaki seya daga mata kai cike da tabbatarwa yace
"Ta yafe miki tuni, Hajiya bata kwanciya bacci da fushin kowa a ranta kuma muma akan haka ta horemu mu ringa yafiya akan duk abinda aka mana. Babu abinda riqon wani a zuciyarka ze qareka dashi a rayuwa sabanin haka idan ka yafe se kaima Allah ya dubeka ya yafe maka naka kurakuren da suke tsakaninka dashi". Qirjinta ya ringa bugawa, wani sabon nauyi da kunyarsu ya sake lullubeta a ranta ta ringa godewa Allah da bebi ta halinta ba ya zabarwa Yayanta tsatso na kwarai, sukam sunada karamci gashi su rabauta da zuciyar da ba kowa Allah yayiwa Arziqin irinta ba ta yafiya. A hankali cikin rarrabewar harshe tace
"Toh toh me yasa duk tsahon lokacin nan tunda ka yafe mun amma ka kasa waiwayata?" se yayi murmushi kawai ba tareda yace mata komai ba har ta fitar da ran samun amsarsa taji yace
"Kina so kisan meya hanani waiwayarki tsahon lokacin nan?" Ya fada yana kallon idonta seta girgiza masa kai alamar Eh ta sauke kanta qasa
"Saboda ina sonki, bana iya riqe kaina idan ina tare dake. Zuciyata bata taba fushi dake idan har nazo inda kike tabbas nasan zan karaya na kasa cika alqawarin dana daukarwa kaina na haqura dake har Abada Umaimah".
Zabura tayi ta dago ta kalleshi saboda abinda ya fada, hawayen da ta samu suka tsaya suka sake balle mata cikin tsananin kuka tace masa
"Saboda baka yafemun bako?"
"Na yafe miki amma bazan miki qarya ba duk sanda na kalleki nasan zan ringa tuna sanda kika tsaya gabana kika zagi Hajiyata" ya fada idanunsa suna sake canza kala da alamar abinda ya fada din ya sosa masa rai. Umaimah ta duqar da kanta qasa, da tana da damar maido da baya data canza abubuwa da dama cikin rayuwarta, Khalil yaci gaba da cewa "bana so mu sake komawa rayuwar aure tare son da nake miki yakai girman da zan iya jure komai da zakiyi mun naji tsoron kar soyayyata ta halakar damu gaba daya kar kawaicina ya kaimu wuta saboda Allah babu ruwansa shiyasa na zabi haqura da son zuciyata na barki badan bana sonki ba ko na dena sonki ba kuma dan bana son ci gaba da zaman aure dake ba sedan kawai hakan shine maslaha a rayuwarmu gaba daya kullum nayi sallah sena roqi ubangiji ya zaba mun mafi Alkhairi a cikin komai na rayuwata duk abinda na rasa kuma ina fatan yasa nayi tawakkali ya bani dangana kuma Alhamdulillah, ina cikin farin ciki tattare da musanyar da yayi mun kullum cikin gode masa nake kema ina miki fatan ki samu farin ciki sama da wanda nake ciki a yanzu zanci gaba da Addu'a yanda na rasaki a duniya, Allah ubangiji ya hadamu qarqashin inuwa daya a Aljanna ya dawo mun dake a matsayin MATATA a inda babu DAMUWA babu BAQIN CIKI babu KISHI babu SAKI babu MUTUWA balle SAKIN AURE".
Kuka take tamkar ranta ze fita shikansa dauriya ce kawai irin tasa amma da zeyi kukan yasan ze samu sauqin radadin da yake ciki. Ya ajiye mata wata Leda fara mara girma sosai sannan ya ciro wata Envelope daga Aljihunsa ya dora akai yana cewa
"Kiyi haquri da wannan akwai ayyukan da nakeyi duk na zuba kudade kuma abin yazo babu shiri, Naji Hajiya tace zatazo gobe may be su taho tareda yara dukda yanzun ma nacewa Mu'ayyad yazo ya rakoni yaqi da alama kishi yake sosai fa" ya fada yana dan murmushi da bekai zuciya ba, bata dago ba kuma bata bar kukan ba, ya sake cewa
"Ki dena kukan nan haka kar Angonki yaci tarata yace na saka masa kuka Amarya, yawwa sannan dan Allah banda tsaki banda muguda baki mazan yanzu saurin hannune dasu be zama lallai yana da haquri iri na ba kar azo ana daddoke mana ke" dukda kukan da take seda tayi dariya dan yanda yayi maganar tasa yace mata
"Ko kefa, bari na tashi naje dan ban gayawa Babyna inda zanje ba kar ta jini shiru" ya miqe itama ta miqe tabi bayansa maganar Babynsa na sukar zuciyarta.
"Me yasa Babana, kasan kana son dawo da matarka duk tsahon lokacin nan meyasa baka maido ta ba?"
"Hajiya ni bani da ra'ayin dawo da ita" ya bata amsa cike da dacin zuciya, Jalilah datazo dubashi tayi caraf tace
"Qarya kakeyi kuma sedai so ya kashe ka wlh badai ka sake zama da Umaimahba mara zuciya kawai wato kai nan da lambu lambu kayi kana jira lokaci ya qara turawa ka maidota ko to ko bayan ran Hajiya baka isa ba balle yanzu da take a raye"
"Kiyi mun shiru Jalilah ni na gaya miki haka?" Hajiyar ta daka mata tsawa kafinta juya kan Khalil daya rintse ido saboda yanda kansa yake sarawa idan ana magana da qarfi tace
"Kayi qwauran baki Babana da kuma ni bana adawa da dawowar Matarka, idanhar dan abinda tayi mun ne wlh na dade da yafe mata tuntuni idan da ka nuna mun kana ra'ayin dawo da ita tuni dana shige maka gaba kuma ko yanzu zanci gaba dayi maka addu'a idan har da Alkhairi a zamanku Allah ya kawo dalilin da zata dawo gareka"
A ransa ya amsa da "Amin" Jalila kuwa a fili ta furta
"In sha Allahu babu, ba zata sake dawowa zuri'armu ba data samu ta auru dakyar taje can ta qarata muda ita sedai dan zuri'ar dake tsakani amma da babu abinda ze sake hadamu".
Sati biyu aka saka tariyar Umaiman, ana saura kwana hudu ta tare yaje gidansu cikin matuqar qarfin hali. Ba Umaimah ba hatta su Mama sunyi matuqar mamakin ganin Khalil din da kuma yanayinsa daya nuna baya jin dadi har seda Mama ta tambayeshi yayi murmushi kawai yace mata rashin lafiya yayi ya kasa dauke idonsa daga kan Umaimah data sha gyaran Amarare tayi bulbul tana sheqi daya tuna matar wani ce a yanzu seya sadda kansa qasa wani abu me daci da maiqo yana taso masa. Shirun da Khalil din yayi ya saka Mama tashi ta basu guri, da alama zuwannata ne bayan tsayin shekaru yau ya waiwayi Umaiman kenan qila daman irin wannan lokacin yake jira.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*
*DUKKAN YABO DA GODIYA SUN TABBATA GA ALLAH SWT DAYA BANI IKON KAMMALA WANNAN LITTAFI, INA FATAN ALLAH YASA MU'AMFANA DA DARUSSAN DA SUKE CIKI, INDA MUKA KUSKURE UBANGIJI KA YAFE MU DARAJAR ANNABI DA ALQU'ANI* 🤲🏼🤲🏼
*AMINCIN ALLAH YA TABBATA A GAREKU MASOYAN RUBUTUN UMMU-MAHEER, UBANGIJI YA SOKU, YA JIBANCI LAMURANKU, NAGODE DA TARIN QAUNAR DA KUKA NUNAMUN KUNE QARFIN GUIWATA KUNA DOMINKU NAKEYI. WANDA NA BATAWA A TSAYIN LOKACIN DA NAKE RUBUTUN NAN INA NEMAN AFUWARSU, A BANGARENA NA YAFE DUK WADDA TA ZAGENI NA YAFE MATA 🥲🥲 ALLAH YA YAFE MANA BAKI DAYA SE MUN SAKE HADUWA A SABON LITTAFI NA DA ZEZO IDAN ALLAH YA YARDA*
*MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER*
*Last page*
Bayan Mama ta fita sun kwashi kusan minti biyar kafin ya nisa a hankali ya kira sunanta, tsigar jikinta suka zuba dalilin saukar muryarsa da lafazin da yayi amfani dashi gurin kiran sunanta se ta shiga a'uziyya a zuciyarta tana kiran sunayen Allah. Cikin sanyi ya shiga ce mata
"Umaimah, da farko zan fara da tayaki murna bisa auran da kika daura, Allah ya sanya Alkhairi ya kuma kade duk wata fitina da abin qi a gidan aurenki ya sanya Albarka da farin ciki a rayuwarku sannan se abu na biyu ina roqon a tsayin zaman mu idan nayi miki wani abu na kuskure ki yafe mun" kuka ta fashe dashi jin abinda ya fada, idan ba dai son ya qara mata laifi ba wace magana ce kuma wai ta yafe masa ita me yayi mata sedai idan so yake yace baze yafe mata ba kawai yafi ya fito kai tsaye akan wannan alayenda yakeyi.
"Ki dena kuka dan Allah, ko ba zaki iya yafe mun ba?" Ya fada muryarsa a karye seta dago da sauri ta kalleshi, idanunta sun gaza boye tarin qaunarsa da kewarsa dake cinta ya kauda nasa idon daga kallonta yana tunatar da kansa matar wani ce cikin kukan tace
"Bakayi mun komai ba Khalil, Allah ne shaida ka kasance Mijin kwarai kuma uba na gari gurin Yayansa, ni na zalunceka kuma naga sakayyar hakan akaina haqqinka yana ta dawainiya dani, ka tausayamun ka yafe mun ko zan samu nutsuwa a sabuwar rayuwar da zan shiga" ta fada cikin tsananin kuka. Yaqe yayi yadan kalleta yace
"Na dade da yafe miki Umaimah, abinda kikayi mun tsakanina dake ban riqeki ba, daga randa Hajiya ta furta ta yafe duk abinda kikayi mata nima na yafe fushin tabata da kikayi"
"Hajiya ta yafe mun?" Ta tambayeshi cikin tsananin mamaki seya daga mata kai cike da tabbatarwa yace
"Ta yafe miki tuni, Hajiya bata kwanciya bacci da fushin kowa a ranta kuma muma akan haka ta horemu mu ringa yafiya akan duk abinda aka mana. Babu abinda riqon wani a zuciyarka ze qareka dashi a rayuwa sabanin haka idan ka yafe se kaima Allah ya dubeka ya yafe maka naka kurakuren da suke tsakaninka dashi". Qirjinta ya ringa bugawa, wani sabon nauyi da kunyarsu ya sake lullubeta a ranta ta ringa godewa Allah da bebi ta halinta ba ya zabarwa Yayanta tsatso na kwarai, sukam sunada karamci gashi su rabauta da zuciyar da ba kowa Allah yayiwa Arziqin irinta ba ta yafiya. A hankali cikin rarrabewar harshe tace
"Toh toh me yasa duk tsahon lokacin nan tunda ka yafe mun amma ka kasa waiwayata?" se yayi murmushi kawai ba tareda yace mata komai ba har ta fitar da ran samun amsarsa taji yace
"Kina so kisan meya hanani waiwayarki tsahon lokacin nan?" Ya fada yana kallon idonta seta girgiza masa kai alamar Eh ta sauke kanta qasa
"Saboda ina sonki, bana iya riqe kaina idan ina tare dake. Zuciyata bata taba fushi dake idan har nazo inda kike tabbas nasan zan karaya na kasa cika alqawarin dana daukarwa kaina na haqura dake har Abada Umaimah".
Zabura tayi ta dago ta kalleshi saboda abinda ya fada, hawayen da ta samu suka tsaya suka sake balle mata cikin tsananin kuka tace masa
"Saboda baka yafemun bako?"
"Na yafe miki amma bazan miki qarya ba duk sanda na kalleki nasan zan ringa tuna sanda kika tsaya gabana kika zagi Hajiyata" ya fada idanunsa suna sake canza kala da alamar abinda ya fada din ya sosa masa rai. Umaimah ta duqar da kanta qasa, da tana da damar maido da baya data canza abubuwa da dama cikin rayuwarta, Khalil yaci gaba da cewa "bana so mu sake komawa rayuwar aure tare son da nake miki yakai girman da zan iya jure komai da zakiyi mun naji tsoron kar soyayyata ta halakar damu gaba daya kar kawaicina ya kaimu wuta saboda Allah babu ruwansa shiyasa na zabi haqura da son zuciyata na barki badan bana sonki ba ko na dena sonki ba kuma dan bana son ci gaba da zaman aure dake ba sedan kawai hakan shine maslaha a rayuwarmu gaba daya kullum nayi sallah sena roqi ubangiji ya zaba mun mafi Alkhairi a cikin komai na rayuwata duk abinda na rasa kuma ina fatan yasa nayi tawakkali ya bani dangana kuma Alhamdulillah, ina cikin farin ciki tattare da musanyar da yayi mun kullum cikin gode masa nake kema ina miki fatan ki samu farin ciki sama da wanda nake ciki a yanzu zanci gaba da Addu'a yanda na rasaki a duniya, Allah ubangiji ya hadamu qarqashin inuwa daya a Aljanna ya dawo mun dake a matsayin MATATA a inda babu DAMUWA babu BAQIN CIKI babu KISHI babu SAKI babu MUTUWA balle SAKIN AURE".
Kuka take tamkar ranta ze fita shikansa dauriya ce kawai irin tasa amma da zeyi kukan yasan ze samu sauqin radadin da yake ciki. Ya ajiye mata wata Leda fara mara girma sosai sannan ya ciro wata Envelope daga Aljihunsa ya dora akai yana cewa
"Kiyi haquri da wannan akwai ayyukan da nakeyi duk na zuba kudade kuma abin yazo babu shiri, Naji Hajiya tace zatazo gobe may be su taho tareda yara dukda yanzun ma nacewa Mu'ayyad yazo ya rakoni yaqi da alama kishi yake sosai fa" ya fada yana dan murmushi da bekai zuciya ba, bata dago ba kuma bata bar kukan ba, ya sake cewa
"Ki dena kukan nan haka kar Angonki yaci tarata yace na saka masa kuka Amarya, yawwa sannan dan Allah banda tsaki banda muguda baki mazan yanzu saurin hannune dasu be zama lallai yana da haquri iri na ba kar azo ana daddoke mana ke" dukda kukan da take seda tayi dariya dan yanda yayi maganar tasa yace mata
"Ko kefa, bari na tashi naje dan ban gayawa Babyna inda zanje ba kar ta jini shiru" ya miqe itama ta miqe tabi bayansa maganar Babynsa na sukar zuciyarta.