Sashe 184
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bibbiyu yake gani da haka ya ringa dafa bango har ya haye sama a nan kan carpet ya kwanta yana dafe da kansa daya sara masa yana hawa saman. Ya rasa abinda yasa a kwanakin yake jin haka kwana yakeyi da ciwon kai ga wano baccin Asara daya sameshi daya rasa kona magani da menene baya sanin sanda yake daukarsa duk kuma yanda yayi ya yakice shi kasawa yake yi balle har ya samu damar tashi yayi Nafila cikin dare Sallar Asuba kanta kwana ukun nan a makare yakeyi amma ya ta'allaqa hakan da rashin kwnanciyar hankali da yake ciki a kwanakin.
Da hannu biyu ya dafe kansa, wancan fada masa akayi yanzu kuma ta maimaita masa harda qarin wasu kalaman da suka fi na farko muni duk akan Hajiyarsa anya idan yaci gaba da zama da Umaimah kuwa ya cika dan Halas? Macenda zata kalli cikin idonsa ta zagi uwar data haifeshi zagi mafi muni ta cancanci yaci gaba da zama qarqashin inuwar aure da ita kuwa?
Be ga ta inda ya kamata ace yayiwa Umaimah uzuri ba bayan wannan abun da tayi masa, idan zata zageshi ya shanye baya tsammanin ze jure cin mutunchin mahaifiyarsa kuma dole ya nuna mata cewar yana martaba Hajiyarsa kuma be hadata da kowa da komai a duniyar nan ba. Dakyar ya iya miqewa ya bude jakar Office dinsa dake ajiye a falon ya dauki biro da takadda ya zauna amma ya kasa rubuta abinda zuviyarsa take ayyana masa. Ya gwada rubutun yafi sau goma amma ya kasa yanda kasan an daure masa yatsu haka yakeji ga wata faduwar gaba tamkar zuciyarsa zata tsaga qirjinsa ta fito haka yake ji se yayi jifa da takaddar da bironya miqe tana layi ya isa gurin Dispenser ya tsiyayi ruwa me sanyi ya ringa sha har seda yaji kamar zeyi amai kafin ya haqura, a nan gurin ya tsugunna ya dafe kansa da hannu biyu, wani irin abu yake ji a cikin jikinsa, ikon Allah ne ya bashi qarfin bude baki ya shiga karanto duk addu'ar da tazo bakinsa be san tsahon lokacin daya dauka a halin da yake ciki ba sejin qarar wayarsa yayi ya bude ido dakyar yana kallon inda yake, anan gana Dispenser yayi bacci, ya yunqura dakyar ya tashi zaune nauyin da kansa yayi masa ya ragu wayarsa ta sake daukar qara ya shiga lalubenta ya dakko, qarfe biyar da minti Ashirin ya gani Alarm din daya saita ne tun qarfe biyar ze yanzu Allah ya bashi ikon ji.
Bayan yayi wanka ya shirya ya fita masallaci, a sahun baya yayi sallah sabanin da da kullum yana sahun farko. Bayan an idar da sallah be tashi ba yana zaune a gurin yana jan carbi, Malam Hashim Dattijo ne baban daya daga cikin Maqotansu ne ya dakko shi daga garinsu bashida lafiya, kullum a sahu daya suke SallarAsuba da Khalil din, haka Magriba da Isha indai a gida yayi su kwanakinya lura da Khalil din baya zuwa sallah masallacin se yau ya ganshi yana shigowa a yanayin da be saba ganinsa ba. Kusada Khalil ya zauna yana kallonsa yanda yayi zuru yana jan carbi ya saka wa guri daya ido bashi da tabbacin yasan abinda yake karantawa m seya kai hannu ya dafashi Khalil yayi firgigit ya kalli Dattijon kafin ya sauke Ajiyar zuciya ya shiga gaishe shi.
"Ibrahimu kwana biyu baka zuwa Masallaci har na tambayi wannan yaron ko kayi tafiya ne yace Aa yana ganin gilmawarka, lafiya dai naga dukka rame ka fita a hayyacinka haka?" Dattijon ya fada har sannan hannunsa na kan kafadar Khalil din se ya sauke ajiyar zuciya ya kalli Tsohon yace
"Ina nan Baba, kwana biyun banajin dadi shi yasa bana iya fitowa amma yanzu Alhamdulillah na samu sauqi"
"Toh Allahya qara rufa Asiri, amma kaganka kuwa wane ciwo ne yake damunka haka daya saka duk ka firgice?" Tsohon ya sake fada yana qare masa kallo se Khalil ya sunkuyar da kansa qasa dan be san me zece masa yana damunsa ba. Shi kansa in banda ciwon kai babu abinda zece gashi yana damunsa dan haka ya bude baki a hankali yace
"Ciwon kai nakeyi Baba, aiki ne yake mun yawa kwana biyu yake saukar mun da ciwon kai"
"Ko naji kasan shi ciwon kai yafi saurin gigita mutum gaba daya kaga ya fitar da mutum daga hayyacinsa, amma bayan ciwon kan babu abinda yake damunka kuma" Baba ya sake fada se Khalil ya daga masa kai alamar Eh Tsohon yaci gaba da cewa
"Bari idan na shiga gida zan duba maka wani magani da na taho dashi daga gida, kwanaki da wannan yaron shima yayi fama da ciwon kan harda jiri yayi ta yawon Asibiti suna cewa jininsa ne ya hau ana bashi magani, tunda ya shaqa maganin nan sau daya kan ya sauka, da yake shi hade hade ne duka da maganin miyagu da makaru na sihiri kuda kuke harka ta mutane daman dole se kun nemi tsari dan baku san zuciyar wadanda kuke tare dasu ba. Sannu bari na shiga gidan yanzu zan dakko maka na bawa takwarana ya kawo maka Allah ya qara afuwa ya ci gaba da doraku akan maqiya".
Da Amin ya amsa danya gaji da surutun tsohon, sun saba sosai kullum se sunyi hira amma yanzu da kansa yake masa kamar ana daka baya buqatar wani dogon surutu, tare suka fita Baban ya wuce gidan dansa shi kuma ya shiga gida. Badan akwai ayyukan da yake so ya qarasa ba saboda tafiyar da zasuyi da yau baze fita aiki ba. Be ko saurari abin karin da Ruqayya ke hadawa na ya wuce bangaren Hajiya a can ya tarar da qullin maganin Musa yaron maqocinsa ya kai mata ta ajiye masa.
Bayanya gaya mata yanda sukayi da Dattijon tace masa
"Ka gwada toh gashi nan kuwa dare daya ka rame dan jiya ba haka ka shigo ba duk idonka sun fada idan ka fita ka biya Asibiti a sake dubaka, na gaya maka ka cire komai daga zuciyarka kaqi bafa a fara ba Babana idan ka karaya tun yanzu ta yaya zaka tafiyar da zaman naku? In har kana ganin ba zaka iya jurwwa na lokaci be qure ba ka janye zama lafiya aka ce yafi zama dan sarki meye amfanin abinda za'ayi a maimakon ka samu nutsuwa da farin ciki ka sake gayyatowa kanki wata damuwar?"
"A can tsohon gidana nake so na ajiyeta, gyaransa kuma a qalla ze iya daukana wata shida Hajiya, idan kun sake yin magana da Baba Abu ki gaya masa se kuma maganar abinda za'a kai shima idan ya yanke se ki gaya mun na tura masa" ya bagarar da maganar da takeyi ya canza mata da wata, se taja numfashi tace
"Yace Alhaji Garba ya bada dubu dari biyu dukiyar aure shi kuma ze bada Dari Sadaki se kaji da biyan bashin da Hasanar ka ta tattago maka su"
"Allah ya saka musu da Alkairi" ya fada kafin ya kwance maganin yana kallonsa Hajiya tace
"Musa yace baya komai suma idan suna ciwon kai Kakan shi yake shaqa muba se ma daya gwadamun yanda akeyi bari ka gani" ta debi garin kadanta shaqa Khalil na kallonta haka ya diba shima ya shaqa da dan yawa ya qulle ledar.
Zama yayi yana jiran Habiba da take soya doya, kamar qura ta taso haka yaji kansa yayi dummm kafin kace me ya shiga jera Atishawa babu qaqqautawa. Tun Hajiya na daukar abun da sauqi harta tsorata ganin yanda yake yinta ya kasa zama akan kujera ya sauka qasa yana ci gaba da jera ta da qarfin gaske idonsa ya tara hawaye. Habiba ta kwalawa kira ta fito a rikice itama dan tana jiyo Atishawar tasa data zarce hankali.
"Kiyi maza ki shiga gidan Officer kice wa Musa yazo" Hajiya ta fada tana riqe Khalil dake Atishawa kamar wanda ya sauka daga iska, fitar Habiba babu dadewa se gata sun dawo tareda Baba Musa, Hajiya ta kalleta tace
"Musa qarami nake nufi ba kai ba Alhaji"
"Wannan kiran ai nawane Hajiya bana Takwara ba, ta gaya mun halin da ake ciki ne nace bari nazo da kaina na gani sannu Ibrahimu kaji Allah ya qara taqaitawa ai mantawa nayi daman ban gaya maka ba, idan da Sihiri ko sammu indai shaqarsa yayi da izinin Allah seya fitar da duk ma abinda ya shige masa kai wannan Atishawar da kika gani shaidanun da suka samu guri akan sa suke haddasa masa ciwon ne suka fita sannu kaji, da za'a samu tazargade se a sake turara masa babu komai in Allah ya yarda sannu" ya sake fada yana dafa Khalil dake zaune a qasa yana maida numfashi dan Atishawar ta lafa masa, kuma wani ikon Allah duk wannan nauyin da yake jin kansa ya masa ya sauka sakayau yake jinsa kamar wanda yayi sabon Aski.
A tarkace Hajiya ta binciko Tazargadenta dade da wata Qanwarta ta kawo mata tace ta ringa turarawa itama amma ko sau daya bata taba gwadawa ba nan Habiba ta kunna coal ta zuba, ba iya Khalil ba duka gidan suka bi suka turare Hajiya na cewa
"Ni Aishatu Babana a ina ka shaqo wannan jaraba kuma koma ina ne dai an auna arziqi tunda mun samu makarin abun da wuri kai Allah kayi mana maganin abinda ya dame mu"
"Nifa Hajiya ban yarda da wani Asiri ko menene ba kawai ciwon kaine kuma stress ya kawo shi, me nayiwa wani da zeyimun Asiri nida hayaqi in ba akan titi ba na motoci a ina nake ganinsa ma ko turaren wuta za'a saka a gidan nan kin sani kafin nadawo an saka dan bana son na ringa shaqar qaurin" Khalil ya fada se Hajiya tace
"Ai shikenan, Allah yaci gaba da karewa ka tashi kaci abincin idan babu hali ka haqura da zuwa aikin ma kawai yau daya dai ka huta" .
Da hannu biyu ya dafe kansa, wancan fada masa akayi yanzu kuma ta maimaita masa harda qarin wasu kalaman da suka fi na farko muni duk akan Hajiyarsa anya idan yaci gaba da zama da Umaimah kuwa ya cika dan Halas? Macenda zata kalli cikin idonsa ta zagi uwar data haifeshi zagi mafi muni ta cancanci yaci gaba da zama qarqashin inuwar aure da ita kuwa?
Be ga ta inda ya kamata ace yayiwa Umaimah uzuri ba bayan wannan abun da tayi masa, idan zata zageshi ya shanye baya tsammanin ze jure cin mutunchin mahaifiyarsa kuma dole ya nuna mata cewar yana martaba Hajiyarsa kuma be hadata da kowa da komai a duniyar nan ba. Dakyar ya iya miqewa ya bude jakar Office dinsa dake ajiye a falon ya dauki biro da takadda ya zauna amma ya kasa rubuta abinda zuviyarsa take ayyana masa. Ya gwada rubutun yafi sau goma amma ya kasa yanda kasan an daure masa yatsu haka yakeji ga wata faduwar gaba tamkar zuciyarsa zata tsaga qirjinsa ta fito haka yake ji se yayi jifa da takaddar da bironya miqe tana layi ya isa gurin Dispenser ya tsiyayi ruwa me sanyi ya ringa sha har seda yaji kamar zeyi amai kafin ya haqura, a nan gurin ya tsugunna ya dafe kansa da hannu biyu, wani irin abu yake ji a cikin jikinsa, ikon Allah ne ya bashi qarfin bude baki ya shiga karanto duk addu'ar da tazo bakinsa be san tsahon lokacin daya dauka a halin da yake ciki ba sejin qarar wayarsa yayi ya bude ido dakyar yana kallon inda yake, anan gana Dispenser yayi bacci, ya yunqura dakyar ya tashi zaune nauyin da kansa yayi masa ya ragu wayarsa ta sake daukar qara ya shiga lalubenta ya dakko, qarfe biyar da minti Ashirin ya gani Alarm din daya saita ne tun qarfe biyar ze yanzu Allah ya bashi ikon ji.
Bayan yayi wanka ya shirya ya fita masallaci, a sahun baya yayi sallah sabanin da da kullum yana sahun farko. Bayan an idar da sallah be tashi ba yana zaune a gurin yana jan carbi, Malam Hashim Dattijo ne baban daya daga cikin Maqotansu ne ya dakko shi daga garinsu bashida lafiya, kullum a sahu daya suke SallarAsuba da Khalil din, haka Magriba da Isha indai a gida yayi su kwanakinya lura da Khalil din baya zuwa sallah masallacin se yau ya ganshi yana shigowa a yanayin da be saba ganinsa ba. Kusada Khalil ya zauna yana kallonsa yanda yayi zuru yana jan carbi ya saka wa guri daya ido bashi da tabbacin yasan abinda yake karantawa m seya kai hannu ya dafashi Khalil yayi firgigit ya kalli Dattijon kafin ya sauke Ajiyar zuciya ya shiga gaishe shi.
"Ibrahimu kwana biyu baka zuwa Masallaci har na tambayi wannan yaron ko kayi tafiya ne yace Aa yana ganin gilmawarka, lafiya dai naga dukka rame ka fita a hayyacinka haka?" Dattijon ya fada har sannan hannunsa na kan kafadar Khalil din se ya sauke ajiyar zuciya ya kalli Tsohon yace
"Ina nan Baba, kwana biyun banajin dadi shi yasa bana iya fitowa amma yanzu Alhamdulillah na samu sauqi"
"Toh Allahya qara rufa Asiri, amma kaganka kuwa wane ciwo ne yake damunka haka daya saka duk ka firgice?" Tsohon ya sake fada yana qare masa kallo se Khalil ya sunkuyar da kansa qasa dan be san me zece masa yana damunsa ba. Shi kansa in banda ciwon kai babu abinda zece gashi yana damunsa dan haka ya bude baki a hankali yace
"Ciwon kai nakeyi Baba, aiki ne yake mun yawa kwana biyu yake saukar mun da ciwon kai"
"Ko naji kasan shi ciwon kai yafi saurin gigita mutum gaba daya kaga ya fitar da mutum daga hayyacinsa, amma bayan ciwon kan babu abinda yake damunka kuma" Baba ya sake fada se Khalil ya daga masa kai alamar Eh Tsohon yaci gaba da cewa
"Bari idan na shiga gida zan duba maka wani magani da na taho dashi daga gida, kwanaki da wannan yaron shima yayi fama da ciwon kan harda jiri yayi ta yawon Asibiti suna cewa jininsa ne ya hau ana bashi magani, tunda ya shaqa maganin nan sau daya kan ya sauka, da yake shi hade hade ne duka da maganin miyagu da makaru na sihiri kuda kuke harka ta mutane daman dole se kun nemi tsari dan baku san zuciyar wadanda kuke tare dasu ba. Sannu bari na shiga gidan yanzu zan dakko maka na bawa takwarana ya kawo maka Allah ya qara afuwa ya ci gaba da doraku akan maqiya".
Da Amin ya amsa danya gaji da surutun tsohon, sun saba sosai kullum se sunyi hira amma yanzu da kansa yake masa kamar ana daka baya buqatar wani dogon surutu, tare suka fita Baban ya wuce gidan dansa shi kuma ya shiga gida. Badan akwai ayyukan da yake so ya qarasa ba saboda tafiyar da zasuyi da yau baze fita aiki ba. Be ko saurari abin karin da Ruqayya ke hadawa na ya wuce bangaren Hajiya a can ya tarar da qullin maganin Musa yaron maqocinsa ya kai mata ta ajiye masa.
Bayanya gaya mata yanda sukayi da Dattijon tace masa
"Ka gwada toh gashi nan kuwa dare daya ka rame dan jiya ba haka ka shigo ba duk idonka sun fada idan ka fita ka biya Asibiti a sake dubaka, na gaya maka ka cire komai daga zuciyarka kaqi bafa a fara ba Babana idan ka karaya tun yanzu ta yaya zaka tafiyar da zaman naku? In har kana ganin ba zaka iya jurwwa na lokaci be qure ba ka janye zama lafiya aka ce yafi zama dan sarki meye amfanin abinda za'ayi a maimakon ka samu nutsuwa da farin ciki ka sake gayyatowa kanki wata damuwar?"
"A can tsohon gidana nake so na ajiyeta, gyaransa kuma a qalla ze iya daukana wata shida Hajiya, idan kun sake yin magana da Baba Abu ki gaya masa se kuma maganar abinda za'a kai shima idan ya yanke se ki gaya mun na tura masa" ya bagarar da maganar da takeyi ya canza mata da wata, se taja numfashi tace
"Yace Alhaji Garba ya bada dubu dari biyu dukiyar aure shi kuma ze bada Dari Sadaki se kaji da biyan bashin da Hasanar ka ta tattago maka su"
"Allah ya saka musu da Alkairi" ya fada kafin ya kwance maganin yana kallonsa Hajiya tace
"Musa yace baya komai suma idan suna ciwon kai Kakan shi yake shaqa muba se ma daya gwadamun yanda akeyi bari ka gani" ta debi garin kadanta shaqa Khalil na kallonta haka ya diba shima ya shaqa da dan yawa ya qulle ledar.
Zama yayi yana jiran Habiba da take soya doya, kamar qura ta taso haka yaji kansa yayi dummm kafin kace me ya shiga jera Atishawa babu qaqqautawa. Tun Hajiya na daukar abun da sauqi harta tsorata ganin yanda yake yinta ya kasa zama akan kujera ya sauka qasa yana ci gaba da jera ta da qarfin gaske idonsa ya tara hawaye. Habiba ta kwalawa kira ta fito a rikice itama dan tana jiyo Atishawar tasa data zarce hankali.
"Kiyi maza ki shiga gidan Officer kice wa Musa yazo" Hajiya ta fada tana riqe Khalil dake Atishawa kamar wanda ya sauka daga iska, fitar Habiba babu dadewa se gata sun dawo tareda Baba Musa, Hajiya ta kalleta tace
"Musa qarami nake nufi ba kai ba Alhaji"
"Wannan kiran ai nawane Hajiya bana Takwara ba, ta gaya mun halin da ake ciki ne nace bari nazo da kaina na gani sannu Ibrahimu kaji Allah ya qara taqaitawa ai mantawa nayi daman ban gaya maka ba, idan da Sihiri ko sammu indai shaqarsa yayi da izinin Allah seya fitar da duk ma abinda ya shige masa kai wannan Atishawar da kika gani shaidanun da suka samu guri akan sa suke haddasa masa ciwon ne suka fita sannu kaji, da za'a samu tazargade se a sake turara masa babu komai in Allah ya yarda sannu" ya sake fada yana dafa Khalil dake zaune a qasa yana maida numfashi dan Atishawar ta lafa masa, kuma wani ikon Allah duk wannan nauyin da yake jin kansa ya masa ya sauka sakayau yake jinsa kamar wanda yayi sabon Aski.
A tarkace Hajiya ta binciko Tazargadenta dade da wata Qanwarta ta kawo mata tace ta ringa turarawa itama amma ko sau daya bata taba gwadawa ba nan Habiba ta kunna coal ta zuba, ba iya Khalil ba duka gidan suka bi suka turare Hajiya na cewa
"Ni Aishatu Babana a ina ka shaqo wannan jaraba kuma koma ina ne dai an auna arziqi tunda mun samu makarin abun da wuri kai Allah kayi mana maganin abinda ya dame mu"
"Nifa Hajiya ban yarda da wani Asiri ko menene ba kawai ciwon kaine kuma stress ya kawo shi, me nayiwa wani da zeyimun Asiri nida hayaqi in ba akan titi ba na motoci a ina nake ganinsa ma ko turaren wuta za'a saka a gidan nan kin sani kafin nadawo an saka dan bana son na ringa shaqar qaurin" Khalil ya fada se Hajiya tace
"Ai shikenan, Allah yaci gaba da karewa ka tashi kaci abincin idan babu hali ka haqura da zuwa aikin ma kawai yau daya dai ka huta" .