Sashe 83
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar wata Laraba ta kirashi akan tanason magana dashi, magiyar datayi masa ta sakashi yarda su hadu a wani gurin cin abinci. Ya rigata zuwa dan ita tareda Khausar suka fita sun tsaya wani guri qarshe ma tafiya tayi ta bar Khausar din saboda yana jiranta.
"Khalil bansan me yasa kake guduna ba, baka son magana dani a waya ballantana kazo inda nake, idan nayi maka wani abun ne ka sanar dani na baka haquri dan Allah?" Hadiza ta fada kamar zatayi masa kuka.
Shiru yayi dan besan ta inda ze farayi mata bayani ba, dukda cewar be taba yi mata alqawarin aure ba a zuciyarsa kadai yake qudurta hakan sedai yasan itama lissafinta kenan tunda soyayyarsu ba soyayyace ta banzaba, suna mu'amala ne irinta wanda suke shirin gina wata rayuwa a gaba tare.
"Khalil kayi shiru kayi magana" ta sake fada, se ya qaqalo murmushi yace
"Bakiyi mun komai ba Hadiza kawai ayyuka ne suka sha kaina, sannan kinga nan akwai banbanci da snada ina Lagos, a nan idan na tashi aiki gida nake komawa gurin iyalina kinga babu dadi ace na koma gida kuma na ringa waya da wata a waje Matata ba zataji dadi ba".
Shiru tayi kafin tace
"Na sani amma a qalla ko sau daya ne ka ware lokacin da zamuyi magana duk sanda na kiraka fa uzuri kake bani, daga na aiki se kana kan hanya tuqi kakeyi kuma idan ka gama ba zaka kirani ba me yasa?"
"Hadiza, qorafi kike so ki koya kema? Na gaya miki uzurina baki yarda dani bane ko yaya" ya fada yana tsareta da ido, itama kallonsa tayi tace
"Hadiza?"
"Oh sorry Dijahna, shikenan?" Ya fada yana dage mata gira daya seta sun kuyar da kanta qasa, wato tana son Khalil da yawa, she can't wait ace ta zama matarsa".
"Yanzu ya akayi, kin ce kina son muyi magana me muhimmanci" ya katse mata tunaninta seta daga kai ta kalle shi tace
"Daman Yaya ne yayi mun magana akan ya kamata idan da gaske kakeyi ka turo da manya su shiga maganar" ta qarasa a sanyaye, Khalil dake shan ruwa be san sanda ya kware shi ba ya shiga tari duk ta rikice tana masa sannu, seda ya lafa masa kafin ya kalleta da idonsa da sukayi ja yace
"Dijah, amma bakiyiwa su Mama bayani akaina bane ba?"
"Kamar Yaya Khalil wane bayani kake so nayi musu kuma? Na fada musu wanene kai da Komai naka dana sani shine dalilin ma da Yayan yace na gaya maka ka turo dan yayi bincike a kanka kai mutumin kirki ne" Hadiza ta fada tana kallonsa. Seda ya hadiye yawun daya tarar masa a baki a ransa yana cewa
"Abinda nake gudu kenan" a fili kuma yace
"Amma baki fada masa shekarata biyu da aure ba ko?"
"Meye hadin shekarun auranka da maganar namu auran kuma?" Ta mayar masa da tambayar seya tareta da cewa
"Yana da Hadi sosai ma Hadiza, yanzu misali ace kece Matata, haka kawai babu wata matsala tsakaninmu shekara Biyu nace zan qara aure zaki yarda?
Bama Matata kadai ba hatta da iyayena nasan idan naje musu da maganar a yanzu se sun tuhumi dalilin da ya saka nake son qara auren".
"Kenan yaudarata kake yi daman ba aurene ya kawo ka gurina na?" Hadiza ta fada muryarta na rawa se Khalil yayi saurin cewa
"Wallahi Aa, Allah shine shaidata banzo gurinki da niyyar yaudara ba amma nima ki fahimceni dole ina da buqatar saita abubuwa da yawa kafin nace zan taso da maganar aure yanzu, dole ne na fara samun goyon baya daga gurin Magabatana sannan ita kanta Matata sena samu hadin kanta kafin nace zan turo da magana gidanku"
"Kenan ni kuma ina zaune ina zaman jiranka idan baka samu hadin kan nasu ba na tashi a tutar babu koh? Wallahi Khalil ka cuceni ka bata mun lokaci. Da kasan baka shirya auran ba me yasa ka shigo rayuwata har ka saka na kori kowa duk a tunanina na samu Mijin aure? Lokacin da kake cewa idan ka samu yanda kake so kafin qashen shekarar nan zakayi aure daman duk yaudara ce ko kuma akwai wadda kake nema bayan ni ni bata mun lokaci kawai kakeyi? Hadiza ta fada cikin Kuka tana miqewa tsaye se shima ya miqe ganin hankalin mutane ya fara dawowa kansu.
"Kiyi haquri Ki zauna kinga mutane suna kallonmu karsu dauka wani abin nayi miki" ya fada cikin lallashi seta zabura tace
"Su kalle mu mana kuma ai wani abun kayi mun yaudarata kayi ka ha'ince ni" ta fada cikin daga sauti kafin ta figi jakarta tana cewa
"Bazan yafe maka ciwon son daka jefani a ciki ba, in sha Allahu kaima se Allah ya jarabceka da son wata kuma ta wahalar dakai"
miqewa yayi ganin ta fara tafiya ya sha gabanta yana cewa
"Haba Hadiza ya zaki yimun Allah ya isa ki tsaya muyi magana nifa ba cewa nayi bazan aureki ba lokaci nace ki bani na samu na daidaita abubuwa"
"Ka matsa mun na wuce Khalil" Hadizan ta fada yanda tayi maganar se yaga kamar ba'a hayyacinta take ba, dafe qirjinta da yaga tayi ya sakashi tunawa da tana da Ciwon qirji kuma damuwa ce take tayar mata dashi ta gaya masa, qoqarin yi mata magana yakeyi amma taqi tsayawa so kawai take ya bata guri ta wuce, ganin da yayi tana layi kamar zata fadi ya sakashi riqota yana cewa
"Ki nutsu kinga zaki fadi muje mota dan Allah ki nutsu badai maganar na turo bane zan turo ina sonki zan aureki Hadiza". Tallafeta yayi a jikinsa har suka qarasa jikin motar sa ya bude gaba ya sakata seda ta zauna dakyau ya kulle qofar ya zagaya mazauninsa. Da qarfi qirjinsa ya buga ganin wani Saurayi fuskarsa sanye da Facemask dab dasu ya daga wayasa kamar meyin video, sakin murfin motar yayi ya nufeshi sedai saurayin na ganinsa ya juya da sauri ya bar gurin nan take ya bace masa.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 36
Motar ya koma yana tunanin wanene wannan din kuma me yake dauka? Ganin bashi da me bashi amsa ya saka ya mayar da hankalinsa kan tuqin da yakeyi yana yi yana lallashin Hadiza dake kuka, har qofar gidansu ya kaita, be barta ta fita ba seda ya tabbatar ta sakko kuma ta dena kukan da takeyi ya lallabeta ya kuma tabbatar mata da In sha Allahu ze aureta amma tayi haquri ta bashi lokaci kuma ta ringa musu Addu'a.
"Ina son Matata sosai bansan ta yanda zan kalleta nace mata zan qara aure ba" ya fada yana kallon Hadizan ta buga masa wata harara tareda jan tsaki kafin ta kama murfin motar ta fice batareda ta tanka masa ba ya rakata da Murmushi, haega Allah yana son Hadiza kodan sanyin Halinta da kulawar da take bashi kuma tafi sonsa akan wanda yake mata yasan zata riritashi ta kiyaye bacin ransa to amma damuwar ta inda ze tunkari ita Uwargidan da wannan magana dan ta Hajiya da duk wani da ze iya kawo cikas me sauqi ne.
Gaba ya danyi ya bar qofar gidan nasu ya samu guri ya tsaya. Jalila ya kira ringing biyu ta daga tana cewa
"Aa Hussaina yau ka tuna dani kenan"
"Dama na taba cewa na manta dake ne?" Ya bata amsa se tayi yar dariya tace
"Toh ai muj sallamawa Maman Mu'ayyad kai, ta tsare gaba ta tsare baya Hajiya kadai ake bawa damar ganinka da magana dakai sanda taso mu kuwa idan mun gaji da neman ka sedai mu kirata mu bada saqo"
"Kina da Matsala Jalila yanzu duk meya kawo wannan qorafin" ya katseta, seta sake cewa
"Gaskiya ce kawai ba qorafi ba gaba daya ka maqalewa Mace baka da lokacin kowa yanzu se nata duk sunkasa fasa maka ne ni kasan bazanyi shiru ba"
Qaramin tsaki yaja yace
"Mutum na cikin wata damuwar zaki zo ki qara masa, kiranki nayi ki bani shawara amma zaki cikamun kunne da mita haba" yanda yayi maganar cikin alamun abu na damunsa ya sakata sassauta murya tace
"Yi haquri toh dan qanina meya faru, wace damuwa kake ciki kuma shawarar me zamuyi?"
"Aure nake so na qara Jalila" ya bata amsa kaitsaye dan bayaso aja maganar se tayi shiru kusan minti daya kafin ta numfasa tace
"Aure Khalil, ka gayawa Hajiya kuma ta yarda?"
"Ban gayawa kowa ba shawararki nake nema me kike gani akai nayi ko Aa?" Ya mayar mata da wata tambayar se Jalila ta ajiye numfashi tace
"Wannan ai ba maganar da kai tsaye zance maka yi ko karkayi bace. Qarin aure yana zuwa ne akan abu biyu, buqatuwar yin hakan ko kuma yazo maka baqatatan daga Allah dukda dukka biyun nufin Allah ne amma kashin farko da niyya kuma mutum yaso yin hakan kai wannene naka a ciki?"
"Nima ban sani ba" bata amsa kamar me shirin fasa kuka, baya so Hadiza ta zarge shi da laifin yaudara dukda wani mummunan abu be taba shiga tsakaninsu ba ze iya cewa ko hannunta be taba ba sedai bisa kuskure amma dukda haka bazeso haqqin Soyayyar da takeyi mishi ya kamashi ba kuma tsoron sa Allah tsoronsa yanda ze tunkari Umaimah musamman da yanzu suke zaune lafiya babu wata matsala a tsakaninsu. Dariyar Jalila ce ta dawo dashi hayyacinsa yaji tana cewa
"Dan qanina maganar nan bata waya bace, ka samu lokaci kazo mu tattauna in fahimceka kafin nasan abin da zan baka shawara akai"
Yayi Na'am da shawararta dan haka yace mata
"Shikenan zanzo, amma dan Allah kar wanda yasan wannan maganar ko da Hajiya ce na gaya miki ban sanar da kowa ba seke, ba kuma naso suji se na gama yanke shawarar yi ko akasin haka"
"Khalil bansan me yasa kake guduna ba, baka son magana dani a waya ballantana kazo inda nake, idan nayi maka wani abun ne ka sanar dani na baka haquri dan Allah?" Hadiza ta fada kamar zatayi masa kuka.
Shiru yayi dan besan ta inda ze farayi mata bayani ba, dukda cewar be taba yi mata alqawarin aure ba a zuciyarsa kadai yake qudurta hakan sedai yasan itama lissafinta kenan tunda soyayyarsu ba soyayyace ta banzaba, suna mu'amala ne irinta wanda suke shirin gina wata rayuwa a gaba tare.
"Khalil kayi shiru kayi magana" ta sake fada, se ya qaqalo murmushi yace
"Bakiyi mun komai ba Hadiza kawai ayyuka ne suka sha kaina, sannan kinga nan akwai banbanci da snada ina Lagos, a nan idan na tashi aiki gida nake komawa gurin iyalina kinga babu dadi ace na koma gida kuma na ringa waya da wata a waje Matata ba zataji dadi ba".
Shiru tayi kafin tace
"Na sani amma a qalla ko sau daya ne ka ware lokacin da zamuyi magana duk sanda na kiraka fa uzuri kake bani, daga na aiki se kana kan hanya tuqi kakeyi kuma idan ka gama ba zaka kirani ba me yasa?"
"Hadiza, qorafi kike so ki koya kema? Na gaya miki uzurina baki yarda dani bane ko yaya" ya fada yana tsareta da ido, itama kallonsa tayi tace
"Hadiza?"
"Oh sorry Dijahna, shikenan?" Ya fada yana dage mata gira daya seta sun kuyar da kanta qasa, wato tana son Khalil da yawa, she can't wait ace ta zama matarsa".
"Yanzu ya akayi, kin ce kina son muyi magana me muhimmanci" ya katse mata tunaninta seta daga kai ta kalle shi tace
"Daman Yaya ne yayi mun magana akan ya kamata idan da gaske kakeyi ka turo da manya su shiga maganar" ta qarasa a sanyaye, Khalil dake shan ruwa be san sanda ya kware shi ba ya shiga tari duk ta rikice tana masa sannu, seda ya lafa masa kafin ya kalleta da idonsa da sukayi ja yace
"Dijah, amma bakiyiwa su Mama bayani akaina bane ba?"
"Kamar Yaya Khalil wane bayani kake so nayi musu kuma? Na fada musu wanene kai da Komai naka dana sani shine dalilin ma da Yayan yace na gaya maka ka turo dan yayi bincike a kanka kai mutumin kirki ne" Hadiza ta fada tana kallonsa. Seda ya hadiye yawun daya tarar masa a baki a ransa yana cewa
"Abinda nake gudu kenan" a fili kuma yace
"Amma baki fada masa shekarata biyu da aure ba ko?"
"Meye hadin shekarun auranka da maganar namu auran kuma?" Ta mayar masa da tambayar seya tareta da cewa
"Yana da Hadi sosai ma Hadiza, yanzu misali ace kece Matata, haka kawai babu wata matsala tsakaninmu shekara Biyu nace zan qara aure zaki yarda?
Bama Matata kadai ba hatta da iyayena nasan idan naje musu da maganar a yanzu se sun tuhumi dalilin da ya saka nake son qara auren".
"Kenan yaudarata kake yi daman ba aurene ya kawo ka gurina na?" Hadiza ta fada muryarta na rawa se Khalil yayi saurin cewa
"Wallahi Aa, Allah shine shaidata banzo gurinki da niyyar yaudara ba amma nima ki fahimceni dole ina da buqatar saita abubuwa da yawa kafin nace zan taso da maganar aure yanzu, dole ne na fara samun goyon baya daga gurin Magabatana sannan ita kanta Matata sena samu hadin kanta kafin nace zan turo da magana gidanku"
"Kenan ni kuma ina zaune ina zaman jiranka idan baka samu hadin kan nasu ba na tashi a tutar babu koh? Wallahi Khalil ka cuceni ka bata mun lokaci. Da kasan baka shirya auran ba me yasa ka shigo rayuwata har ka saka na kori kowa duk a tunanina na samu Mijin aure? Lokacin da kake cewa idan ka samu yanda kake so kafin qashen shekarar nan zakayi aure daman duk yaudara ce ko kuma akwai wadda kake nema bayan ni ni bata mun lokaci kawai kakeyi? Hadiza ta fada cikin Kuka tana miqewa tsaye se shima ya miqe ganin hankalin mutane ya fara dawowa kansu.
"Kiyi haquri Ki zauna kinga mutane suna kallonmu karsu dauka wani abin nayi miki" ya fada cikin lallashi seta zabura tace
"Su kalle mu mana kuma ai wani abun kayi mun yaudarata kayi ka ha'ince ni" ta fada cikin daga sauti kafin ta figi jakarta tana cewa
"Bazan yafe maka ciwon son daka jefani a ciki ba, in sha Allahu kaima se Allah ya jarabceka da son wata kuma ta wahalar dakai"
miqewa yayi ganin ta fara tafiya ya sha gabanta yana cewa
"Haba Hadiza ya zaki yimun Allah ya isa ki tsaya muyi magana nifa ba cewa nayi bazan aureki ba lokaci nace ki bani na samu na daidaita abubuwa"
"Ka matsa mun na wuce Khalil" Hadizan ta fada yanda tayi maganar se yaga kamar ba'a hayyacinta take ba, dafe qirjinta da yaga tayi ya sakashi tunawa da tana da Ciwon qirji kuma damuwa ce take tayar mata dashi ta gaya masa, qoqarin yi mata magana yakeyi amma taqi tsayawa so kawai take ya bata guri ta wuce, ganin da yayi tana layi kamar zata fadi ya sakashi riqota yana cewa
"Ki nutsu kinga zaki fadi muje mota dan Allah ki nutsu badai maganar na turo bane zan turo ina sonki zan aureki Hadiza". Tallafeta yayi a jikinsa har suka qarasa jikin motar sa ya bude gaba ya sakata seda ta zauna dakyau ya kulle qofar ya zagaya mazauninsa. Da qarfi qirjinsa ya buga ganin wani Saurayi fuskarsa sanye da Facemask dab dasu ya daga wayasa kamar meyin video, sakin murfin motar yayi ya nufeshi sedai saurayin na ganinsa ya juya da sauri ya bar gurin nan take ya bace masa.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 36
Motar ya koma yana tunanin wanene wannan din kuma me yake dauka? Ganin bashi da me bashi amsa ya saka ya mayar da hankalinsa kan tuqin da yakeyi yana yi yana lallashin Hadiza dake kuka, har qofar gidansu ya kaita, be barta ta fita ba seda ya tabbatar ta sakko kuma ta dena kukan da takeyi ya lallabeta ya kuma tabbatar mata da In sha Allahu ze aureta amma tayi haquri ta bashi lokaci kuma ta ringa musu Addu'a.
"Ina son Matata sosai bansan ta yanda zan kalleta nace mata zan qara aure ba" ya fada yana kallon Hadizan ta buga masa wata harara tareda jan tsaki kafin ta kama murfin motar ta fice batareda ta tanka masa ba ya rakata da Murmushi, haega Allah yana son Hadiza kodan sanyin Halinta da kulawar da take bashi kuma tafi sonsa akan wanda yake mata yasan zata riritashi ta kiyaye bacin ransa to amma damuwar ta inda ze tunkari ita Uwargidan da wannan magana dan ta Hajiya da duk wani da ze iya kawo cikas me sauqi ne.
Gaba ya danyi ya bar qofar gidan nasu ya samu guri ya tsaya. Jalila ya kira ringing biyu ta daga tana cewa
"Aa Hussaina yau ka tuna dani kenan"
"Dama na taba cewa na manta dake ne?" Ya bata amsa se tayi yar dariya tace
"Toh ai muj sallamawa Maman Mu'ayyad kai, ta tsare gaba ta tsare baya Hajiya kadai ake bawa damar ganinka da magana dakai sanda taso mu kuwa idan mun gaji da neman ka sedai mu kirata mu bada saqo"
"Kina da Matsala Jalila yanzu duk meya kawo wannan qorafin" ya katseta, seta sake cewa
"Gaskiya ce kawai ba qorafi ba gaba daya ka maqalewa Mace baka da lokacin kowa yanzu se nata duk sunkasa fasa maka ne ni kasan bazanyi shiru ba"
Qaramin tsaki yaja yace
"Mutum na cikin wata damuwar zaki zo ki qara masa, kiranki nayi ki bani shawara amma zaki cikamun kunne da mita haba" yanda yayi maganar cikin alamun abu na damunsa ya sakata sassauta murya tace
"Yi haquri toh dan qanina meya faru, wace damuwa kake ciki kuma shawarar me zamuyi?"
"Aure nake so na qara Jalila" ya bata amsa kaitsaye dan bayaso aja maganar se tayi shiru kusan minti daya kafin ta numfasa tace
"Aure Khalil, ka gayawa Hajiya kuma ta yarda?"
"Ban gayawa kowa ba shawararki nake nema me kike gani akai nayi ko Aa?" Ya mayar mata da wata tambayar se Jalila ta ajiye numfashi tace
"Wannan ai ba maganar da kai tsaye zance maka yi ko karkayi bace. Qarin aure yana zuwa ne akan abu biyu, buqatuwar yin hakan ko kuma yazo maka baqatatan daga Allah dukda dukka biyun nufin Allah ne amma kashin farko da niyya kuma mutum yaso yin hakan kai wannene naka a ciki?"
"Nima ban sani ba" bata amsa kamar me shirin fasa kuka, baya so Hadiza ta zarge shi da laifin yaudara dukda wani mummunan abu be taba shiga tsakaninsu ba ze iya cewa ko hannunta be taba ba sedai bisa kuskure amma dukda haka bazeso haqqin Soyayyar da takeyi mishi ya kamashi ba kuma tsoron sa Allah tsoronsa yanda ze tunkari Umaimah musamman da yanzu suke zaune lafiya babu wata matsala a tsakaninsu. Dariyar Jalila ce ta dawo dashi hayyacinsa yaji tana cewa
"Dan qanina maganar nan bata waya bace, ka samu lokaci kazo mu tattauna in fahimceka kafin nasan abin da zan baka shawara akai"
Yayi Na'am da shawararta dan haka yace mata
"Shikenan zanzo, amma dan Allah kar wanda yasan wannan maganar ko da Hajiya ce na gaya miki ban sanar da kowa ba seke, ba kuma naso suji se na gama yanke shawarar yi ko akasin haka"