Sashe 179
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Munafuka?" Ya maimaita kalmar cikin mamaki, Umaimah ta kira Hajiya da Munafukan akan me?
"Kuma itama Hajiya da laifinta fa Yaya, saboda Anty Jalilah ta mareta bakaga yanda Hajiyar ta taso mata ba kamar zata rama mata marin kuma wai ta shiga lallashinta tana bata haquri ai wlh naji dadi dan antyn ta gaggaya mata magana ta kuma jaddada mata aurenka babu fashi sedai ta mutu da yake mahaukaciyace se cewa tayi se tayi Ajalinka ni kuwa nayi recording wlh kuma ko kwarzane ya sameka se mun hadu da ita a Kotu akanta zan fara practicing profession dina" Khalifa yaci gaba da magana Khalil dai kallonsa kawai yakeyi shi maganar zata kashe ma bata bashi mamaki ba dan ba yau ya faraji ba tun kafin ya aureta take jaddada masa wannan kuma ta gwada ya gani Munafuka data kira Hajiya dashi ne ya daure masa kai sosai ya bashi mamaki dan be dauka rashin darajarta harya kai haka ba, ya zata dai shi da yake marainin wayonta take zaginsa sanda taso abun akansa ya tsaya ashe ya tsallake ya isa har kan uwar data haifeshi.
Can qasan ransa sosai yake jin fushi da bacin ran abinda tayin yana kuma ayyana abubuwan da zeyi mata na daukar fansa amma kuma cikin zuciyarsa ko kusa ya kasa hasaso laifin da tayi balle ya samu kwarin guiwar hukuntata, dafe kansa yayi yana karanta hasbunallahu wani'imal wakeel a fili seda ya samu yar nutsuwa daga abinda yakeji kafin ya miqe a hankali kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki ya wuce cikin gidan Khalifa ya bishi da kallo.
UMAIMAH
Dan kanta ta gaji da zage zagen ganin ya haye sama ya barta nan se kuma ta juya kan kayan dake cikin falon ta shiga jifa dasu tana kuka kamar wadda kanta ya tabu, kan kujera ta zube taci gaba da kukan, kamar wadda aka tsikara ta miqe tunawa da maganar Mama Hauwa da tace sunyi magana da Hajiya dazu kuma ta gaya mata a satin nan za'ajewa Khalil neman aure wato ma Hajiya ce ta shirya komai, qila ma ita ta turashi yaga Humairan ita take so ta hada auran me yasa tun farko batayi tunanin bama. Fita tayi ta wuce bangaren Hajiyar, tun daga kan barander ta jiyo muryar Jalilah na cewa
"Nifa bazan tafi ba Hajiya se Hussaini yazo mun qarasa lissafin nan, da za'a bi tatawa ma a hada komai har lefen su tafi dashi kawai a huta da jeka ka dawo kinga gari da nisa ga yanayin hanya an huta tunda daman Mazan ne dai zasu koma su kai"
"Toh uwar Azarbabi duk saurinki dai ai se kin jira sunje sun tambaya ance an basu kafin kice akai lefe ko?" Hajiya ta mayar mata cikin raha kafin Jalilan ta sake cewa wani abu Umaimah ta banka qofar falon ta shiga duk suka kalleta a tsorace saboda bazatan da tayi musu.
"Lafiya Umaimah ko jikin ne?" Hajiya ta fada seta watsawa Hajiyar wani kallo tace
"Dole ki tambayeni ko lafiya Qasurgumar munafuka. Ni daman na sani babu yanda za'ayi wata uwar Miji ta qaunaceka tsakani da Allah har ta fifitaka sama da yayan data haifa ashe jira kike na saki jiki dake kafin ki nuna mun Halinku na rashin Amana to wallahi bari kiji ni kadai kika haifawa Khalil ba kuma ki isa ki sake soko wata mace cikin rayuwarsa ba bayan ni duk wani munafunchi da kutunguilar ku ya qare akanku amma Khalil nan gani nan bari idan bakiyi wasa bama kedashi sedai gani daga nesa dan se nayi...." Marin da Jalilah ta dauketa dashi ne ya sakata yin shirun dole ba tareda ta shirya ha ta dafe idonta da taji kamar an watsa mata barkono a ciki.
Nunata Jalilan tayi tana cewa
"Ke qaramar mahaukaciya ki iya bakinki ki kuma san a inda kike, tsakaninki da Khalil canku gane dan da saninsa ya kwasowa kansa Annoba dan haka duk wani haukanki da dabbanci ya tsaya akansa na rantse da girman Allah koda wasa kika sake takowa nan kika ce zaki harari uwarmu balle har ta kai ga ki zageta sena zubar miki da haqora na karyaki na watsar da abin banza ko yanzu darajar abinda yake jikinki kikaci bazan dakeki na yi dakon rai na amma dana banbance miki tsakanin aya da tsakuwa yanzun mara kunyar qarya"
"Ya isa haka Jalilah, wani irin sakarci ne wanann bakiga a halin da take ciki bane zaki mareta?" Hajiya ta daka mata tsawa se Jalilan ta kalli Hajiya fuska dauke da mamaki tace
"Hajiya naga halin da take ciki Halin hauka ba ta samu zaucewar tunani dan shine ze saka ta aikata abinda tayi yanzu to ko Dawanau ce a kanta qarewarta ita ya shafa nidai na fada" seta juya kan Umaimah dake dafe da ido tace
"Sannan kuma maganar hadin aure da kikeyi ta isa ne shiyasa ta hada, wace uwace ma har zata dauke ido danta ya zauna da shaidaniya irin tsahon shekarun nan bata saka ya kadaki inda ya kwasoki ba? Yazu kuwa aure take so tayi masa da yarinyar kirki data san mutunchin mutane ba irinki ba kuma ko zaki mutu se anyi auran nan in Allah ya yarda".
Cikin qunar rai Umaiman ta kalleta tace
"Haka kikace? To na rantse da Allah se nayi sanadin Khalil sedai kowa ya rasa nida ku duk se dai muyi Asara" tana fadar haka ta juya fuu Hajiya ta bita tana kiran Sunanta Jalilah ma bin bayansu tana cewa
"Ai idan Khalil ya mutu Umaimah se kinfi kowa shiga uku wlh mu sedai muyi jimami na rashin dan uwa ke kuwa Allah dai ya taqaita amma inaga idan baki bishi ba se kin haukace".
Sanda ta koma bangarenta zama tayi a qasa cikin kayan data farfasa ta sake fashewa da kukan dayafi ma dazu, Ruqayya ta tsaya tsuru daga gefe tsoron kulata takeyi karta huce akanta amma haka ta ja numfashi ta matsa kadan tana ce mata
"Hajiya kiyi haquri ki dena kukan nan kodan halin da kike ciki, kishiya ai ba ciwon Ajali bace ba kuma kanki aka fara ba dan Allah ki tattara hankalinki guri daya ki nutsu, addu'a ya kamata ki tashi tsaye kiyi akan duk ma wadda zata shigo Allah ya tsare ki daga sharrinta ya hadaki da Alkhairinta".
"Ruqayya idan kika sake yimun magana se naci abu ta kaza kazan ubanki" Umaiman ta fada tana kallonta da jajayen kumburarrun idanunta da suke tsiyayar sa hawaye kafin ta juya taci gaba da kukan kamar yarinya se kuma ta ta miqe ta shige dakinta, wayarta ta dauka ta shiga kiraj Safinah tana dagawa tace
"Safina duk inda kike duk abinda kikeyi ki bari ki maido mun da kudina da kuka damfareni keda dan abu ta kaza kazan Malaminki, kuma daga yau ko hanya karki bari mu hadu idan ba haka ba sena huce haushin bata mun lokaci da kika kaini akayi kuka yaudareni na dauka aikinsa yayi ashe zagon qasa yayi mun ya daka rusa komai" ta qarasa tana rushewa da kuka.
Safina dake zaune a falo tayi baqi qannen Mijinta ta miqe ta shige daki tana ce musu tana zuwa. Seda ta shiga bandaki ta kullo qofar dan kar wani ya shigo yaji abinda take fada kafin tace
"Haba Umaimah kiyi shiru kiyimun bayani me ya faru kuma? Ina dazu da safe kike ce mun har aiki ya fara ci me kuma ya faru yanzu har ya kawo wannan maganar?"
"Babu ruwanki sa abinda ya faru kwai kiyi abinda nace idan ba haka ba kin san halina wallahi se nazo na farke miki laya, yanda banyi nasara ba kema se Alqadarinki ya karye wlh" Umaiman ta sake fada a fusace se Safina tayi saurin mayar mata itama cikin fushi tace
"Kinga bafa tsoronki nake ji ba da zaki ringa gaya mun magana ina wani lallashinki, aiki na rakaki akayi miki da yardar kuma ba daukarki nayi akai na ballantana kice ke uwar garaje da jaraba an ce miki kibi komai a sannu amma ba haka ba na tabbata yanzun ma wani haukan kika tafka ya warware komai zakizo kina dora laifi akaina. Daman ai na gaya miki ko kinyi Asiri dole ki hada da kissa idan kina so kiga daidai amma ke kamar wadda ake girki a zuciyarta dan qaramin abu kin dau zafi bazaki ringa tankwara zuciyarki kina dauke kai ba ai ita rayuwa bata yuwuwa haka idan kana so kaci riba ai seka yi haquri kayi juriya".
Shiru Umaimah tayi tana rusa mata kuka, Safina ta sake jan tsaki dan harga Allah ita kanta Umaiman ta isheta inaga Khalil kuma ai wallahi yana bala'in qoqari, sake ce mata tayi
"Kinga kuka baya maganin komai gara ki bude baki ki gayamun abinda ya faru najin idan da akwai ta inda zan taimaka miki in kuma Malam zan kira na gaya masa toh se musan abinyi"
"Ni karki sake sakomun wani malam a magana kuma ba haqura nayi ba se kin biyani kudina, bayan yace mun maganar aure zata watse kuma se yanda nayi dasu gashi nan ba inda aka je ni banga komai ba. A gaban Hajiyar yar uwarta take jaddadamun aure babu fashi kuma bata hana ba bayan har naman kan na dafa kuma taci sannan shi kansa na bashi umarnin ya kira yarinyar ya gaya mata ta fita a sabgarsa yaqi qarshe ma se munafukar uwar ruqon nata ce ta daga wayar har takr yaba mun magana tana gayamin wani satin za'aje tambaya, wallahi Safina ji nake kamar na dau wuqa na cakawa kaina kawai na mutu na huta da baqin ciki" ta sake rushewa da Kuka wiwi.
"Kuma itama Hajiya da laifinta fa Yaya, saboda Anty Jalilah ta mareta bakaga yanda Hajiyar ta taso mata ba kamar zata rama mata marin kuma wai ta shiga lallashinta tana bata haquri ai wlh naji dadi dan antyn ta gaggaya mata magana ta kuma jaddada mata aurenka babu fashi sedai ta mutu da yake mahaukaciyace se cewa tayi se tayi Ajalinka ni kuwa nayi recording wlh kuma ko kwarzane ya sameka se mun hadu da ita a Kotu akanta zan fara practicing profession dina" Khalifa yaci gaba da magana Khalil dai kallonsa kawai yakeyi shi maganar zata kashe ma bata bashi mamaki ba dan ba yau ya faraji ba tun kafin ya aureta take jaddada masa wannan kuma ta gwada ya gani Munafuka data kira Hajiya dashi ne ya daure masa kai sosai ya bashi mamaki dan be dauka rashin darajarta harya kai haka ba, ya zata dai shi da yake marainin wayonta take zaginsa sanda taso abun akansa ya tsaya ashe ya tsallake ya isa har kan uwar data haifeshi.
Can qasan ransa sosai yake jin fushi da bacin ran abinda tayin yana kuma ayyana abubuwan da zeyi mata na daukar fansa amma kuma cikin zuciyarsa ko kusa ya kasa hasaso laifin da tayi balle ya samu kwarin guiwar hukuntata, dafe kansa yayi yana karanta hasbunallahu wani'imal wakeel a fili seda ya samu yar nutsuwa daga abinda yakeji kafin ya miqe a hankali kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki ya wuce cikin gidan Khalifa ya bishi da kallo.
UMAIMAH
Dan kanta ta gaji da zage zagen ganin ya haye sama ya barta nan se kuma ta juya kan kayan dake cikin falon ta shiga jifa dasu tana kuka kamar wadda kanta ya tabu, kan kujera ta zube taci gaba da kukan, kamar wadda aka tsikara ta miqe tunawa da maganar Mama Hauwa da tace sunyi magana da Hajiya dazu kuma ta gaya mata a satin nan za'ajewa Khalil neman aure wato ma Hajiya ce ta shirya komai, qila ma ita ta turashi yaga Humairan ita take so ta hada auran me yasa tun farko batayi tunanin bama. Fita tayi ta wuce bangaren Hajiyar, tun daga kan barander ta jiyo muryar Jalilah na cewa
"Nifa bazan tafi ba Hajiya se Hussaini yazo mun qarasa lissafin nan, da za'a bi tatawa ma a hada komai har lefen su tafi dashi kawai a huta da jeka ka dawo kinga gari da nisa ga yanayin hanya an huta tunda daman Mazan ne dai zasu koma su kai"
"Toh uwar Azarbabi duk saurinki dai ai se kin jira sunje sun tambaya ance an basu kafin kice akai lefe ko?" Hajiya ta mayar mata cikin raha kafin Jalilan ta sake cewa wani abu Umaimah ta banka qofar falon ta shiga duk suka kalleta a tsorace saboda bazatan da tayi musu.
"Lafiya Umaimah ko jikin ne?" Hajiya ta fada seta watsawa Hajiyar wani kallo tace
"Dole ki tambayeni ko lafiya Qasurgumar munafuka. Ni daman na sani babu yanda za'ayi wata uwar Miji ta qaunaceka tsakani da Allah har ta fifitaka sama da yayan data haifa ashe jira kike na saki jiki dake kafin ki nuna mun Halinku na rashin Amana to wallahi bari kiji ni kadai kika haifawa Khalil ba kuma ki isa ki sake soko wata mace cikin rayuwarsa ba bayan ni duk wani munafunchi da kutunguilar ku ya qare akanku amma Khalil nan gani nan bari idan bakiyi wasa bama kedashi sedai gani daga nesa dan se nayi...." Marin da Jalilah ta dauketa dashi ne ya sakata yin shirun dole ba tareda ta shirya ha ta dafe idonta da taji kamar an watsa mata barkono a ciki.
Nunata Jalilan tayi tana cewa
"Ke qaramar mahaukaciya ki iya bakinki ki kuma san a inda kike, tsakaninki da Khalil canku gane dan da saninsa ya kwasowa kansa Annoba dan haka duk wani haukanki da dabbanci ya tsaya akansa na rantse da girman Allah koda wasa kika sake takowa nan kika ce zaki harari uwarmu balle har ta kai ga ki zageta sena zubar miki da haqora na karyaki na watsar da abin banza ko yanzu darajar abinda yake jikinki kikaci bazan dakeki na yi dakon rai na amma dana banbance miki tsakanin aya da tsakuwa yanzun mara kunyar qarya"
"Ya isa haka Jalilah, wani irin sakarci ne wanann bakiga a halin da take ciki bane zaki mareta?" Hajiya ta daka mata tsawa se Jalilan ta kalli Hajiya fuska dauke da mamaki tace
"Hajiya naga halin da take ciki Halin hauka ba ta samu zaucewar tunani dan shine ze saka ta aikata abinda tayi yanzu to ko Dawanau ce a kanta qarewarta ita ya shafa nidai na fada" seta juya kan Umaimah dake dafe da ido tace
"Sannan kuma maganar hadin aure da kikeyi ta isa ne shiyasa ta hada, wace uwace ma har zata dauke ido danta ya zauna da shaidaniya irin tsahon shekarun nan bata saka ya kadaki inda ya kwasoki ba? Yazu kuwa aure take so tayi masa da yarinyar kirki data san mutunchin mutane ba irinki ba kuma ko zaki mutu se anyi auran nan in Allah ya yarda".
Cikin qunar rai Umaiman ta kalleta tace
"Haka kikace? To na rantse da Allah se nayi sanadin Khalil sedai kowa ya rasa nida ku duk se dai muyi Asara" tana fadar haka ta juya fuu Hajiya ta bita tana kiran Sunanta Jalilah ma bin bayansu tana cewa
"Ai idan Khalil ya mutu Umaimah se kinfi kowa shiga uku wlh mu sedai muyi jimami na rashin dan uwa ke kuwa Allah dai ya taqaita amma inaga idan baki bishi ba se kin haukace".
Sanda ta koma bangarenta zama tayi a qasa cikin kayan data farfasa ta sake fashewa da kukan dayafi ma dazu, Ruqayya ta tsaya tsuru daga gefe tsoron kulata takeyi karta huce akanta amma haka ta ja numfashi ta matsa kadan tana ce mata
"Hajiya kiyi haquri ki dena kukan nan kodan halin da kike ciki, kishiya ai ba ciwon Ajali bace ba kuma kanki aka fara ba dan Allah ki tattara hankalinki guri daya ki nutsu, addu'a ya kamata ki tashi tsaye kiyi akan duk ma wadda zata shigo Allah ya tsare ki daga sharrinta ya hadaki da Alkhairinta".
"Ruqayya idan kika sake yimun magana se naci abu ta kaza kazan ubanki" Umaiman ta fada tana kallonta da jajayen kumburarrun idanunta da suke tsiyayar sa hawaye kafin ta juya taci gaba da kukan kamar yarinya se kuma ta ta miqe ta shige dakinta, wayarta ta dauka ta shiga kiraj Safinah tana dagawa tace
"Safina duk inda kike duk abinda kikeyi ki bari ki maido mun da kudina da kuka damfareni keda dan abu ta kaza kazan Malaminki, kuma daga yau ko hanya karki bari mu hadu idan ba haka ba sena huce haushin bata mun lokaci da kika kaini akayi kuka yaudareni na dauka aikinsa yayi ashe zagon qasa yayi mun ya daka rusa komai" ta qarasa tana rushewa da kuka.
Safina dake zaune a falo tayi baqi qannen Mijinta ta miqe ta shige daki tana ce musu tana zuwa. Seda ta shiga bandaki ta kullo qofar dan kar wani ya shigo yaji abinda take fada kafin tace
"Haba Umaimah kiyi shiru kiyimun bayani me ya faru kuma? Ina dazu da safe kike ce mun har aiki ya fara ci me kuma ya faru yanzu har ya kawo wannan maganar?"
"Babu ruwanki sa abinda ya faru kwai kiyi abinda nace idan ba haka ba kin san halina wallahi se nazo na farke miki laya, yanda banyi nasara ba kema se Alqadarinki ya karye wlh" Umaiman ta sake fada a fusace se Safina tayi saurin mayar mata itama cikin fushi tace
"Kinga bafa tsoronki nake ji ba da zaki ringa gaya mun magana ina wani lallashinki, aiki na rakaki akayi miki da yardar kuma ba daukarki nayi akai na ballantana kice ke uwar garaje da jaraba an ce miki kibi komai a sannu amma ba haka ba na tabbata yanzun ma wani haukan kika tafka ya warware komai zakizo kina dora laifi akaina. Daman ai na gaya miki ko kinyi Asiri dole ki hada da kissa idan kina so kiga daidai amma ke kamar wadda ake girki a zuciyarta dan qaramin abu kin dau zafi bazaki ringa tankwara zuciyarki kina dauke kai ba ai ita rayuwa bata yuwuwa haka idan kana so kaci riba ai seka yi haquri kayi juriya".
Shiru Umaimah tayi tana rusa mata kuka, Safina ta sake jan tsaki dan harga Allah ita kanta Umaiman ta isheta inaga Khalil kuma ai wallahi yana bala'in qoqari, sake ce mata tayi
"Kinga kuka baya maganin komai gara ki bude baki ki gayamun abinda ya faru najin idan da akwai ta inda zan taimaka miki in kuma Malam zan kira na gaya masa toh se musan abinyi"
"Ni karki sake sakomun wani malam a magana kuma ba haqura nayi ba se kin biyani kudina, bayan yace mun maganar aure zata watse kuma se yanda nayi dasu gashi nan ba inda aka je ni banga komai ba. A gaban Hajiyar yar uwarta take jaddadamun aure babu fashi kuma bata hana ba bayan har naman kan na dafa kuma taci sannan shi kansa na bashi umarnin ya kira yarinyar ya gaya mata ta fita a sabgarsa yaqi qarshe ma se munafukar uwar ruqon nata ce ta daga wayar har takr yaba mun magana tana gayamin wani satin za'aje tambaya, wallahi Safina ji nake kamar na dau wuqa na cakawa kaina kawai na mutu na huta da baqin ciki" ta sake rushewa da Kuka wiwi.