← Book details Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 68 OF 267

Sashe 68

Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A wayarta Salisu ya kira Alhaji Auwalu kamar yanda ta bashi umarni tana kuka ya shaida masa Abun tana cikin wani hali aba buqatar kudi da za'ayi belinta, Alhajin ya jajanta musu yace kudinta dubu dari bakwai da Hamsin ne a hannunsa amma yanzu bazasu samu duka ba dan yayi sari, sedai akwai kudin da aka kawo masa yanzu na wasu dubu dari biyar, ze bayar idan yaso saga baya idan dari biyu da hamsin din ta hadu seya ciko musu ya gaya masa inda zeje ya same shi ya karba Salisu ya tafi bayan data gaya masa inda kudin Adashin data dauka suke. Be dade ba ya dawo da kudaden harda Receipt din Sarqar Umaimah yana nan a inda kudin suke gaba daya abinda aka samu dubu dari shida da sha biyar.

Mama ce ta kalli Khalil tace
"Kirawo mun Abokin naka kaji nawa gram din gwal yake yanzu" zeyi magana ta harareshi dole ya kira Bashir ya gaya masa ta bude wayarta ta buga lissafi ta nunawa DPO tana cewa
"Kaga kudin da zata biya nan, ga receipt nan a hannunka ka kuma ji farashin sa a kasuwa ka lissafa ka gani".
DPO ya karbi kudin ya saka akayi rubutu a takadda aka rubuta kudin sarqa da kuma abinda aka samu a hannunta da ragowar cikon da zatayi, Salisu ya nemi Alfarmar dasu barta ta koma gida, shi ze tsaya duk sanda ta samu kudin da kansa ze ringa kaiwa Police station din har a warware amma yana neman alfarmar su bata lokaci dan ta samu ta hada kudin, haka aka rabu DPO ya damqa kudi a hannun Mama nan take ta irge dubu sha biyar din sama ta miqawa Khalil tace

"Na cire kudina dan ni bazan dauki asara na yanda naga kana wani fuskar tausayinta tsaf zaka iya cewa ka yafe to kuje ku qarata in ta biya ku kukuka sani idan ma ta cinye matarka taja maka asara" tana gamawa tayi gaba abinta ta barsu suka qarasa.

Har sukaje gida tana mita da zagin Umaimah da tayi muqus, ita mamaki Maman Nihal ne ya cikata lallai mutum se a barshi.
Har aka kusa cinye sati Mama na mita kafin ta haqura tayi shiru da zancen, Mijin Abu kuwa ya cika alqawari dan da ya ganta da kudi seya san yanda yayi da kanta ba bayar aka kai Police station din, shi kadai yasan ta yanda yake tsoratar da ita kuka kuwa da tsinuwa da Allah ya isa tayi su babu Adadi.

A haka Umaimah taci gaba da jego cikin kulawa ita da yaronta sunyi kyau sunyi bulbul dasu abin sha'awa har suka cinye kwana Arba'in dinsu, ana gobe suyi Arba'in aka aiko da rasuwar Babban Yayansu Abba da suke kira Baban Qaraye dan shi acan yake zaune wannan dalilin yasa ta roqi Khalil akan ya barta suje gaisuwar idan sun dawo seta koma dukda beso ba haka ya haqura dan harga Allah a matse yake, shikadai yasan irin halin da yake ciki na rashinta a kusa dashi kullum cikin Azumi yake. Shi be taba sanin mabuqaci bane bama shi se bayan da yayi aure dukda tun kafin auransa daman yana da buqatar amma saboda ya tsare kansa yana yawan Azumi sannan baya kai idonsa ga kallon abinda ze tayar masa da hankali.

Sunje Qaraye seda akayi sadakar uku suka dawo ta tararda Khalil shi kuma ya tafi Sokoto wani aiki zeyi sati daya dan haka yace tayi amfani da wannan damar taje duk wani gaishe gaishen Arba'in da akeyi kafin ya dawo. Da bangarenta ta fara a kwanaki biyu ta gama zagaya duk inda zataje suka huta kwana biyu kafin Khalifa da kuma Habiba Hajiya ta saka suka ringa yawo da ita nasu dangin suna gaisawa, sun yawata sosai dan har Gaya sda sukaje suka kwana daya suka dawo kuma ranar ne zagayen su na qarshe a sannan saura kwana biyu Khalil ya dawo dan har su Maman Asad sunje sunyi mata shara da gyaran gida ita kuma washe gari zatayi lalle da kitso gyaran jiki ciki da waje kuwa daman sun dade suna yi.

Washe gari da safe Hajiya ta kirata akan idan babu damuwa ta shirya yanzu Khalifa zezo ya kaita gidan Goggo Zahra'u qanwar Mahaifinsu Khalil da shaf ta manta basuje can ba se jiya ta kirata tana qorafin an kaita ko ina a dangi ta gaishe su bada gidanta saboda ita bare ce.
Wadda zatayi mata kitso da lalle ta rigada tazo amma haka ta saka doguwar riga ta dauki Mu'ayyad suka tafi tana ta Mita Mama ta kwabeta.

Goggo Zahra'u ta karbe ta faran faran ta rasa ina zata sakata haka yaranta suka ringa zuwa suna gaisheta ita dai hankalinta yayi ta tafi gida tayi uzurin gabanta, sun kwashe sama da awa daya a gidan sam Umaimah ta kasa taba komai na abinda aka kawo musu ita kuwa Goggon ta qanqame Mu'ayyad tana ta janta da surutu, suna haka tayi baquwa suka gaisa ta zauna take tambayar Goggon wacece Umaimahn tace mata matar Khalil din Yaya Bayero ce seta riqe baki tace

"Oh kinga rabo wani baya haifar dan wani, da yanzu yaron Bariyyah ne"
"Kin rigani a fili ne Hajara ni kaina tun shigowarsu Nake juya yaron nan a raina ina cewa da yanzu na Bariyyah ne, idanda rabo ai seta haifi qannensa" Goggo Zahara'u ta fada tana yar dariya.

Kallonsu Umaimah ta ringayi har suka dire zancensu ji tayi kanta yana juya mata kamar wadda tayi hajijiya, bata manta sunan nan ba Bariyyah, tsohuwar budurwar Khalil cousin dinsa daman nan ne gidan su shine saboda rashin mutunchi za'a ce tazo ta gaishe su lallai ai kuwa yau zasuga qarshen rashin mutunchi kuwa se sun gane ita din ba kanwar lasa bace. Maganar da baquwar ta sakeyi tace

"Ai dai wallahi duk munso hadin Allah ne beyi ba da kuma rabo amma yanzu kinga se azo a sasanta kuma zamanku zakuyi lafiya lau dan naganki kema shiru babu ruwanki kamar Bariyyan" Baquwar ta fada tana kallon Umaimah

"Sedai mu zauna da kutumar uban Bariyyah, ni za'ayi wa rashin mutunchi ace nazo na gaishe ku sannan ku sakani a gaba kuna kawo mun zancen wata kucaka karuwa da taqi auruwa wai na hada miji da ita to wanda be fasa ba, ba ita ba harke uwarta se kin saka kanki a masifa da bala'in da baki zata ba wallahi aikin banza kawai" Umaimah ta fada kafin ta miqe ta fizge Mu'ayyad dake hannunta tayi waje, a bakin qofar suka ci karo da wadda take da tabbacin ita ce Badariyyan dan ance tana Islamiyya ganin mace ta shigo da Uniform ba tayi wata wata ba ta kwasheta da mari tace
"Wallahi ko inuwar mijina kika kalla se nayi Ajalinki ballantana ki saka tunanin hada miji dani a ranki banza garwa kawai" taja tsaki ta fice.

Khalifa na qofar gidan dan tuni ya gaji da soki burutsun Goggon tasu ya fita ya barsu se ganinta yayi kamar an jefota ta bude motar ta shiga tana huci dan haka yabi bayanta shima ya shiga ya tayar da motar, sau daya ya tambayeta meya faru tayi shiru bata amsa masa ba daga nan shima ya kama kansa be kuma ce mata komai ba har suka isa gida ya ajiyeta ta fice daga motar ba tareda ta rufe ba jakar goyon Mu'ayyad ma se shi ya bita ciki dasu.

Tana shiga kai tsaye dakin da take ta shiga ta ajiye Mu'ayyad akan gado, safa da marwa ta shigayi a dakin ji takeyi tamkar zuciyarta zata fashe saboda zafin da takeyi mata idan ta tuna maganganunsu se taji kamar ta koma ta shaqe su duk su biyun har se sun dena numfashi wai me ma ya saka ta taho ba tareda ta lallasa su ba amma ba laifinsu bane, laifin Hajiyar da tace taje ta gaishe su ne daman sun san rashin mutunchin da suka shirya shine za'ace taje ita gaishe su?

Wayarta ta janyo ta shiga kiran Khalil, tana so taji dalilin turata a wulaqantata da sukayi sedai tayi Rashin sa'a wayar a kashe.
Mama data gaji da kiran Umaiman tun shigowarta ta bita dakin tana cewa
"Lafiyarki kin shigo ana magana kinyi banza da mutane kin wuce, sannan tun dazu ake kiranki a waya kun tafi kunyi zamanku ko kin manta da kin bar mata tana zaman jiranki"

"Ni Mama ta tafi na fasa bazanyi lallenba" ta fada ba tareda ta kalli Maman ba, se Mama ta qarasa shiga dakin tana kallonta tace
"Uhm, fadan kukayi ko? To ki wuce tun muna shaida juna kije ayi miki abinda za'ayi miki kafin ranki ya baci yanzun nan"

Kuka ta fasa mata tana cewa
"Ni wallahi bazanyi ba, gidan ma bazan koma ba se yaje ya auro yar uwar tasa ya sakata a gidan ai amma ni na gama zama dashi"
Baki Mama ta bude tana kallonta har ta gama kafin tace
"Allah ya rufa asiri" ta juya abinta.

A can gidan Goggo Zahara'u kuwa daga ita har baquwarta kasa motsi sukayi har Umaimah ta gama tijararta ta fice ta barsu, qarar mari da Kukan Bariyya ne ya dawo dasu daga gajeran suman da sukayi suka zabura gaba daya sedai kafin su kai qofa Umaimah ta fice daga gidan.

"Zara'u wannan wace irin tijararriyar yarinya ce kinga tashin hankali daga magana se cibi ya zama qari har ta bi yarinya da tukuicin Mari gaskiya karki bar maganar nan gara ki kira Yaya Aishan ki gaya mata abinda surukarta tayi" Baquwarta ta fada tana kama baki,

"Wa ai fada ma bata baki yanzu kuwa zan kirata da take zagin Bariyyah tana kiranta mara tarbiyya ai ga qarshen rashin tarbiyya nan matar danta tazo ta mana, kuma wallahi bata daki banza ba auren Khalil da Bariyyah kuwa idan taga ba'ayi ba toh kice bana numfashi" Goggo Zahara'u ta fada tana numfarfashi nan take ta kira Hajiyar su Khalil a waya ta shiga tsara mata qarya da gaskiya wai Umaiman tazo tayi musu cin mutunchi ta daki Badariyyah dakyar aka kwaceta,
Chapter 68 · 0% Book details