← Book details Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 267

Sashe 11

Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Yar unguwarmu kwana da yawa?" Khalil ya fada yana kallonta, kamar kuwa tana jira ta doka masa uwar Harara harda murguda baki, gani take kamar ma suna tare da Nabilan, qila ma soyya tayi nisa har suna shirin aure.

Jan ta Nasir ya ringayi da hira amma ina hankalinta na kan Khalil daya duqar dakai yana dannan waya yana murmushi, Albishir ne akayi masa, ya samu aiki da wani babban construction company a Lagos interview din yaje kwanaki har Nabila ta ganshi tareda wani abokinsa Taufeeq Babatunde wanda shi yayi masa hanyar aikin da yake Babansa babban mutum ne a Lagos din.
Yanzu yana gaya masa ne cewar comapany sun bude branch a nan Kano dan haka anan ze zauna.

Ita kuwa Umaimah gani takeyi ai da Yammata yake chatting zuciya tayo sama fuu ta fizgi jakarta murya a cunkushe tayiwa Sir Nasir sallama ta fice yana tsayar da ita amma taqi tsayawa.

Dagowa Khalil yayi jin an buga qofa da qarfi yace "lafiya? Me aka mata?"
"Kai zan tambaya dan tunda ta shigo kai naga tana harara da alama ka mata wani abun ne" Nasir ya fada yana dariya.

"Ni a ina zan ganta na wanta wani abu?" Ya fada yana daga hannu sama, Nasir daya miqe ya fara tattara takaddu yace

"Na sanin muku ba naji kace yar unguwarku ba waya sani ko tuni kun jone babu labari"
"Can da dadewa ne naganta a gidan mu an aiketa kai naman suna, ashe sister matar Habib Neighbor din mu ce, shine muka gaisa daga nan sau daya na sake ganinta tare da wadannan qawayen nata masu kalar rashin ji kusan six months kenan fa se yau na sake ganin ta ma ni" Khalil din ya fada cikin son kare kanshi.

"Nifa bance wani abu ba kake koro mun bayani kamar wani Lawyer, muje dan Allah ka sauke ni gareji na dauki motata nasan yanzu an gama gyaran, qarfe hudu zan kai Amir dressing Asibiti" Nasir ya fada bayan daya dauki abubuwan da ze buqata ya nufi qofa. Miqewa Khalil yayi shima yabi bayan sa yana cewa

"Dressing name? Meya samu Amir din?"
"Wallahi qonewa yayi da ruwan tea a qafa amma da sauqi inagadaga yau ma mun gama zuwa" Nasir ya bashi amsa daidai sanda suka isa gaban Motar Khalil din daya siya kwanannan Toyota Yaris Fara me kyau da ita.
Suna tafe yana masa qorafin rashin gaya masa qonewar Amir din suka isa get, rana ta take dan haka ana wahalar abin hawa.

Daga can gefe suka hango Umaimah a rabe fuskar nan kamar hadiri kai kace zata fasa kuka da alama tasha tsayuwa har ta gaji dan a jingine take da bango.

"Ga mutuniyarka can fa inaga ta rasa ride ne" Khalil ya fada yana kallo ta, se Nasir ya waiwaya shima ya kalleta yace
"Kai dai duk inda yarinyar nan take se idon ka ya hasko maka ita, toh ka mata lift ka kaita gida mana tunda hanyar ku daya"

"Bafa hanyar mu daya ba na gaya maka gidan sister tane a layin mu kai ka fiya matsala wallahi"

"Toh kaga daga nan seka gano Asalin gidan su mana ko ni me nace ne" Nasir ya fada yana qunshe dariya. Qarasawa kusa da inda take ya danna mata horn. Hararar da tayiwa motar idan da ace mutum tayiwa se ya kusa faduwa qila, ta qara tunzura baki gaba, ita ba akan titi take ba bare ace ta tare hanya amma koma waye ya kuskura ya qara mata horn seya gane kurensa.

Nasir ne ya sauje glass din bangarensa ya kalleta da murmushi yace "kina tsaye a rana abin hawa yayi wahala koh? Bismillah muje mu rage miki hanya".

Badan gajiya da ranar da ake kwallawa ba da babu abinda ze sa ta hau motar mutumin nan, tana qunquni haka ta bude baya ta shiga, sanyin Ac da qamshin turarensa suka sakata sakin ajiyar zuciyar dole seta qara bajewa tana jan iska a hankali, ta centre mirrow yake kallo ta ta sani amma tayi kamar bata san yanayi ba a ranta cewa take " shi kuma ciwon kallon mata ne dashi qilan.

A hanya Nasir ya sauka suka rabu akan da daddare Khalil zeje gida ya duba Amir din, Nasir ne ya bude mata qofa yace ta koma gaba, ba tayi niyya ba da taso ta mayar dashi Driver ne ya jata ya kaita gida amma ta daure ta sakko ta koma gaban.

Seda ya tsaya a wani guri ya siyo Youghort na L and Z manya guda uku masu Azabar sanyi da ruwan gora kafin suka ci gaba da tafiya. Youghort din ya miqa mata guda daya da ruwa ya ajiye ragowar

"Ban iya cin abinci a waje ba indai ba girkin Hajiyata ba sedai kona matata idan nayi aure shiyasa kullum wuni nake ina shan youghort idan bana gida" Khalil ya fada da son kawar da shirun da sukayi. Seta tabe baki, haka kawai ta samu kanta da cewa

"Amma ka iya zuwa Restaurant a Lagos kaci abinci har ka yi zance da yammata".

Kallon ta yayi cikin rashin fahimtar inda zancenta ya dosa yace
"Waya gaya miki naje Lagos?"
"Aljanuna ne suka gaya mun" ta bashi amsa kai tsaye, se ya saki murmushu, tana da tsiwa, kamar a jininta abin yaje hakan kuma kyau yake qara mata daidai sanda suka zo kwanar gidansu bisa kwatancen data bashi tace ya tsaya a nan.

"Har munzo ne?" Ya tambayeta yana gyara parking. Kayanta ta shiga tattarawa tana cewa

"Aa ka sauke ni a nan na qarasa cikin layi, bana so aga ka sauke ni a mota"

"Saboda me?"
"Saboda zaayi mun fada ace waye kai?" Ta bashi amsa a qage, dan bata so wani ya ganta, jiya jiya Mama ta gama yi mata fada akan shige shigen motocin samari kullum da wanda ze sauketa a gida da sunan abokanan aikinta hakanba mutunchi bane yanzu se mutane su chanza mata manufa dukda ita ba wani abu ta aikata ba.

"Mu qarasa, idan kina gudun fada ne zan shiga har cikin gidan na gayawa Mamanku ni na kawo ki bazata ce komai ba" Khalil ya fada yana taka motar ya shiga cikin layin,

"Se kace tasan ka, nidai ka koma baya ka sauke ni kawai dan Allah hakanma nagode" ta fada kamar zatayi kuka, be kulata ba yaci gaba da tafiya bata da zabi ganin yana neman wuce gidan ta tsayar dashi, a gurguje tayi masa sallama ta fice a motar, Layin kamar anyi shara babu kowa saboda uwar ranar data kwalle ta samu ta shige gida, ita kanta tana jin yanda gaba daya jikinta ya game da qamshin turarensa wanda ya kama motar.

Tsakar gidan ma babu kowa se Anty dake girki a kitchen ta rabe daga qofar gurin saboda rana.
"Allah shi qara, baku iyayi masu tausayin miji ba kuka jajibowa kanku girkin ice ai gashinan kuna ji a jikinku" Umaimah ta fada a zuciya, a fili kuwa murmushin qeta tayiwa Antyn harda gaisheta da yi mata sannu da gida ta wuce dakinsu saboda ta hango qofar Mama a rufe qila bata nan.

"Kai Yaya Umaimah turarenki dadi, zanzo dan Allah ki sammun, Salman qaninta ya fada daidai sanda tazo giftashi, tana qoqarin bashi amsa Mama ta shigo gidan da sallama idonta akan Umaimah data duburburce, Addu'arta Allah yasa Maman bata ga shigowarta ba.

*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK*

*(UMMU-MAHEER)*

*MARUBUCIYAR*

*WATA KISHIYAR🥰👹 (ALKHAIRI CE KO SHARRI)*

*RUBUTACCIYAR QADDARAH AND NOW*

*HALIN KISHI*

*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE NAIRA 500*

*GA DUK ME SO ZE TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*

*MARYAM UMAR FAROUK*

*SE A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*

Free page 6

Kallo daya Mama ta mata ta girgiza kai kawai ta shige ciki dan akan idonta Umaiman ta fito daga motar Khalil tana tsaye a soron gidan Maman Nana dan ta aiki Nanan tun tuni taji shiru ga babu yaron da zata tura shine tabi sahu da kanta. Ita dai fatanta kullum Allah ya shiryi Umaimah yasa ta ringa jin magana, bata zarginta da aikata wani abu amma wannan shegen rawar kan nata da kwashe kwashen ya isa ya janyo mata magana abinda batayi bama ace tayi.

Umaimah ko dakin su ta shige tunda dai batace komai ba idan ma ta gantan ai shikenan, ruwa ta fara watsawa saboda mugun zafin da ake ta saka doguwar riga me siririn hannu da hula ta nufi kitchen inda Anty take girki, yau Alhamis tasan dole a samu dan farfesun wani abun saboda kusan kowa na gidan yana azumi, litinin da Alhamis din kuwa se Abba ya siyo abinda zaayi romo aci da buda baki duk satin Allah.

Tundaga tsakar gidan kuwa ta fara jiyo qamshin dahuwar nama, ta hadiyi yawu tayi murmushi kafin ta qarasa daga qofar kitchen din ta kalli Anty da ido yayi ficifici saboda hayaqi ga zafin wuta gana gari tace

"Sannu Anty, an abinci ya sauka ne a sammin yunwa nake ji"
Murmushi Antyn ta mayar mata, harga Allah har cikin zuciyarta tana qaunar Umaimah amma a duk yaran gidan babu wanda ya rainata yake mata rashin kunya da diban Albarka irinta duk cikin taya mahaifiyarta kishi wadda ita sam ko a jikinta, tunda aka aurota bazata iya cewa yau ga ranar da Mama Malika tayi mata wani abu da sunan Kishi ba sedai sabani irin wanda kowanne yan Adam suke samu in dai an zauna amma kam maceceme tsananin kirki data kama girmanta haka tsayyaya ce aka yaranta kaf dinsu girmama Antyn suke hatta da Aminu da zasuyi Sa'anni idanya zo gidan yanda ze durqusa ya gaida Mahaifiyarsa haka ze durqusa mata wannan me ido atsakiyar kan ce se Addu'a kuma ita sam halin Umaiman ma ba damu ta yake ba.

Taf ta cika mata bowl da farfesun Naman rago daya ji kayan qamshi yawun Umaimah har tsinkewa yake,
"Ki duba fridge a dakina ki debi Zobo, akwai biredi akan Dining se ki hada tunda shinkafar bata sauka ba" Antyn ta sake fada tana kallonta.
Chapter 11 · 0% Book details