Sashe 102
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yanda taga saqunan nasu a jejjere wani na bin wani ga kuma tarin numbobi da babu suna ya qara sakata a rudu seta bude chat din farko na Umar Tsohon saurayinta ne wanda daga shi ne ta hadu da Khalil, taso shi amma halayyarsu bata zo daya ba dan tantirin manemin matane tunda ya fito mata da muradinsa ta nuna masa ba haka take ba ya dauke qafa ya dena nemanta.
"Hadiza kenan, nayi matuqar mamaki na kuma tabbatar da baki da kunya, ke a yanda kike har kike iya mun wa'azi da gaya mun Allah yace Annabi yace ko? Koda yake daman na zargin hakan..." Kiran waya ne ya shigo ya katse mata karatun da takeyi seta daga ganin Anty Bilkisu ce matar Yaya Isma'il.
"Duk inda kike Hadiza ki maza kizo gidan nan yanzu karki koma gidan Mama" Abinda ta fada mata kenanta kashe waya daga muryarta ta karanci zallar tashin hankalin da take ciki seta kalli me Adaidaita dake ta yan waqe waqensa tace
"Malam bi nan Darmanawa zamu koma"
"Toh Hajiya" ya bata amsa yana shiga kwanar yan Katako suka ci gabada tafiya. A qofar gidan ya ajiyeta ta bashi kudinsa ta shiga, Anty Bilkisu na tsaye bakin qofar palour ta cikin shirin fita tana hangota tace
"Allah sa baki sallami me Adaidaitan ba fita zamuyi" seta juya da sauri har ya fara tafiya ta tsaidashi ta fito suka shiga yaja. Aisami tace ya kaisu unguwar su Anty Bilkin seta raya a ranta ko ba lafiya ba.
"Bani wayarki Hadiza" ta fada seta zarota a jaka ta miqa mata daidai sannan kiran Yaya Isma'il ya shigo zata daga Bilkisunta fizge ta kashe wayar gaba daya ta saka a jakarta. Tata wayarce ta shiga ruri, ta ciro ta duba shidin ne seta riqeta a hannu har kiran ya katse wani ya dake shigowa sanann ta daga. Seda ta daidaita muryarta kafin tayi sallama muryarsa ta katseta yana cewa
"Duk inda kuka tafi ku dawo yanzu Bilkisu keda Hadiza, wallahi in har kuka dara Minti talatin baki kawota gidan Mama ba a bakin auranki kuma saki uku" yana fadar haka ya kashe Bilkisu ta kalli Hadiza data tabbatar da taji abinda Yayan nata ya fada saboda kidima bata iya magana ba se Hadizan ce ta tsaida Me Adaidaita tace su Koma Na'ibawa ya karkata Mashin yana cewa
"Ba matsala hajiya aikin kudi nakeyi ai".
"Anty Bilki ki gaya mun abinda yake faruwa dan Allah dan na fara rasa tunanina. Daga zuwana gurin aiki aka bani takaddar sallama, kin kirani babu shiri kince nazo sannan ga maganganun da Yaya ya fada menene dalilin da z kafa sharadi a bakin auranki? Meyake faruwa dani dan girman Allah ki gaya mun saboda nasan abinda zan tunkara" Hadiza ta fada tana jijjiga Bilkisu da tayi shiru kamar wadda ruwa ya cinye, kallon tausayi tabi Hadizan dashi ba tateda tace komai ba ta maida kanta tana kallon waje ganin haka ya saka itama Hadizan taja Hijabinta ta rufe har fuskarta a zuciyarta tana maimaita duk addu'ar datazo bakinya. Bata san menene ya tunkaro rayuwarta ba amma tana fatan koma menene Ubangijin daya jarabceta dashi ya bata ikon dauka.
Tundaga qofar gidan tasan ba lafiya ba, Kukan Mama da kururuwarta dake jiyowa da wasu muryoyi da bata tabbatar da masu su ba suna bata haquri nan take jikinta ya dauki rawa ta coge a qofar soron saboda wani matsanancin tsoron abinda zata tarar daya dirar mata a zuciya. Anty Bilki ce ta kama hannunta tana cewa
"Muje Hadiza Allah yana tare da me gaskiya muma kuma muna tare dake karkiji tsoron komai in sha Allahu ubangiji ze wanke ki"
"Me akace na aikata?" Ta fada cikin wata irin karyayyar murya tana kallon Anty Bilki da kwalla ke zubo mata, seta jata suka shiga gidan ba tareda ta amsa mata ba, a tsaitsaye suka tarar da Mata uku, Malama Lawisa maqociyarsu ce kuma Aminiyar Mama se Hajiya Zuwaira itama qawarta ce ta kusa da sukayi aiki tare se kuma Alhaji Sunusi Mahaifin Khausar wanda suka riqe tamkar uba.
"Yawwa gatanan, na gaya miki daman babu inda Hadiza zataje, kiyi haquri ki sauqaqawa zuciyarki Karima idan baki shaidi yarki ba waye ze bata kariya a duniyar nan" Hajiya Zuwaira ta fada tana kamo hannun Hadizan zuwa gaban Mama data yi saurin ja da baya tana cewa
"Ta fita bana son ganinta, ta fita na barwa duniya ita. Yanda kika ci mutunchinmu hadiza kika tozarta mu kema Allah yayi miki haka. Kin cucemu kin cuci Ahalinmu kije kici gaba da abinda kika zabawa kanki amma daga yau ki saka a ranki baki da uwa, ki fauka tamkar daga sama kika fadi baki da kowa ki riqe rayuwar da kika zabawa kanki ta zamar miki uwa da uba da dangi kije gaki ga duniya Hadiza".
Sulalewa tayi daga hannun Hajiya Zuwaira ta zube ta shiga jan guiwoyinta har zuwa gaban Maman dake kuka kamar ranta ze fita, cikin rawar jiki ta kai hannu zata tabata kafin ta kai ga hakan Maman ta dauketa da wani gigitaccen Mari da seda jinta ya dauke na wani lokaci kafin ta kalleta tana cewa
"Idan kika kuskura kika tabani da qazamin hannunki ban yafe ba ki kuma tashi ki fice daga gidan in har ba qarasani kike so kiyi da baqin cikin ki ba, wallahi Hadiza nayi nadamar haihuwarki. Da nasan abinda zaki jawo mun kenan dana danneki tun dana haifeki kin mutu kowa ya huta"
"Subhanallahi wai Karimatu bazaki dena jifan yarinyar nan da mugayen kalamai ba. Koma menene hannunka baya taba rubewa kayar, addu'a da neman shiriyar ubangiji ita take da buqata a yanzu ba mugayen kalaman da zasu qara tagayyara rayuwarta ba. Ke Hadiza tashi kije, kuje can gidan ki zauna karkije ko ina daga nan ina zuwa" Alhaji Sunusi ya fada cikin bacin ran abinda Maman takeyi. Tunda mugun labarin ya riske shi yana kasuwa yaji yaran shagonsa suna surutu da la'antar yarinyar har yaji daya yana fadin yar unguwarsu ce ya santa abinda yaja hankalinsa kenan har ya nemi jin ba'asin meya faru suka nuna masa.
Hankalinsa yayi masifar tashi babu shiri ya baro kasuwar ya taho gida yana zuwa Matarsa take sake jadda masa ita ma ta gani a wayar ta an tura a group Khausar bata kwana gida ba tana gidan Yayarta shiyasa bata ji gargar din maganar ba dan a cikin tashin hankali ya sameta na tsoron ko itama Khausar din irin rayuwar da takeyi kenan tunda a koda yaushe suna tare shine babu shiri ya tafi gidan su Hadizan yaje ya tarar da Isma'il ya rigada ya kwazawa Maman labarin tana ta tashin hankali abin dai babu dadi.
Anty Bilkisu ce ta kama Hadiza da sam ta gagara kuka se zare ido takeyi kwakwalwarta tamkar an wanke ta babu tunanin komai a ciki. Ta rasa gane me yake faruwa, gaba daya duk wani motsi ko magana sake jefata cikin rudani yakeyi. A bakin qofa suka ci karo da Isma'il daya bi sahun Hadiza gurin aiki aka tabbatar masa tazo ta tafi daga can ya wuce gidansa yana zuwa yaran sukace Mamansu ta fita da Anty Hadiza dalilin kiran da yayi mata kenan akan ta dawo daga can kuma ya wuce gurin wani abokinsa ya kai masa hotunan dan ya duba masa sahihancinsu saboda zuciyarsa ta kasa yarda cewar yar uwarsa Hadiza zata aikata hakan sedai ya tabbatar masa da hotunan gaskiya ne ba hadasu akayi ba wani irin rugugin tashin hankali yake ji a cikin kansa dakyar ya iya tuqo mota ya dawo gida.
Yana sako kai Soron suna saka nasu zasu fita, daga Hadiza har Bilkisu babu wadda zatace taga sanda ya iso gabansu illah mahangurbar daya kaiwa Hadizan a fuska jini yayi tsartuwa daga hancinta da bakinta da suka fashe lokaci guda, kafin tagama sanin abinda yake faruwa ya rufeta da wani irin mugun duka kamar yanda kasan ya kama Barawo, da gudu jama'ar cikin gidan suka fito amma an gagara samun wanda ze iya kwatarta a hannunsa dan duka yake kai mata ta ko ina babu ji babu gani qafa da hannu tuni qofar gidan ta cika maqil da jama'a yan kallo harda masu daukar video dan daman hotunan sun gama karada unguwa anata yamadidi masu gaskgatawa nayi harda kafa hujja ta bata kula samari wasu kuma suna ganin ba gaskiya bane ba.
Duk irin roqo da magiya dasu Alhaji Sunusi suka ringa yi masa Isma'il be dene dukan Hadiza ba seda yaga bata motsi idanunta sun qaqqafe sannan ya tsallaketa ya shiga cikin gidan Hajiya Zuwaira da Malama Lawisa suka dagota a tare suka fasa kuka suna cewa
"Ya kasheta, Isma'il kayi kisan kai"
Daga cikin gidan Mama dako gezau batayi ba kan dukan da yakeyi mata tace
"Ai gara daya kasheta dan daman hukuncinta kenan kuma ko shi be kasheta ba ni da hannuna zan miqa ta ga Kotun musulunci a yanke mata hukunci, mun huta an rage mugun iri a doron qasa" ta qarasa tana fashewa da wani irin kuka da duk wanda yaji se ta bashi tausayi. Gabanta ya durqusa shima yana kukan tamkar mace yace
"Naje Mama suntabbatar mun hotunan gaskiya ne ba hadasu akayi ba, da gaske ne Mama Hadiza Mata take nema yan uwanta shi yasa taqi tsayar da Miji tayi aure.
Kuka suke babu me rarrashin wani, acan soro kuwa haka suka kamata aka sakata a motar Alhaji Sunusi wanda dakyar aka kori mutane da suka taru suna kallo. Asibiti suka kaita, seda likitoci sukayi dagaske kafin numfashinta ya daidaita kafin sukayi mata allurar bacci saboda jininta daya hau ya samu daidaito. Sanadiyyar dukan ta samu tsagewar qashi a hannun dama da qa targade babu adadi banda fuskarta data kumbura suntum saboda duka taimakon da Allah yayi mata be sameta a ido ba. Malama Lawisa ce ta zauna da ita Hajiya zuwaira da Anty Bilkisu suka koma gida tana taraddadin hukuncin da zata fuskanta daga mijin nata itama shiyasa bata koma gidan Maman ba kaitsaye ta wuce gidanta a ranta tana tausayawa Hadiza har kuma sannan bataji daidai da kwayar zarra ta yarda da abinda ake zarginta dashi ba. Ita shaida ce akan Hadiza a ko ina kuma zata bugi qirji ta qarya ta cewar Hadizan bata aikata abinda ake tuhumarta ba.
"Hadiza kenan, nayi matuqar mamaki na kuma tabbatar da baki da kunya, ke a yanda kike har kike iya mun wa'azi da gaya mun Allah yace Annabi yace ko? Koda yake daman na zargin hakan..." Kiran waya ne ya shigo ya katse mata karatun da takeyi seta daga ganin Anty Bilkisu ce matar Yaya Isma'il.
"Duk inda kike Hadiza ki maza kizo gidan nan yanzu karki koma gidan Mama" Abinda ta fada mata kenanta kashe waya daga muryarta ta karanci zallar tashin hankalin da take ciki seta kalli me Adaidaita dake ta yan waqe waqensa tace
"Malam bi nan Darmanawa zamu koma"
"Toh Hajiya" ya bata amsa yana shiga kwanar yan Katako suka ci gabada tafiya. A qofar gidan ya ajiyeta ta bashi kudinsa ta shiga, Anty Bilkisu na tsaye bakin qofar palour ta cikin shirin fita tana hangota tace
"Allah sa baki sallami me Adaidaitan ba fita zamuyi" seta juya da sauri har ya fara tafiya ta tsaidashi ta fito suka shiga yaja. Aisami tace ya kaisu unguwar su Anty Bilkin seta raya a ranta ko ba lafiya ba.
"Bani wayarki Hadiza" ta fada seta zarota a jaka ta miqa mata daidai sannan kiran Yaya Isma'il ya shigo zata daga Bilkisunta fizge ta kashe wayar gaba daya ta saka a jakarta. Tata wayarce ta shiga ruri, ta ciro ta duba shidin ne seta riqeta a hannu har kiran ya katse wani ya dake shigowa sanann ta daga. Seda ta daidaita muryarta kafin tayi sallama muryarsa ta katseta yana cewa
"Duk inda kuka tafi ku dawo yanzu Bilkisu keda Hadiza, wallahi in har kuka dara Minti talatin baki kawota gidan Mama ba a bakin auranki kuma saki uku" yana fadar haka ya kashe Bilkisu ta kalli Hadiza data tabbatar da taji abinda Yayan nata ya fada saboda kidima bata iya magana ba se Hadizan ce ta tsaida Me Adaidaita tace su Koma Na'ibawa ya karkata Mashin yana cewa
"Ba matsala hajiya aikin kudi nakeyi ai".
"Anty Bilki ki gaya mun abinda yake faruwa dan Allah dan na fara rasa tunanina. Daga zuwana gurin aiki aka bani takaddar sallama, kin kirani babu shiri kince nazo sannan ga maganganun da Yaya ya fada menene dalilin da z kafa sharadi a bakin auranki? Meyake faruwa dani dan girman Allah ki gaya mun saboda nasan abinda zan tunkara" Hadiza ta fada tana jijjiga Bilkisu da tayi shiru kamar wadda ruwa ya cinye, kallon tausayi tabi Hadizan dashi ba tateda tace komai ba ta maida kanta tana kallon waje ganin haka ya saka itama Hadizan taja Hijabinta ta rufe har fuskarta a zuciyarta tana maimaita duk addu'ar datazo bakinya. Bata san menene ya tunkaro rayuwarta ba amma tana fatan koma menene Ubangijin daya jarabceta dashi ya bata ikon dauka.
Tundaga qofar gidan tasan ba lafiya ba, Kukan Mama da kururuwarta dake jiyowa da wasu muryoyi da bata tabbatar da masu su ba suna bata haquri nan take jikinta ya dauki rawa ta coge a qofar soron saboda wani matsanancin tsoron abinda zata tarar daya dirar mata a zuciya. Anty Bilki ce ta kama hannunta tana cewa
"Muje Hadiza Allah yana tare da me gaskiya muma kuma muna tare dake karkiji tsoron komai in sha Allahu ubangiji ze wanke ki"
"Me akace na aikata?" Ta fada cikin wata irin karyayyar murya tana kallon Anty Bilki da kwalla ke zubo mata, seta jata suka shiga gidan ba tareda ta amsa mata ba, a tsaitsaye suka tarar da Mata uku, Malama Lawisa maqociyarsu ce kuma Aminiyar Mama se Hajiya Zuwaira itama qawarta ce ta kusa da sukayi aiki tare se kuma Alhaji Sunusi Mahaifin Khausar wanda suka riqe tamkar uba.
"Yawwa gatanan, na gaya miki daman babu inda Hadiza zataje, kiyi haquri ki sauqaqawa zuciyarki Karima idan baki shaidi yarki ba waye ze bata kariya a duniyar nan" Hajiya Zuwaira ta fada tana kamo hannun Hadizan zuwa gaban Mama data yi saurin ja da baya tana cewa
"Ta fita bana son ganinta, ta fita na barwa duniya ita. Yanda kika ci mutunchinmu hadiza kika tozarta mu kema Allah yayi miki haka. Kin cucemu kin cuci Ahalinmu kije kici gaba da abinda kika zabawa kanki amma daga yau ki saka a ranki baki da uwa, ki fauka tamkar daga sama kika fadi baki da kowa ki riqe rayuwar da kika zabawa kanki ta zamar miki uwa da uba da dangi kije gaki ga duniya Hadiza".
Sulalewa tayi daga hannun Hajiya Zuwaira ta zube ta shiga jan guiwoyinta har zuwa gaban Maman dake kuka kamar ranta ze fita, cikin rawar jiki ta kai hannu zata tabata kafin ta kai ga hakan Maman ta dauketa da wani gigitaccen Mari da seda jinta ya dauke na wani lokaci kafin ta kalleta tana cewa
"Idan kika kuskura kika tabani da qazamin hannunki ban yafe ba ki kuma tashi ki fice daga gidan in har ba qarasani kike so kiyi da baqin cikin ki ba, wallahi Hadiza nayi nadamar haihuwarki. Da nasan abinda zaki jawo mun kenan dana danneki tun dana haifeki kin mutu kowa ya huta"
"Subhanallahi wai Karimatu bazaki dena jifan yarinyar nan da mugayen kalamai ba. Koma menene hannunka baya taba rubewa kayar, addu'a da neman shiriyar ubangiji ita take da buqata a yanzu ba mugayen kalaman da zasu qara tagayyara rayuwarta ba. Ke Hadiza tashi kije, kuje can gidan ki zauna karkije ko ina daga nan ina zuwa" Alhaji Sunusi ya fada cikin bacin ran abinda Maman takeyi. Tunda mugun labarin ya riske shi yana kasuwa yaji yaran shagonsa suna surutu da la'antar yarinyar har yaji daya yana fadin yar unguwarsu ce ya santa abinda yaja hankalinsa kenan har ya nemi jin ba'asin meya faru suka nuna masa.
Hankalinsa yayi masifar tashi babu shiri ya baro kasuwar ya taho gida yana zuwa Matarsa take sake jadda masa ita ma ta gani a wayar ta an tura a group Khausar bata kwana gida ba tana gidan Yayarta shiyasa bata ji gargar din maganar ba dan a cikin tashin hankali ya sameta na tsoron ko itama Khausar din irin rayuwar da takeyi kenan tunda a koda yaushe suna tare shine babu shiri ya tafi gidan su Hadizan yaje ya tarar da Isma'il ya rigada ya kwazawa Maman labarin tana ta tashin hankali abin dai babu dadi.
Anty Bilkisu ce ta kama Hadiza da sam ta gagara kuka se zare ido takeyi kwakwalwarta tamkar an wanke ta babu tunanin komai a ciki. Ta rasa gane me yake faruwa, gaba daya duk wani motsi ko magana sake jefata cikin rudani yakeyi. A bakin qofa suka ci karo da Isma'il daya bi sahun Hadiza gurin aiki aka tabbatar masa tazo ta tafi daga can ya wuce gidansa yana zuwa yaran sukace Mamansu ta fita da Anty Hadiza dalilin kiran da yayi mata kenan akan ta dawo daga can kuma ya wuce gurin wani abokinsa ya kai masa hotunan dan ya duba masa sahihancinsu saboda zuciyarsa ta kasa yarda cewar yar uwarsa Hadiza zata aikata hakan sedai ya tabbatar masa da hotunan gaskiya ne ba hadasu akayi ba wani irin rugugin tashin hankali yake ji a cikin kansa dakyar ya iya tuqo mota ya dawo gida.
Yana sako kai Soron suna saka nasu zasu fita, daga Hadiza har Bilkisu babu wadda zatace taga sanda ya iso gabansu illah mahangurbar daya kaiwa Hadizan a fuska jini yayi tsartuwa daga hancinta da bakinta da suka fashe lokaci guda, kafin tagama sanin abinda yake faruwa ya rufeta da wani irin mugun duka kamar yanda kasan ya kama Barawo, da gudu jama'ar cikin gidan suka fito amma an gagara samun wanda ze iya kwatarta a hannunsa dan duka yake kai mata ta ko ina babu ji babu gani qafa da hannu tuni qofar gidan ta cika maqil da jama'a yan kallo harda masu daukar video dan daman hotunan sun gama karada unguwa anata yamadidi masu gaskgatawa nayi harda kafa hujja ta bata kula samari wasu kuma suna ganin ba gaskiya bane ba.
Duk irin roqo da magiya dasu Alhaji Sunusi suka ringa yi masa Isma'il be dene dukan Hadiza ba seda yaga bata motsi idanunta sun qaqqafe sannan ya tsallaketa ya shiga cikin gidan Hajiya Zuwaira da Malama Lawisa suka dagota a tare suka fasa kuka suna cewa
"Ya kasheta, Isma'il kayi kisan kai"
Daga cikin gidan Mama dako gezau batayi ba kan dukan da yakeyi mata tace
"Ai gara daya kasheta dan daman hukuncinta kenan kuma ko shi be kasheta ba ni da hannuna zan miqa ta ga Kotun musulunci a yanke mata hukunci, mun huta an rage mugun iri a doron qasa" ta qarasa tana fashewa da wani irin kuka da duk wanda yaji se ta bashi tausayi. Gabanta ya durqusa shima yana kukan tamkar mace yace
"Naje Mama suntabbatar mun hotunan gaskiya ne ba hadasu akayi ba, da gaske ne Mama Hadiza Mata take nema yan uwanta shi yasa taqi tsayar da Miji tayi aure.
Kuka suke babu me rarrashin wani, acan soro kuwa haka suka kamata aka sakata a motar Alhaji Sunusi wanda dakyar aka kori mutane da suka taru suna kallo. Asibiti suka kaita, seda likitoci sukayi dagaske kafin numfashinta ya daidaita kafin sukayi mata allurar bacci saboda jininta daya hau ya samu daidaito. Sanadiyyar dukan ta samu tsagewar qashi a hannun dama da qa targade babu adadi banda fuskarta data kumbura suntum saboda duka taimakon da Allah yayi mata be sameta a ido ba. Malama Lawisa ce ta zauna da ita Hajiya zuwaira da Anty Bilkisu suka koma gida tana taraddadin hukuncin da zata fuskanta daga mijin nata itama shiyasa bata koma gidan Maman ba kaitsaye ta wuce gidanta a ranta tana tausayawa Hadiza har kuma sannan bataji daidai da kwayar zarra ta yarda da abinda ake zarginta dashi ba. Ita shaida ce akan Hadiza a ko ina kuma zata bugi qirji ta qarya ta cewar Hadizan bata aikata abinda ake tuhumarta ba.