Sashe 238
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Guraren qarfe biyu Driver su Bibi ya kirashi, bayan ya daga yake ce masa
"Alhaji, me sunan Hajiya ce gata nan tana ta kuka harda birgima a qasa nayi nayi ta shiga mota mu tafi taqi hatta da Malam sunyi banbaki amma ta kafe ba zata shiga ba" Khalil ya dafa kansa yana jinjina rigimar Bibi dan haka yace ya bata wayar tana karba kuwa ta fasa masa kuka me hade da ihu taqi cewa komai
"Me akayi miki kike kuka har kina birgima a qasa?" Ya tambayeta seta tsagaita kukan dukda haka murya na sarqewa tace masa
"Tun jiya na tambayeka yau zamuje gurin Momy kace toh na gaya masa shine yace shi baka gaya masa baze kaimu ba ni kuma in dai ba gurin Momy ze kaimu ba bazan hau motar ba" ta qarasa tana sake fashewa da wani ihun da seda ya janye wayar daga kunnensa. Lallashinta ya shigayi akan ta bari su fara zuwa gida idan yaso sukayi wanka se a kaisu amma taqi daga qarshe ma ta yarda wayar dan yana jin tsawar da wani ya mata yana cewa
"Akan me zaki jefar masa da waya idanta fashe fa?"
Manniru Driver ya dauki wayarsa a qasa cikin qunar rai ganin Khalil din be kashe ba ya sakashi cewa
"Ranka ya dade jefar da wayar tayi"
"Ka kaisu Manniru amma ba ajiyesu zakayi ba ka jira su shiga su fito idan kun kusa qarasawa ka kirani a waya zan musu magana" Khalil ya fada a hankali daga nan ya kashe wayar zuciyarsa duk babu dadi, sam baya son damuwar yaransa amma fitinar Bibi kullum qara yawa takeyi tunda aka fara kaisu gidansu Umaimah yanzu basa sati biyu bata saka rigimar se sunje ba dukda basa kwana sedai au yini su dawo dan wani lokacin ma ita kadai ake kaiwa Mu'ayyad ya kance ai munje ranar nan Iman kuwa daman ko a jikinta saboda yan uwan take zuwa amma ita tana da bala'in qulafucin uwar ga dan banzan naci idanta fara roqon akaisu harse ya yarda zata barshi ya sarara ko jiyan nacin ta ringa masa ya amsa mata badan da gaske yake ba dan basuyi cikakken sati da zuwa ba ashe ita ta riqe shine taje tana creating scene a makaranta ze koma gida zasu hadu ne.
UMAIMAH
Kuka takeyi haiqan kamar ranta ze fita Abba ya zuba mata ido yana sauraronta ba tareda yace mata komai ba, seda ta haqurtar da kanta ta tsagaita kukan kafin taci gaba da cewa
"Na sani na tafka babban kuskure a rayuwata kuma kunada duk wani dalili na daukar ko wanne mataki a kaina. Na biyewa zuciya da zugar mugayen mutane na watsa muku qasa a ido na zubar muku da mutunchi a idon duniya Allah shine shaidata nayi nadamar abinda na aikata kuma a shirye nake dana gyara kuskurena hakan kuma baze yuwu ba har se na fita daga fushinku, Abba dan girman Allah dan Darajar Ma'aikin Allah ku dubi rauni na ku yake mun laifin dana aikata muku. Ku sassauta fushin ku akaina ko na samu ubangiji ya dubeni ya yafemun sauran laifukan dana aikata tsakani na dashi.
Wallahi nayi nadama nayi dana sani biyewa son rai" ta sake rushewa da wani kukan daya fi na farko ganin Abban na zaune still ko gezau a kallonta kawai yakeyi kamar wata talabijin. Sunkwashe kusan minti goma sha biyar a haka tana kukan kafin Abban ya nisa yace
"Toh ni abinda ban gane ba ni menene nawa a ciki Umaimah da kikazo kina bani haquri sannan duk tsahon lokacin nan se yanzu ne kikaga mun isa da ki bamu haquri ko me me kike buqata?"
Se tayi saurin tsayar da kukan tana cewa
"Wlh Abba badan baku isa bane a kullum nauyi da kunyar yanda zan tunkareku bayan duk abubuwan dana aikata a bayane ya hanani gurfana gabanku na nemi yafiyarku amma yanzu na gane bani da wata mafita domin fushinku a kullum qara dagulamun lissafi yakeyi. Abba kuyi haquri ku yafe wlh nayi nadama kuma in sha Allahu zan gyara kuskurena".
"Toh Alhamdulillahi dama abinda ake so da mumini idan yayi kuskure ya gane ya tuba ya kuma guji sake maimaita kuskuren a gaba idan har dagske kikeyi kinyi sahihin tuba ina fatan Allah ya shiga Al'amuranki Umaimah ya duba miki ya rabaki da duk wani abu dayake ingizaki ga sabon Allah ya rangwanta miki zafin zuciyarki dake kaiki ga aikin dana sani. A bangarena na dade da yafe miki, domin da banyi miki afuwa ba da baki samu yancin zama a cikin gidan nan ba zan sallawa duniya kene kamar yanda kika dade da sallama mata kanki amma bamyi hakan ba mun rungumeki a kullum kuma muna miki fatan shiriya
Sannan maganar Yafiya da akwai wadanda yafi kamata da ki nemi yafiyarsu bayan mu, idan har dagske kinyi nadama ki nemi yafiyar ubangiji a farko kan sabawar da kika masa sannanki nemi yafiyar wadanda kika zalunta domin kinsan ubangiji baya yafe haqqin bawa da dan uwansa bawa ya dauka dan haka in har kina so kiga daidai Umaimah dole sekin sauke haqqin wadanda kika dauka" Abba yayi maganar cikin nutsuwa.
Umaimah taja majina kafin tace
"Nagode Abba kuma in sha Allahu bazan sake komawa ga abinda na aikata a baya ba ku tayani da addu'a"
"Allah yayi miki Albarka ya shiga cikin lamuranki, shikenan zan iya tafiya?" Abban ya sake fada dan yana shirin fita tayi masa dirar mikiya tana shiga kuma ta fasa masa kuka, saurin girgiza kai Umaimah tayi kafin tace
"Aa Abba bashi kenan ba dan Allah Abba zaka tayani roqan Mama"
"Ni yanzu waya tayaki roqona?" Ya fada yana kallonta seta marairaice tace
"Abba kai da sauqi amma Mama fushinta ya zarce naka wlh na rasa ta yanda zan tunkareta Abba ko dakinta bata bari na shiga duk yanda kuma naso nayi mata maganar seta nunamun ita ban mata komai ha kaga kenan ta qullaceni da yawa".
Shiru Abban yayi kafin yace
"Shikenan kiyi ta qoqarin kyautata mata kuma karki dena bata haqurin har se sanda ta sakko ta saurareki abinda kika aikata Umaimah dole badan mu muka haifeki ba babu yanda zamuyi dake da tuni wata maganar akeyi yanzu dan kinyi mana cin fuskar da badan zuciyar musulunci ha da sanin tasirin da bakinmu da fushinmu zeyi akanki dole muka taushi zukatanmu amma ya wuce tunda har kin gene kuskurenki kin nemi afuwa nayi miki itama kuma nasan zata sakko a hankali in sha Allahu"
"Nagode Abba Allah ya saka da Alkhairi ya qara girma" ta fada cikin murnar samun daidaito da Mahaifinta ya amsa mata da
"Amin, Allah yayi muku Albarka keda sauran yan uwanku Ubangiji ya dubeku ya tsare ku daga dukkan sharri" ya fada yana dafa kanta. Tare suka fito daga dakin, Mama da Anty na tsakar gidan a tare suka musu kallo daya suka dauke kai Abba ya yi murmushi yana kallonsu yace
"Zan fita" suka hada baki gurin yi masa a dawo lafiya Umaimah ma tayi masa bakinta yaqi rufuwa saboda farin cikin da take ciki seda Abban ya fita kafin ta matsa inda Mama take ta durqusa gabanta tace
"Mamame za'a dafa da rana?"
"Girkin Antyn kune ai banawa ba" Maman ta bata amsa seta juya ta kalli Anty data dauke kai ta hade fuska tun fitowarsu da Abban kafinma tayi mata magana tace
"Ki barshi zanyi da kaina ai naga kun shirya da Abban naki".
Yanda tayi maganar seta bawa Mama da Umaiman mamaki har seda Mama ta kasa daurewa tace
"Kamar yaya zakiyi da kanki saratu ba doka Alhaji ya kafa cewar ita zatayi aikin gidan nan ba ko kunyi dashi yace miki ya janye ki karbi aikinki?" Seta kalli Maman bayan data miqe tsaye tace
"Aa kawai dai zan karbi aikina tunda har sun fara shiga daki su fito suna dariya kinga alama tana nuna gwamnatinta ta dawo kenan gara na karbi aikina da kaina kafin a maidomun tunda daman bani nace a karba ba" ta shige dakinta Mama ta bita da kallo dan sam bata fahimci abinda Antyn take nufi ba mema ya bata mata rai yanzu yanzu bayan hira sukeyi cikin nishadi daga fitowar Alhaji da Umaimah seta canza fuska me yake faruwane?
Ita dai Umaimah na zaune ta sunkuyar da kai Mama ta kalleta tace
"Kinji abinda tace ai se ki wuce inda wani abinda zakiyi kiyi"
"Babu abinda zanyi yanzu sedai ko in akwai Aikin da zanyi miki" Umaiman ta fada cikin ladabi, Mama ta girgiza mata kai alamar babu seta narke fuska kalar tausayi tace
"Jiya naga an kawo miki kayan wanki tunda akwai wuta sena goge miki".
Bata zata Maman zata amsa ba taji tace
"Toh, amma kiyi a hankali karki qona mun kaya nasanki ba iya guga kikayi ba" seta miqe cike da murna tana cewa
"Bazan qona ba In sha Allah" ta shige dakin Maman.
"Alhaji, me sunan Hajiya ce gata nan tana ta kuka harda birgima a qasa nayi nayi ta shiga mota mu tafi taqi hatta da Malam sunyi banbaki amma ta kafe ba zata shiga ba" Khalil ya dafa kansa yana jinjina rigimar Bibi dan haka yace ya bata wayar tana karba kuwa ta fasa masa kuka me hade da ihu taqi cewa komai
"Me akayi miki kike kuka har kina birgima a qasa?" Ya tambayeta seta tsagaita kukan dukda haka murya na sarqewa tace masa
"Tun jiya na tambayeka yau zamuje gurin Momy kace toh na gaya masa shine yace shi baka gaya masa baze kaimu ba ni kuma in dai ba gurin Momy ze kaimu ba bazan hau motar ba" ta qarasa tana sake fashewa da wani ihun da seda ya janye wayar daga kunnensa. Lallashinta ya shigayi akan ta bari su fara zuwa gida idan yaso sukayi wanka se a kaisu amma taqi daga qarshe ma ta yarda wayar dan yana jin tsawar da wani ya mata yana cewa
"Akan me zaki jefar masa da waya idanta fashe fa?"
Manniru Driver ya dauki wayarsa a qasa cikin qunar rai ganin Khalil din be kashe ba ya sakashi cewa
"Ranka ya dade jefar da wayar tayi"
"Ka kaisu Manniru amma ba ajiyesu zakayi ba ka jira su shiga su fito idan kun kusa qarasawa ka kirani a waya zan musu magana" Khalil ya fada a hankali daga nan ya kashe wayar zuciyarsa duk babu dadi, sam baya son damuwar yaransa amma fitinar Bibi kullum qara yawa takeyi tunda aka fara kaisu gidansu Umaimah yanzu basa sati biyu bata saka rigimar se sunje ba dukda basa kwana sedai au yini su dawo dan wani lokacin ma ita kadai ake kaiwa Mu'ayyad ya kance ai munje ranar nan Iman kuwa daman ko a jikinta saboda yan uwan take zuwa amma ita tana da bala'in qulafucin uwar ga dan banzan naci idanta fara roqon akaisu harse ya yarda zata barshi ya sarara ko jiyan nacin ta ringa masa ya amsa mata badan da gaske yake ba dan basuyi cikakken sati da zuwa ba ashe ita ta riqe shine taje tana creating scene a makaranta ze koma gida zasu hadu ne.
UMAIMAH
Kuka takeyi haiqan kamar ranta ze fita Abba ya zuba mata ido yana sauraronta ba tareda yace mata komai ba, seda ta haqurtar da kanta ta tsagaita kukan kafin taci gaba da cewa
"Na sani na tafka babban kuskure a rayuwata kuma kunada duk wani dalili na daukar ko wanne mataki a kaina. Na biyewa zuciya da zugar mugayen mutane na watsa muku qasa a ido na zubar muku da mutunchi a idon duniya Allah shine shaidata nayi nadamar abinda na aikata kuma a shirye nake dana gyara kuskurena hakan kuma baze yuwu ba har se na fita daga fushinku, Abba dan girman Allah dan Darajar Ma'aikin Allah ku dubi rauni na ku yake mun laifin dana aikata muku. Ku sassauta fushin ku akaina ko na samu ubangiji ya dubeni ya yafemun sauran laifukan dana aikata tsakani na dashi.
Wallahi nayi nadama nayi dana sani biyewa son rai" ta sake rushewa da wani kukan daya fi na farko ganin Abban na zaune still ko gezau a kallonta kawai yakeyi kamar wata talabijin. Sunkwashe kusan minti goma sha biyar a haka tana kukan kafin Abban ya nisa yace
"Toh ni abinda ban gane ba ni menene nawa a ciki Umaimah da kikazo kina bani haquri sannan duk tsahon lokacin nan se yanzu ne kikaga mun isa da ki bamu haquri ko me me kike buqata?"
Se tayi saurin tsayar da kukan tana cewa
"Wlh Abba badan baku isa bane a kullum nauyi da kunyar yanda zan tunkareku bayan duk abubuwan dana aikata a bayane ya hanani gurfana gabanku na nemi yafiyarku amma yanzu na gane bani da wata mafita domin fushinku a kullum qara dagulamun lissafi yakeyi. Abba kuyi haquri ku yafe wlh nayi nadama kuma in sha Allahu zan gyara kuskurena".
"Toh Alhamdulillahi dama abinda ake so da mumini idan yayi kuskure ya gane ya tuba ya kuma guji sake maimaita kuskuren a gaba idan har dagske kikeyi kinyi sahihin tuba ina fatan Allah ya shiga Al'amuranki Umaimah ya duba miki ya rabaki da duk wani abu dayake ingizaki ga sabon Allah ya rangwanta miki zafin zuciyarki dake kaiki ga aikin dana sani. A bangarena na dade da yafe miki, domin da banyi miki afuwa ba da baki samu yancin zama a cikin gidan nan ba zan sallawa duniya kene kamar yanda kika dade da sallama mata kanki amma bamyi hakan ba mun rungumeki a kullum kuma muna miki fatan shiriya
Sannan maganar Yafiya da akwai wadanda yafi kamata da ki nemi yafiyarsu bayan mu, idan har dagske kinyi nadama ki nemi yafiyar ubangiji a farko kan sabawar da kika masa sannanki nemi yafiyar wadanda kika zalunta domin kinsan ubangiji baya yafe haqqin bawa da dan uwansa bawa ya dauka dan haka in har kina so kiga daidai Umaimah dole sekin sauke haqqin wadanda kika dauka" Abba yayi maganar cikin nutsuwa.
Umaimah taja majina kafin tace
"Nagode Abba kuma in sha Allahu bazan sake komawa ga abinda na aikata a baya ba ku tayani da addu'a"
"Allah yayi miki Albarka ya shiga cikin lamuranki, shikenan zan iya tafiya?" Abban ya sake fada dan yana shirin fita tayi masa dirar mikiya tana shiga kuma ta fasa masa kuka, saurin girgiza kai Umaimah tayi kafin tace
"Aa Abba bashi kenan ba dan Allah Abba zaka tayani roqan Mama"
"Ni yanzu waya tayaki roqona?" Ya fada yana kallonta seta marairaice tace
"Abba kai da sauqi amma Mama fushinta ya zarce naka wlh na rasa ta yanda zan tunkareta Abba ko dakinta bata bari na shiga duk yanda kuma naso nayi mata maganar seta nunamun ita ban mata komai ha kaga kenan ta qullaceni da yawa".
Shiru Abban yayi kafin yace
"Shikenan kiyi ta qoqarin kyautata mata kuma karki dena bata haqurin har se sanda ta sakko ta saurareki abinda kika aikata Umaimah dole badan mu muka haifeki ba babu yanda zamuyi dake da tuni wata maganar akeyi yanzu dan kinyi mana cin fuskar da badan zuciyar musulunci ha da sanin tasirin da bakinmu da fushinmu zeyi akanki dole muka taushi zukatanmu amma ya wuce tunda har kin gene kuskurenki kin nemi afuwa nayi miki itama kuma nasan zata sakko a hankali in sha Allahu"
"Nagode Abba Allah ya saka da Alkhairi ya qara girma" ta fada cikin murnar samun daidaito da Mahaifinta ya amsa mata da
"Amin, Allah yayi muku Albarka keda sauran yan uwanku Ubangiji ya dubeku ya tsare ku daga dukkan sharri" ya fada yana dafa kanta. Tare suka fito daga dakin, Mama da Anty na tsakar gidan a tare suka musu kallo daya suka dauke kai Abba ya yi murmushi yana kallonsu yace
"Zan fita" suka hada baki gurin yi masa a dawo lafiya Umaimah ma tayi masa bakinta yaqi rufuwa saboda farin cikin da take ciki seda Abban ya fita kafin ta matsa inda Mama take ta durqusa gabanta tace
"Mamame za'a dafa da rana?"
"Girkin Antyn kune ai banawa ba" Maman ta bata amsa seta juya ta kalli Anty data dauke kai ta hade fuska tun fitowarsu da Abban kafinma tayi mata magana tace
"Ki barshi zanyi da kaina ai naga kun shirya da Abban naki".
Yanda tayi maganar seta bawa Mama da Umaiman mamaki har seda Mama ta kasa daurewa tace
"Kamar yaya zakiyi da kanki saratu ba doka Alhaji ya kafa cewar ita zatayi aikin gidan nan ba ko kunyi dashi yace miki ya janye ki karbi aikinki?" Seta kalli Maman bayan data miqe tsaye tace
"Aa kawai dai zan karbi aikina tunda har sun fara shiga daki su fito suna dariya kinga alama tana nuna gwamnatinta ta dawo kenan gara na karbi aikina da kaina kafin a maidomun tunda daman bani nace a karba ba" ta shige dakinta Mama ta bita da kallo dan sam bata fahimci abinda Antyn take nufi ba mema ya bata mata rai yanzu yanzu bayan hira sukeyi cikin nishadi daga fitowar Alhaji da Umaimah seta canza fuska me yake faruwane?
Ita dai Umaimah na zaune ta sunkuyar da kai Mama ta kalleta tace
"Kinji abinda tace ai se ki wuce inda wani abinda zakiyi kiyi"
"Babu abinda zanyi yanzu sedai ko in akwai Aikin da zanyi miki" Umaiman ta fada cikin ladabi, Mama ta girgiza mata kai alamar babu seta narke fuska kalar tausayi tace
"Jiya naga an kawo miki kayan wanki tunda akwai wuta sena goge miki".
Bata zata Maman zata amsa ba taji tace
"Toh, amma kiyi a hankali karki qona mun kaya nasanki ba iya guga kikayi ba" seta miqe cike da murna tana cewa
"Bazan qona ba In sha Allah" ta shige dakin Maman.