Sashe 236
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kekam idanunki basa ciwo kullum kuka kamar matar Mamaci? Gaki ga dakin ai bismillah ki shigo" ta wuce cikin daki ta barta a qofar falon tana kuka, ita kam tana rasa ajin da zata saka Umaimah lokuta da yawa ta rasa wauta ce ko gabunta suke damunta se Allah amma Al'amarinta bayan Iskanci na qashin kai harda rashin cikakken wayo ma duk ta hada.
Umaimah kuwa ta gama kukanta ta tashi ta koma daki ta dora, to ita tayaya zata nuna musu ta gane kurenta bayan babu fuska? Ai ya kamata koda sau daya ne su saurareta duk wanda ya kalleta ko bata fada ba ai yasan tana cike sa nadama da dana sanin abubuwan data aikata. Da zata gaida Abbanma dai kasa shiga falonsa tayi ta durqusa daga bakin qofa ya amsa mata faran faran kai ba zaka ce akwai wani grudges tsakaninsu ba. Haka ta wuni tana bare bare da Maman ta yunqura zatayi abu zata karba koda baya cikin ayyukan da take musu a gidan so takeyi tayi mata magana ta roqeta amma tsoron yanda zata karbeta takeji ita kuwa Maman tana ankare da ita tsaf sedai tayi murmushi a ranta da zahiri ko a kullum cikin nema mata shiriya a gurin ubangiji takeyi dan ta yarda fushi bazeyi mata magani ba. A haka suka sake kwashe sati biyu kuma Ruma bata sake zuwa ba damuwa ta sake mata rubdugu ta kasa sakin jiki kamar yanda Ruman ta gaya mata dukda tayi Namijin qoqarin ranar Juma'a dasu Nuratu sukaje gidan kamar yanda suka saba har bakin qofar Mama taje ta durqusa ta gaishe su ai kam seda sukayi Suman zaune na sakanni kafin suka hada baki gurin amsa mata kowacce cike da Mamakinta, yanda ta sunkuyar da kai tana hawaye kamar wadda tazo Maula ya taba su amma suka dake, jin daga gaisuwar bata qara cewa komai ba suma basu ce mata ba ta gaji da durquson ta tashi Anty Hafsa tace
"Allah ya yayewa yarinyar nan abinda yake damunta" Mama ta amsa da Amin kafin tace
"Haka take kullum zatazo bakin qofar nan tayi ta zubar da hawaye ni kuwa kanzil bana ce mata daga nan har randa qiyama zata tsaya muddin bata budi baki tayi magana ba mu zuba mu gani itace a wahale".
A haka rayuwa taci gaba da gara mata kullum kuma maimakon ta samu sauqin Al'amura qara tsananta sukeyi a cikin wannan yanayi Ummu-Salma diyar Anty da akayi aure wata goma kenan tadawo gida haihuwa. Nan dakin da take Abba yace Ummu-Salman ta zauna dake ita bata da Matsala kamar qanwarta lafiya lau suke zaune zuwan nata ma seya zamo mata wata sa'ida tubda ko babu komai ta samu abokiyar hira musamman da yanzu itama tayi aure ta fara sanin rayuwa da yanda take cikin hikima take nunarwa da Umaiman kurakuren daya kamata tasha kansu tamkar dai maganganun da Ruma ta gaya mata sedai tsoro yasa har sannan ta kasa tunkarar Maman ko Abban kai tsaye da magana se rara gefe takeyi da suke nuna tamkar basu san me take ciki ba.
Satin Salma daya da dawowa gida ta haihu, Umaimah ce ta zama yar saka ruwan wanka bisa Umarnin Abba ga damuna a lokacin wata rana haka take zama kamar zata zauce saboda hayaqi gana girki ga na ruwan wanka safe da yamma shikansa girkin ya qaru saboda yan zuwa barka haka yan uwan Anty zasuyita yada mata magana wasu a fakaice wasu kai tsaye yanda ta ringa musu a baya wai ta baro daula ta dawo Boyi boyi da zaman dabaro, ana gobe suna wata yar Yayar Anty da suke sa'anni zamanin yammatanci tare sukayi tana yawan zuwa gidan haka Umaimah zatayi ta gwaba mata magana wai tazo cin arziqi saboda gidansu Babu kullum tana tafe yawon kwadayi abun na bala'in yiwa Nabilan ciwo amma lokacin se Anty ta hanata mayar mata da martani. Ana gobe suna tazo barkar Ummu Salman itama da tsohon cikinta sukayi kicibus da Umaimah na kwashe ruwan wanka tayi yarkace yarkace dan ba qaramar wuya taci ba kafin itacen ya kama Nabilan ta kalleta cikin izgilanci ta kalli wadda suka shigo tare tace
"Kinga ma shikenan ina zancen neman me zaman dabaro ga wata bari mu shiga na tambayi Anty inda suka samota dan da gani zatayi aiki sosai sannu baiqar Allah" yanda tayi maganar seka rantse bata gane Umaiman ba nan kiwa tsabar wulaqanci ne daman Allah Allah take tazo ta ganewa idonta yanda akace Umaiman ta koma lokacin biki basu wani ganta ba daki ta ringa shiga tana kulle kanta har aka gama yanzu kuwa bbau dama tunda an dora mata Alhakin dora garwar wanka ya ta iya da ranta. Maganar Nabilan ta mata ciwo kwarai har seda ta zagaya bayan gida tayi kuka ta more ta yarda duk abinda ta gani ba komai bane akan irin tsiyatakun data shuka a baya.
Washe gari ranar suna sega yaranta babu zato an Kawo su suka wuni tareda sauran cousins dinsu duk inda suka gifta se anyi maganarsu ta haka kuma za'a zageta wasu a fakaice wasu kai tsaye kamar yanda suke fada ai ba tsoronta sukeji ba, Mijin da take taqamar ya tsaya mata yanzu babu ita da banza duk daya suka a gurinsu da Magriba aka zo daukar yaran seda aka sha daga da Bibi kafin ymta yarda ta bisu tana kuka sosai Driver su daya kaisu ya dauke su haka rayuwa taci gaba yau baqi gobe tsumma.
GIDAN KHALIL
Washe gari hankalinsu be kwanta ba daga shi har Humaira seda sukaje Asibiti. Dr Mahmud likitan da yake dubashi ya kalleshi da murmushi bayan ya gama examining nashi ya kuma hada da bayanan da yayi masa akan abinda yaji a daren jiyaj fuskarsa dauke da murmushi yace
"Kaga abinda muka gaya maka ko? Dama na gaya maka bazamuce ka rasa lafiyarka gaba daya ba haka nan ba zamu baka tabbacin zaka warke ko kuma lokacin faruwar hakan ba amma gashi yanzu cikin yardar Allah alamun nasara sun fara bayyana. Abinda nake so dakai shine kayi qoqarin kiyayewa kar kace zaka takura kanka kamar yanda al'amarin jiya ya faru ba tareda ka shirya masa ba muna fatan hakan taci gaba da faruwa amma kayi haquri karkace zakayi gaggawa kabi komai a sannu ciwon kuma da kaji wannan dolene idan kayi la'akari da cewar ka kwashi shekaru ba tareda irin saqon nan yaje kwakwalwarka ba jijiyoyin da suke da alhakin hakan duk sun kwanta dole yanzu da aka motsa su za'a dan sha wahala kafin su daidaita su koma aiki yanda ya kamata shiyasa nace se kabi a sannu banda Garaje in Allah yayarda a dan lokaci komai ze daidaita dan Alamun nasarar da qafinsu sukazo tinda har kace kaji alamar kayi releasing sannan koda ace lafiyarka ta dawo zaka fuskanci wannan matsalar ta saurin Inzali amma kar hakan ya dameka da sannu komai ze daidaita".
Khalil dai baki kamar gonar auduga inda Humaira ta sunkuyar da kai qasa a ranta tana cewa wannan likitan bashi da kunya me makon yace ta fita. Seda ya canza masa magunguba kafin suka miqe zasu fita sukayi Musabaha da Khalil ya kalleta tana masa se anjima yace
"Madallah Amarya ina sakw tayaki murna, se a lallabamun patient dai kar ayi masa garaje".
Da kusan gudu ta fice daga office din suka rakata da dariya kafin Khalil yabi bayanta, a mota ma tasa ta yayi da tsokana ita dai ta kanne taqi kulashi, a gida Hajiya ta ringa tambayarsa meya faru saboda farincikin dake kan fuskarsa ya kasa boyuwa amma rashin kunyar tasa bata kai ya iya mata bayani ba balle Humaira se ta barsu akan kawai dadin zama ne domin ita shaida ce irin zaman da sukeyi me tsafta da girmama juna. A haka yaci gaba da lelen lafiyarsa kamar yanda likitan ya fada kuma beyi garaje ba dan be sake attempting tabata ba sedai suyi abinda suka sabayi wanda shima yanzu baya iya jurewa da yawa saboda jikinsa ya fara komawa daidai daya fara tabata zeji yana son kasancewa da ita sedai wani lokacin kafin yakai ga jikinta ma zeyi releasing daga nan komai ze sakeshi wannan al'amarin ya dameshi har yaso yafi sanda ya tabbatar da basho da lafiyar gaba daya shiga tashin hankali saboda a yanzu baya iyayi mata abubuwan daya saba a baya hakan kuma na damunta wanda ya fara fahimtar hakan a tareda ita. Walwalarta ta ragu, duk sanda ya jagwalgwalata ba tareda ta samu nutsuwa ba ranar wuni zasuyi babu dadi ita dai bata taba bude baki ta masa qorafi ba amma yasan abun yana damunta. Shi kuma ciwon da yake damunsa da mutuwar jikin da yake fuskanta da zarar ya fitar da abinda ya dameshi ne suke hanashi samar mata da nutsuwar, gashi daya fara tabata yanzu jikinsa ze amsa har ya fara jin dama ya zauna a yanda yake yafi samun kwanciyar hankali da iyalinsa dan yanzu wannan sabon Al'amarin na neman ya dagula musu lissafi.
Tilas babu shiri ya sake tafiya India ganin likita, suka gama masa duk gwaje gwajen daya kamata suka qara masa magunguna tareda kalaman ban haquri akan komai zeyi daidai with time haka ya tattaro ya dawo cike da fargabar yanda zamansu zeci gaba da kasancewa sedai be yanke qauna ba Allahn daya farfado dashi shi ze bashi isashshiyar lafiyar daze cigaba da kulawa da ita.
Umaimah kuwa ta gama kukanta ta tashi ta koma daki ta dora, to ita tayaya zata nuna musu ta gane kurenta bayan babu fuska? Ai ya kamata koda sau daya ne su saurareta duk wanda ya kalleta ko bata fada ba ai yasan tana cike sa nadama da dana sanin abubuwan data aikata. Da zata gaida Abbanma dai kasa shiga falonsa tayi ta durqusa daga bakin qofa ya amsa mata faran faran kai ba zaka ce akwai wani grudges tsakaninsu ba. Haka ta wuni tana bare bare da Maman ta yunqura zatayi abu zata karba koda baya cikin ayyukan da take musu a gidan so takeyi tayi mata magana ta roqeta amma tsoron yanda zata karbeta takeji ita kuwa Maman tana ankare da ita tsaf sedai tayi murmushi a ranta da zahiri ko a kullum cikin nema mata shiriya a gurin ubangiji takeyi dan ta yarda fushi bazeyi mata magani ba. A haka suka sake kwashe sati biyu kuma Ruma bata sake zuwa ba damuwa ta sake mata rubdugu ta kasa sakin jiki kamar yanda Ruman ta gaya mata dukda tayi Namijin qoqarin ranar Juma'a dasu Nuratu sukaje gidan kamar yanda suka saba har bakin qofar Mama taje ta durqusa ta gaishe su ai kam seda sukayi Suman zaune na sakanni kafin suka hada baki gurin amsa mata kowacce cike da Mamakinta, yanda ta sunkuyar da kai tana hawaye kamar wadda tazo Maula ya taba su amma suka dake, jin daga gaisuwar bata qara cewa komai ba suma basu ce mata ba ta gaji da durquson ta tashi Anty Hafsa tace
"Allah ya yayewa yarinyar nan abinda yake damunta" Mama ta amsa da Amin kafin tace
"Haka take kullum zatazo bakin qofar nan tayi ta zubar da hawaye ni kuwa kanzil bana ce mata daga nan har randa qiyama zata tsaya muddin bata budi baki tayi magana ba mu zuba mu gani itace a wahale".
A haka rayuwa taci gaba da gara mata kullum kuma maimakon ta samu sauqin Al'amura qara tsananta sukeyi a cikin wannan yanayi Ummu-Salma diyar Anty da akayi aure wata goma kenan tadawo gida haihuwa. Nan dakin da take Abba yace Ummu-Salman ta zauna dake ita bata da Matsala kamar qanwarta lafiya lau suke zaune zuwan nata ma seya zamo mata wata sa'ida tubda ko babu komai ta samu abokiyar hira musamman da yanzu itama tayi aure ta fara sanin rayuwa da yanda take cikin hikima take nunarwa da Umaiman kurakuren daya kamata tasha kansu tamkar dai maganganun da Ruma ta gaya mata sedai tsoro yasa har sannan ta kasa tunkarar Maman ko Abban kai tsaye da magana se rara gefe takeyi da suke nuna tamkar basu san me take ciki ba.
Satin Salma daya da dawowa gida ta haihu, Umaimah ce ta zama yar saka ruwan wanka bisa Umarnin Abba ga damuna a lokacin wata rana haka take zama kamar zata zauce saboda hayaqi gana girki ga na ruwan wanka safe da yamma shikansa girkin ya qaru saboda yan zuwa barka haka yan uwan Anty zasuyita yada mata magana wasu a fakaice wasu kai tsaye yanda ta ringa musu a baya wai ta baro daula ta dawo Boyi boyi da zaman dabaro, ana gobe suna wata yar Yayar Anty da suke sa'anni zamanin yammatanci tare sukayi tana yawan zuwa gidan haka Umaimah zatayi ta gwaba mata magana wai tazo cin arziqi saboda gidansu Babu kullum tana tafe yawon kwadayi abun na bala'in yiwa Nabilan ciwo amma lokacin se Anty ta hanata mayar mata da martani. Ana gobe suna tazo barkar Ummu Salman itama da tsohon cikinta sukayi kicibus da Umaimah na kwashe ruwan wanka tayi yarkace yarkace dan ba qaramar wuya taci ba kafin itacen ya kama Nabilan ta kalleta cikin izgilanci ta kalli wadda suka shigo tare tace
"Kinga ma shikenan ina zancen neman me zaman dabaro ga wata bari mu shiga na tambayi Anty inda suka samota dan da gani zatayi aiki sosai sannu baiqar Allah" yanda tayi maganar seka rantse bata gane Umaiman ba nan kiwa tsabar wulaqanci ne daman Allah Allah take tazo ta ganewa idonta yanda akace Umaiman ta koma lokacin biki basu wani ganta ba daki ta ringa shiga tana kulle kanta har aka gama yanzu kuwa bbau dama tunda an dora mata Alhakin dora garwar wanka ya ta iya da ranta. Maganar Nabilan ta mata ciwo kwarai har seda ta zagaya bayan gida tayi kuka ta more ta yarda duk abinda ta gani ba komai bane akan irin tsiyatakun data shuka a baya.
Washe gari ranar suna sega yaranta babu zato an Kawo su suka wuni tareda sauran cousins dinsu duk inda suka gifta se anyi maganarsu ta haka kuma za'a zageta wasu a fakaice wasu kai tsaye kamar yanda suke fada ai ba tsoronta sukeji ba, Mijin da take taqamar ya tsaya mata yanzu babu ita da banza duk daya suka a gurinsu da Magriba aka zo daukar yaran seda aka sha daga da Bibi kafin ymta yarda ta bisu tana kuka sosai Driver su daya kaisu ya dauke su haka rayuwa taci gaba yau baqi gobe tsumma.
GIDAN KHALIL
Washe gari hankalinsu be kwanta ba daga shi har Humaira seda sukaje Asibiti. Dr Mahmud likitan da yake dubashi ya kalleshi da murmushi bayan ya gama examining nashi ya kuma hada da bayanan da yayi masa akan abinda yaji a daren jiyaj fuskarsa dauke da murmushi yace
"Kaga abinda muka gaya maka ko? Dama na gaya maka bazamuce ka rasa lafiyarka gaba daya ba haka nan ba zamu baka tabbacin zaka warke ko kuma lokacin faruwar hakan ba amma gashi yanzu cikin yardar Allah alamun nasara sun fara bayyana. Abinda nake so dakai shine kayi qoqarin kiyayewa kar kace zaka takura kanka kamar yanda al'amarin jiya ya faru ba tareda ka shirya masa ba muna fatan hakan taci gaba da faruwa amma kayi haquri karkace zakayi gaggawa kabi komai a sannu ciwon kuma da kaji wannan dolene idan kayi la'akari da cewar ka kwashi shekaru ba tareda irin saqon nan yaje kwakwalwarka ba jijiyoyin da suke da alhakin hakan duk sun kwanta dole yanzu da aka motsa su za'a dan sha wahala kafin su daidaita su koma aiki yanda ya kamata shiyasa nace se kabi a sannu banda Garaje in Allah yayarda a dan lokaci komai ze daidaita dan Alamun nasarar da qafinsu sukazo tinda har kace kaji alamar kayi releasing sannan koda ace lafiyarka ta dawo zaka fuskanci wannan matsalar ta saurin Inzali amma kar hakan ya dameka da sannu komai ze daidaita".
Khalil dai baki kamar gonar auduga inda Humaira ta sunkuyar da kai qasa a ranta tana cewa wannan likitan bashi da kunya me makon yace ta fita. Seda ya canza masa magunguba kafin suka miqe zasu fita sukayi Musabaha da Khalil ya kalleta tana masa se anjima yace
"Madallah Amarya ina sakw tayaki murna, se a lallabamun patient dai kar ayi masa garaje".
Da kusan gudu ta fice daga office din suka rakata da dariya kafin Khalil yabi bayanta, a mota ma tasa ta yayi da tsokana ita dai ta kanne taqi kulashi, a gida Hajiya ta ringa tambayarsa meya faru saboda farincikin dake kan fuskarsa ya kasa boyuwa amma rashin kunyar tasa bata kai ya iya mata bayani ba balle Humaira se ta barsu akan kawai dadin zama ne domin ita shaida ce irin zaman da sukeyi me tsafta da girmama juna. A haka yaci gaba da lelen lafiyarsa kamar yanda likitan ya fada kuma beyi garaje ba dan be sake attempting tabata ba sedai suyi abinda suka sabayi wanda shima yanzu baya iya jurewa da yawa saboda jikinsa ya fara komawa daidai daya fara tabata zeji yana son kasancewa da ita sedai wani lokacin kafin yakai ga jikinta ma zeyi releasing daga nan komai ze sakeshi wannan al'amarin ya dameshi har yaso yafi sanda ya tabbatar da basho da lafiyar gaba daya shiga tashin hankali saboda a yanzu baya iyayi mata abubuwan daya saba a baya hakan kuma na damunta wanda ya fara fahimtar hakan a tareda ita. Walwalarta ta ragu, duk sanda ya jagwalgwalata ba tareda ta samu nutsuwa ba ranar wuni zasuyi babu dadi ita dai bata taba bude baki ta masa qorafi ba amma yasan abun yana damunta. Shi kuma ciwon da yake damunsa da mutuwar jikin da yake fuskanta da zarar ya fitar da abinda ya dameshi ne suke hanashi samar mata da nutsuwar, gashi daya fara tabata yanzu jikinsa ze amsa har ya fara jin dama ya zauna a yanda yake yafi samun kwanciyar hankali da iyalinsa dan yanzu wannan sabon Al'amarin na neman ya dagula musu lissafi.
Tilas babu shiri ya sake tafiya India ganin likita, suka gama masa duk gwaje gwajen daya kamata suka qara masa magunguna tareda kalaman ban haquri akan komai zeyi daidai with time haka ya tattaro ya dawo cike da fargabar yanda zamansu zeci gaba da kasancewa sedai be yanke qauna ba Allahn daya farfado dashi shi ze bashi isashshiyar lafiyar daze cigaba da kulawa da ita.