← Book details Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 160 OF 267

Sashe 160

Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yanda tayi maganar cikin sangarta da quruciya ya sakashi sakin murmushi. Rage gudun da yakeyi yayi, so yake yayi amfani da wannan damar yasan wasu abubuwa akanta dan haka ya sassauta muryarsa cikin lallami yace
"Toh amma naga harda waqoqin soyayya kike sakawa duk saboda shi sannan kuma kince Abokinki ne. Ki fada mun gaskiya daman wani ne ya ganki yave mun yana Sonki ni kuma naga kinada saurayi shiyasa bana so na hada ku kice bakya sonsa bazanji dadi ba dan dan uwanane".

Kallonsa ta ringayi harya yi shiru, ta tuna qawarta Mimi da tace mata ita banza ce da takr kula saurayi guda daya saurayin ma yaro duk ga mutane masu sonta nan da yawa amma tana musu wulaqanci gara ta qara samun ko mutum biyu ne da zata ringa hira dasu ta qara gogewa ta san Halayyar Maza da yawa. Wannan maganar ce ta sakata ce masa
"Eh to zan gaya maka gaskiya dai Saurayina ne kuma shi nake so na aura, amma daman ina so na qarayin wasu Samarin nima dan qawayena duk ba saurayi daya ne dasu ba"
Yanda take ke maganar zaka gane zallar yarinta a tattare da ita, kafin yayi magana taci gaba da cewa
"Kuma dan uwan naka indai dan gayune irinka toh ina sonsa amma fa a Aboki ba saurayi ba dan ni inada wanda zan aura".

"Ikon Allah" ya fada a ransa a fili kuwa ya kalleta yace
"Toh ai shi gaskiya da aure yake sonki kinga babu dama kuma kice sedai kuyi abota, sannan wa ya ce miki ma Mace da Namiji suna Abota ne?"
"Sunayi mana a school ina da Abokanai yan class dinmu sannan Friends dina ma bayan yan class dinmu suna da wasu Abokanan a waje kuma manya ne ma ba kamar mu ba" ta sake bashi amsa Innocently se yayi murmushi yace
"Yan class dinku wadannan class mates ne karatu ne ya hadaku bayan haka babu wata alaqa ta Abota da za'ace tsakanin Mace da Namiji se ta soyayya, idan kinyarda zaki bashi dama ya gwada miki tashi soyayyar toh sena hada ku".

Shiru tayi tana tunanin maganarsa se taji yace
"Zan bashi number wayarki, sati daya kacal ze gwada Sa'a idan har kika fara sonsa shikenan idan kuma sati ya cika baki fada sonsa ba ze haqura kin yarda?"

Haka kawai ta kasa musa masa, na farko cewar da yayi Abokinsa ne tasan Dan gayune irinsa ita kuma tana son Namiji me gayu shiyasa take qara son Noor dinta abu na biyu kuma itama tana so ta gwada Double dating kamar yanda qawayenta suke ta kwadaita mata dan haka ta amince ba tareda bata lokaci ba.
"Bari na baki number sa kiyi saving dan karya kira baki san waye ba kiqi dagawa" ya sake fada yana ciro wayarsa. Number ya karanta mata tayo saving kamar yanda yace, Abokin Yah Khalil ta saka saboda tafi ganewa. Yanzun ma daya maida ta be shiga ba yace ta gaida Maman ya bata ledojin Abincin daya siyo kafin ya kama hanyar gida.

Yana zuwa ya tarar da Umaimah na murqususun ciwon Mara, ko zama beyi ba suka sake juyawa Asibiti. A can ya barta ya dawo gida dan yayi wanka saboda sunce zata dan kwanta ta huta zuwa yamma kafin a sallameta.
Already ya sanarwa da Anwar baze je office ba ranar shiyasa yanayin wankan ya samu abinci yaci ya haye gado dan yayi baccin da be samu yayi da Safe ba kafin ya koma Asibiti.

Qaramar wayarsa ya dakko ya kunna, ba kasafai ya fiya amfani da ita ba number Layin da yake kanta ya bawa Humairan a matsayin number Abokinsa, seya dakko dayar wayarsa ya kwafi number ta ya saka akai kafin ya dannan mata kira.

HUMAIRAH
Tana shiga bayan ta gama bawa Mama labarin Jarabawa ta dora mata dana Abokin Khalil daya bata number sa. Mama tace
"Ikon Allah, nifa nace zaryar nan ta Khalil da walakin, harna fara tunanin ko Dan uwansa Khalifa yakeyiwa kamu kinji ashe wani Abokinsa ne. Nayiwa Mansur zancen nasan baze gaza sanin waye ba, me yace miki sunan Abokin?"
"Tab ya manta be fadamun ba nima kuma ban tambayeshi ba kawai da Abokinsa nayi saving number" Humairan ta bata amsa se Maman ta sake cewa
"Toh Allah ya tabbatar da Alkhairi, se ki nutsu idan ya kiraki kar kiyi masa maganar yarintar da kuka saba da Nura, kinga dai shi da hankalinsa dukda ban ganshi ba nasan Khalil baze hada ki da mutumin banza ba".

Tura baki tayi gaba tace
"Nifa cewa yayi sati daya kawai idan ban fara son Mutumin ba shikenan kuma kema kinsan inada wanda nake so kawai dan kar Yah Khalil din yaga na masa rashin kunya ne shi yasa na yarda". Se Maman ta kama baki tace

"Eh ai ni gashi kina mun rashin kunyar, ke ni na dawo daga rakiyar wannan alaqar taku da bata da Alqibla, Addu'ata kawai Allah ya zaba miki Miji na gari da ze rungumeki ya kula da ke ko bayan raina na samu nutsuwa nasan bazakiyi kukan maraici ba. Dan haka kema kiyi ta addu'a kawai lokaci da yawa abinda kake nacin So bashine Alkhairi a gareka ba".

Ita dai jin Maman kawai take amma ta tabbata babu wani Alkhairi a rayuwarta daya wuce Noor, shiyasanta yake kuma Sonta tun bata san kanta ba ta tabbatar kuma ze tarairayeta ya riqeta Amana kamar yanda Maman take mata fata. Bacci ta kwanta, a cikin baccin taji qarar wayarta tana farkawa taga Abokin Khalil ne yake kira. Kafin ta daga wayar ta katse se ga wani kiran ya sake shigowa dan haka ta miqe zaune tana goge ido kafin ta amsa wayar da Sallama tana tattaro dukkan Nutsuwarta kamar yanda Mama tace ta nutsu.

KHALIL
Yanajin ta amsa wayar tayi sallama gaba daya seya duburburce ya rasa abinda zece mata, meyasa kai tsaye be gaya mata shine ba yanzu idan ta gane muryarsa ai girmansa ya fadi zataga yayi mata qarya ne daya sani kai tsaye kawai ya fada mata shine ba wani Abokinsa ba. Sallamarta data sake ratsa kunnensa ya sakashi tattaro nutsuwarsa gaba daya ya amsa mata da dakakkiyar murya se sukayi shiru gana dayansu kafin ta shiga gaishe shi.

Maganar Minti goma sukayi, ya sanar mata da sunansa Ibrahim kuma shi dan Kano ne yana da Mata daya da yara biyu, Jim tayi kafin ta amsa masa dukda daman tasan da wuya ace Abokin nasa ya zama saurayi amma daya fada mata cewar yana da matar taji wani iri to wai ma meya shafeta ko mata dari ne dashi?
Itama a taqaice ta gaya masa Sunanta Aisha shikenan tayi shiru, ya tambayeta mutanen gida da kuma yaushe ya kamat yazo suga juna kafin magana tayi nisa a tsakaninsu se tayi shiru bata ce masa komai ba.
"Naji kinyi shiru Aish, koda akwai matsala ne?" Ya fada jin bata amsashi ba. Gabanta ya fadi, tunda suka fara magana daman muryarsa take mata wani iri, kodan ta sakawa ranta ne taji kamar Muryar Khalil din oho amma maganar da yayi yanzu ta sake jin muryar tankar ta Khalil din seta bude baki a hankali tace

"Ai munyi magana da Yah Khalil be gaya maka ba?"
"Be gaya mun komai ba, kawai ya turomun da number yace nakiraki shikenan" ya bata amsa.
"Toh ka tambayeshi kaji ze gaya mata yanda mukayi" ta sake fada masa se yayi murmushi yace
"Aa, ai Khalil ya fita daga cikin Maganar mu yanzu ni dakene, ki fada mun komai kanki tsaye karkiji nauyin komai kinji".

Dan Jim tayi kafin tace
"Daman na gayawa Yah Khalil ina da saurayi, sedai kawai in kana so mu zama Abokai se yace Aa, wai na baka 1 week ka gwada Sa'arka, idan kafin satin daya ban fara sonka ba shikenan" tayi shiru

"Idan kuma kika fara so nafa?" Ya tambayeta cikin sigar wasa se ta yi murmushi ba tareda tace komai ba ya sake ce mata
"Hakan ma nagode ni kuma na tabbatar miki kafin cikar wannan wa'adin sena kafa gwamnati na a zuciyarki tunda ina sonki zan kuma yi duk yanda zanyi kema ki soni. Ki saka a ranki kawai kin zama tawa dan satin nan yana cika tofa babu wata sauran magana se kawai na turo iyayena ayi maganar auranmu ba kuma nason ya wuce wata daya kin zama matata".

Shiru kawai tayi tana jin ikon Allah ji wani azarbabi to taji ta gani ai ita dai tasan ba zata taba son wani bayan Noor ba kawai dai zata bata masa lokaci nr sati yacika ya kama gabansa da haka sukayi sallama akan ze sake kiranta.

Wasa wasa a hankali cikin kwana biyu wata irin shaquwa ta shiga tsakaninsu. Rashin lafiyar da Umaimah takeyi ta sake bashi damar samun lokaci da Humairan dan ta koma dakinta na qasa gaba daya bata hawa saman sedai shi ya sauka ya sameta shiyasa ya samu guri yake baje kolin soyayyarsa da yar yarinyar da a hankali ya fuskanci bata san komai ba. Soyayyar da take iqirarin tana yiwa Noor din soyayya ce ta yarinta kawai dan haka yayi amfani da wannan damar ya cusa mata sonsa a ranta ba tareda ta sani ba. Kullum sukanyi waya sau uku sau hudu ko be kirata na zata kirashi ita, Chat kuwa duk sanda ya bude ze tarar da saqonta dukda maganar tasu rabi duk shirmen yarintarta ne wanda yake masa dadi sosai.

Ranar da suka cika kwana shida da yarjejeniya da daddare yana kwance a Falonsa suna waya yake ce mata
"Kinga Gobe wa'adin da kika dibar mun ze cika, dan haka ya kamata ki fada mun sakamakona idan har naci nasara a goben zan bayyana miki kaina, idan kuma banyi nasara ba se in ce miki Allah ya hadamu da Alkhairi, idan mun hadu a Aljanna na gaya miki nine Ibrahim".
Chapter 160 · 0% Book details