Sashe 224
Rawanin Zalinci Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsayawa ya yi a gaban windown room ɗinsa dake fuskantar harabar family part, kalaman Smart ne kawai suke yi mashi yawo a ransa, ta wani ɓangare na zuciyarsa kuma rashin Zunaira, ta ko'ina ba sauki, babban abin da ya fi ɗaga mashi hankali shi ne kamar yadda Smart ya ce sai ya faɗa mashi uwar Ramish, to abin tashin hankalin a nan ne shi ne allura ce take shirin tono jibgegiyar garma mai girman gaske, domin kuwa ba faɗar uwar Ramish ɗin ne matsala ba, matslar shi ne ya aka yi ya baiwa mama Ramish a matsayin ɗanta ita kuma bata san ba nata bane? Wannan shi ne ainahin tashin hankali da yake ciki, dan tono yadda aka yi ya bata Ramish babban bala'i ne ga gabaɗaya kingdom ɗin wanda sai ta shafi kowa da kowa, idan Smart ɗin ma bai yi hankali ba zata zama sanadiyar mutuwarsa ko na mommarsa or guyson, dama shi guyson a kan hanya yake, taimakon Allah yasa bai mutu ba yake fama da ciwon ciki mai zuwa dik shekara kenan, wannan ba karamar bala'i bace, gara ma sanin me yake a tsakaninsa da matar commander a kan wancan bala'i na Ramish, siririn da a ka rufe tsawon shekaru 30 amma Smart ko daga ina ya jiyo sirrin har ya bankaɗo shi?. WANNAN SMART SAI DAI SHIRIN ALLAH, YA TAYARWA DA DATTIJO HANKALI YA BARSA CIKIN CIWO DA AZABA!!
Haƙiƙa King ya shiga tashin hankalin da bai san ranar fita ba. Batu a kan maman Hoorain wato matar commander wannan tabbas suna da alaƙa, kai tin ba yau ba, tin kafin King ya yi aure suke tare, bari in maku tarihin, sun sha soyayya nakin karawa, saboda matar commander uwarta baturiya ce ubanta balarabe, shiyasa ta fita daban a masarautar, sai dai kuma tana matsayin baiwarsu, King Zuhair ya kamu da sonta sosai, yadda kuka ga Auta ta so Hoorain, haka suma suka so juna, sai dai kash, King Abdul Malik ya ce ko mutuwa King yake yi ba zai taɓa aurar baiwa ba, ya haramta masu mallakan juna, wannan dalilin yasa suka kasance a tare a bayan fage, suka rinƙa sheke ayarsu har King Abdul Malik ya fitar mashi da mata, wato da Mummyn Chuchu da Mamansu Aneesa, bai yi gardama dik da cewa baya sonsu ba, dan shi ai yana tare da wacce yake so a ɓoye.
Aka aura mashi su, ya cigaba da kasancewa da matar commander har ita ma ta yi aure, tsantsar soyayyar da suke yi wa junansu yasa suka gagara rabuwa dik da suka yi aure, haka suka cigaba da rayuwa har shigowar momma rayuwarsa a wani zuwa Dubai da ya yi, already Mummyn Chuchu and maman Aneesa ba zaɓinsa bane, shiyasa kuka ga ya fin san momma sama da su, dan ita ce zaɓinsa ta biyu bayan maman Hoorain. Maman Hoorain da suka yi aure ba'a cikin kingdom of power suke zaune da commander ba, amma dik da haka suna da wajen da suka ware wanda suke haɗuwa ita da King dan holewarsu.
A takaice lokacin da ya auri momma ta fahimci yana daga cikin sarakuna masu tarewa da kuyangunsu, shiyasa ta yi ƙoƙarin canzasa, kuma ta yi nasara, dan ta canzasa a lokacin da bai taɓa zata ba, a lokacin momma har ta haifi Jaish, lokacin ita kuma matar commander ta haifi Hoorain bai wuci 2 years ba a duniya, a ranar da za'a haifi Hoorain anyi gagarumin yakin da a ranar ne aka kashe King Abdul Malik, lokacin da maman Hoorain da maman Aneesa suna naƙuda, ranar anyi tashin hankali sosai. Bayan komai ya lafa aka yi jana'izar King Abdul Malik kamar yadda yake a dokar sarauta, daga nan King Zuhair ya karɓi karagar mulki, momma ta yi nasarar raba shi da matar commander, tin daga lokacin kuma ya tuba ya zama adalin sarki mai mulki tsakani da Allah, sai dai matsalar da aka sake samu a ɗan gaba kaɗan kafin matar commander ta ɓata da kuma bayan ta ɓata, wannan matsala lokacin da zaku san shi bai ba, dan wannan matsala shi ne yake da alaƙa da Ramish da kuma yaudarar mama da King ya yi, WANNAN SHI NE GASKIYAR ABIN DA YAKE A TSAKANIN KING AND MATAR COMMANDER ZAFAR, TO YANZU A TSAKANIN KING DA COMMANDER WANENE AINAHIN UBAN MARIGAYI HOORAIN? KAM BALA'IN CAN!! UHM WANNAN CAKWAKIYA SAI SMART YA WARWARE MANA! DAN KO SHI KANSA KING ƊIN BAN JIN YANA DA TABBACIN HOORAIN ƊANSA NE KO NA COMMANDER, ITA KANTA MATAR COMMANDER ƊIN BANA JIN TASAN AINAHIN UBANSA, WANNAN SHI NE KWAMACALA. KU DAI MU CIGABA DA ZUWA, AI KWAMACALA MA TANA CAN GABA!!
Hege Smart ya jefa King da kansa a cikin zulumi da tashin hankali shi kuwa yana can yana more rayuwarsa da Pretty, sai nishaɗi suke yi, ga King ya ƙasa zaune ya kasa tsaye, wlh tin da kuka ga King ya girgiza a kan batun Ramish, ba shakka ba karamar ɓarna bace zata bayyana, babban bala'i Smart yake son jijjigo mana wanda gara kowani irin cakwakiyar a littafin nan a kan wannan, tabbas King Zuhair and King Abdul Malik sun bar baya da kura, abin sai shiru, sai lokaci ya nuna mana kawai!!. ZAN BAKU MAMAKI FA, DAMA SUNANANE QUEEN OF SURPRISE, KU YI FATAN BAYYANAR KAMRAN LAFIYA KU DAI!!
----------------------------------------------🔥🔥🔥
"Azumi fa akwai lada, idan kika yi zaki samu lada sosai, kuma waye ya ce maki ana wahala a azumi?". Ya yi tambayar yana ajiye wayarsa a gefe, sannan yasa hannu ya rungumota da kyau. Kai ta shiga girgiza mashi. "Ni ko akwai ladan tin da akwai yunwa bana so, ni ba zan yi ba". "Ɗago kanki ki kalleni". Ya faɗa yana tattare dark black curly hairnta da ya zubo ta gaba ya tufe mata fuska, tattare mata ya yi ya tara a baya, sannan ya riko haɓarta da hannunsa ɗaya yana kallan face ɗinta, dik ta yi jaga jaga da hawaye!.
"Idan kika yi azumi zuwa dare zan saya maki su chocolate dayawa". Sarkin son zaki, kowa ya san halinta sha zuma ce......... "Ni dai kawai idan zaka saya mun saboda Allah haka ka bani to, idan kuma sai na yi azumi ne na hakura ka riƙe kayanka". Ta faɗa tana ƙoƙarin sake fashewa da kuka. .......... "To ya isa haka, yanzu mu je mu ci abinci kafin mu yi batu a kan azumi........." Bai iya ƙarisa maganar ba ya dakata sakamakon wani irin shock da ya ji na saukar hannunta a saman mararsa, a fujaje ya waro idanunsa sosai a kanta, turo mashi baki ta yi, ita a tinaninta jiran amsarta yake yi, bata ɗauki taɓa mashi cibiya da take yi a wani abu ba, sai ta ce. "Ni fa koma me za'ayi ba zan yi azumin nan ba, dan ba zan zauna da yunwa ba". Tana magana tana sake turo baki.
Nisawa ya ɗan yi tare da rakwafo da kansa kaɗan a kanta, kamar mai san raɗa mata magana a kunne, cikin dabara ya haɗe fuskokinsu tare da capke lips ɗinta na ƙasa ya fara tsotsa. Zaro mashi idanu ta yi wanda sai da tasa ya kara jin tsikar jikinsa yana tashi, hannu bibbiyu tasa tana ƙoƙarin tureshi ya sakar mata baki, shi kuwa ya kara riketa da kyau, tirgewa ta fara yi tana mutsu mutsu zata kwace kanta, ina ai yaki bata dama sai da ya yi kissing ɗinta da kyau, sannan ya saketa tare da jingina kansa da jikin headboards na bed ɗin. Ita kuwa kuka ta saka tare da barin jikinsa, hannayenta bibbiyu tasa ta fara goge bakinta wai yasa mata datti kuma yawunsa babu daɗi dan babu zaƙi ita ga sha zuma, zaki kawai take martabawa.
Bilhakki da gaskiyarta take kuka tana ta dirza ɗan bakinta wai tana goge in da nasa ya taɓa mata, sai tufar da yawu take yi, waje ta nufa da gudu, sam bai ji fitarta ba. Kai tsaye ta wuce wajen momma, tana zuwa ta faɗa jikinta tare da sanya mata kuka mai sauti, har lokacin mom tana wajen suna a tare. Da yake momma tasan hali, sakalcin Pretty ya wuci tinani, sai ta ce mata. "Ke da waye kuma babyn Yah Omerish? Yau ba'a kai mashi kara ba sai aka kawo mun?". Momma bata san yau shi ya yi laifi ba, yau kararsa aka kawo ba na mutane da aka saba kawowa or kai mashi ba.
Ita dai momma ba ruwanta, ta fita daban, dama a ko'ina akwai na kirki dana banza, ita dai bata nuna kabilanci da kyamar wasu da ba nasu ba, kowa nata ne da hannun bibbiyu take rungumesa!!.
Cikin kuka ta ce. "Momma Yah Omerish ne ya sa bakinsa a cikin nawa, kuma yasa mun yawunsa da babu zaki babu daɗi a cikin nawa, ya kuma sha mun nan". Ta kai karshen maganar tana nuna lips ɗinta da hannu!. Ajiyar zuciya momma ta sauke, dama tasan za'a yi hakan one day one time, saboda su jaraba gadonta suka yi, ita kuma Pretty ga ɗan banzan kyau kamar ita ta yi kanta, ai keɓewarsu waje guda abu ne mai haɗari sosai, shiyasa take ta lallaɓa Smart ɗin ya aureta kawai sai ayi dik wacce za'ayi, wlh ita Momma ta san cewa Smart yana bala'i kaunar Pretty, dan kuwa ita ce mace ta farko bayan ita da mom ɗinsa and Auta da taɓa shiga rayuwarsa har ta zauna kusa da shi, abin gaskiya yakamata ta ɗauki mataki.
Tana can tana tinani sai ji ta yi Pretty ta miƙe zata bar jikinta tana faɗin. "Bari in je in faɗawa Zunaira abin da Yah Omerish ya yi mun"..... Ita fa Pretty bata ma san dik gurmin da ake yi a kan Auta ta mutu ba, dan tana waya da ita idan ta je wajen Smart, so dik bala'in da ake yi a kingdom ɗin ko a slippers ɗinta, hankalinta a kwance..
Haƙiƙa King ya shiga tashin hankalin da bai san ranar fita ba. Batu a kan maman Hoorain wato matar commander wannan tabbas suna da alaƙa, kai tin ba yau ba, tin kafin King ya yi aure suke tare, bari in maku tarihin, sun sha soyayya nakin karawa, saboda matar commander uwarta baturiya ce ubanta balarabe, shiyasa ta fita daban a masarautar, sai dai kuma tana matsayin baiwarsu, King Zuhair ya kamu da sonta sosai, yadda kuka ga Auta ta so Hoorain, haka suma suka so juna, sai dai kash, King Abdul Malik ya ce ko mutuwa King yake yi ba zai taɓa aurar baiwa ba, ya haramta masu mallakan juna, wannan dalilin yasa suka kasance a tare a bayan fage, suka rinƙa sheke ayarsu har King Abdul Malik ya fitar mashi da mata, wato da Mummyn Chuchu da Mamansu Aneesa, bai yi gardama dik da cewa baya sonsu ba, dan shi ai yana tare da wacce yake so a ɓoye.
Aka aura mashi su, ya cigaba da kasancewa da matar commander har ita ma ta yi aure, tsantsar soyayyar da suke yi wa junansu yasa suka gagara rabuwa dik da suka yi aure, haka suka cigaba da rayuwa har shigowar momma rayuwarsa a wani zuwa Dubai da ya yi, already Mummyn Chuchu and maman Aneesa ba zaɓinsa bane, shiyasa kuka ga ya fin san momma sama da su, dan ita ce zaɓinsa ta biyu bayan maman Hoorain. Maman Hoorain da suka yi aure ba'a cikin kingdom of power suke zaune da commander ba, amma dik da haka suna da wajen da suka ware wanda suke haɗuwa ita da King dan holewarsu.
A takaice lokacin da ya auri momma ta fahimci yana daga cikin sarakuna masu tarewa da kuyangunsu, shiyasa ta yi ƙoƙarin canzasa, kuma ta yi nasara, dan ta canzasa a lokacin da bai taɓa zata ba, a lokacin momma har ta haifi Jaish, lokacin ita kuma matar commander ta haifi Hoorain bai wuci 2 years ba a duniya, a ranar da za'a haifi Hoorain anyi gagarumin yakin da a ranar ne aka kashe King Abdul Malik, lokacin da maman Hoorain da maman Aneesa suna naƙuda, ranar anyi tashin hankali sosai. Bayan komai ya lafa aka yi jana'izar King Abdul Malik kamar yadda yake a dokar sarauta, daga nan King Zuhair ya karɓi karagar mulki, momma ta yi nasarar raba shi da matar commander, tin daga lokacin kuma ya tuba ya zama adalin sarki mai mulki tsakani da Allah, sai dai matsalar da aka sake samu a ɗan gaba kaɗan kafin matar commander ta ɓata da kuma bayan ta ɓata, wannan matsala lokacin da zaku san shi bai ba, dan wannan matsala shi ne yake da alaƙa da Ramish da kuma yaudarar mama da King ya yi, WANNAN SHI NE GASKIYAR ABIN DA YAKE A TSAKANIN KING AND MATAR COMMANDER ZAFAR, TO YANZU A TSAKANIN KING DA COMMANDER WANENE AINAHIN UBAN MARIGAYI HOORAIN? KAM BALA'IN CAN!! UHM WANNAN CAKWAKIYA SAI SMART YA WARWARE MANA! DAN KO SHI KANSA KING ƊIN BAN JIN YANA DA TABBACIN HOORAIN ƊANSA NE KO NA COMMANDER, ITA KANTA MATAR COMMANDER ƊIN BANA JIN TASAN AINAHIN UBANSA, WANNAN SHI NE KWAMACALA. KU DAI MU CIGABA DA ZUWA, AI KWAMACALA MA TANA CAN GABA!!
Hege Smart ya jefa King da kansa a cikin zulumi da tashin hankali shi kuwa yana can yana more rayuwarsa da Pretty, sai nishaɗi suke yi, ga King ya ƙasa zaune ya kasa tsaye, wlh tin da kuka ga King ya girgiza a kan batun Ramish, ba shakka ba karamar ɓarna bace zata bayyana, babban bala'i Smart yake son jijjigo mana wanda gara kowani irin cakwakiyar a littafin nan a kan wannan, tabbas King Zuhair and King Abdul Malik sun bar baya da kura, abin sai shiru, sai lokaci ya nuna mana kawai!!. ZAN BAKU MAMAKI FA, DAMA SUNANANE QUEEN OF SURPRISE, KU YI FATAN BAYYANAR KAMRAN LAFIYA KU DAI!!
----------------------------------------------🔥🔥🔥
"Azumi fa akwai lada, idan kika yi zaki samu lada sosai, kuma waye ya ce maki ana wahala a azumi?". Ya yi tambayar yana ajiye wayarsa a gefe, sannan yasa hannu ya rungumota da kyau. Kai ta shiga girgiza mashi. "Ni ko akwai ladan tin da akwai yunwa bana so, ni ba zan yi ba". "Ɗago kanki ki kalleni". Ya faɗa yana tattare dark black curly hairnta da ya zubo ta gaba ya tufe mata fuska, tattare mata ya yi ya tara a baya, sannan ya riko haɓarta da hannunsa ɗaya yana kallan face ɗinta, dik ta yi jaga jaga da hawaye!.
"Idan kika yi azumi zuwa dare zan saya maki su chocolate dayawa". Sarkin son zaki, kowa ya san halinta sha zuma ce......... "Ni dai kawai idan zaka saya mun saboda Allah haka ka bani to, idan kuma sai na yi azumi ne na hakura ka riƙe kayanka". Ta faɗa tana ƙoƙarin sake fashewa da kuka. .......... "To ya isa haka, yanzu mu je mu ci abinci kafin mu yi batu a kan azumi........." Bai iya ƙarisa maganar ba ya dakata sakamakon wani irin shock da ya ji na saukar hannunta a saman mararsa, a fujaje ya waro idanunsa sosai a kanta, turo mashi baki ta yi, ita a tinaninta jiran amsarta yake yi, bata ɗauki taɓa mashi cibiya da take yi a wani abu ba, sai ta ce. "Ni fa koma me za'ayi ba zan yi azumin nan ba, dan ba zan zauna da yunwa ba". Tana magana tana sake turo baki.
Nisawa ya ɗan yi tare da rakwafo da kansa kaɗan a kanta, kamar mai san raɗa mata magana a kunne, cikin dabara ya haɗe fuskokinsu tare da capke lips ɗinta na ƙasa ya fara tsotsa. Zaro mashi idanu ta yi wanda sai da tasa ya kara jin tsikar jikinsa yana tashi, hannu bibbiyu tasa tana ƙoƙarin tureshi ya sakar mata baki, shi kuwa ya kara riketa da kyau, tirgewa ta fara yi tana mutsu mutsu zata kwace kanta, ina ai yaki bata dama sai da ya yi kissing ɗinta da kyau, sannan ya saketa tare da jingina kansa da jikin headboards na bed ɗin. Ita kuwa kuka ta saka tare da barin jikinsa, hannayenta bibbiyu tasa ta fara goge bakinta wai yasa mata datti kuma yawunsa babu daɗi dan babu zaƙi ita ga sha zuma, zaki kawai take martabawa.
Bilhakki da gaskiyarta take kuka tana ta dirza ɗan bakinta wai tana goge in da nasa ya taɓa mata, sai tufar da yawu take yi, waje ta nufa da gudu, sam bai ji fitarta ba. Kai tsaye ta wuce wajen momma, tana zuwa ta faɗa jikinta tare da sanya mata kuka mai sauti, har lokacin mom tana wajen suna a tare. Da yake momma tasan hali, sakalcin Pretty ya wuci tinani, sai ta ce mata. "Ke da waye kuma babyn Yah Omerish? Yau ba'a kai mashi kara ba sai aka kawo mun?". Momma bata san yau shi ya yi laifi ba, yau kararsa aka kawo ba na mutane da aka saba kawowa or kai mashi ba.
Ita dai momma ba ruwanta, ta fita daban, dama a ko'ina akwai na kirki dana banza, ita dai bata nuna kabilanci da kyamar wasu da ba nasu ba, kowa nata ne da hannun bibbiyu take rungumesa!!.
Cikin kuka ta ce. "Momma Yah Omerish ne ya sa bakinsa a cikin nawa, kuma yasa mun yawunsa da babu zaki babu daɗi a cikin nawa, ya kuma sha mun nan". Ta kai karshen maganar tana nuna lips ɗinta da hannu!. Ajiyar zuciya momma ta sauke, dama tasan za'a yi hakan one day one time, saboda su jaraba gadonta suka yi, ita kuma Pretty ga ɗan banzan kyau kamar ita ta yi kanta, ai keɓewarsu waje guda abu ne mai haɗari sosai, shiyasa take ta lallaɓa Smart ɗin ya aureta kawai sai ayi dik wacce za'ayi, wlh ita Momma ta san cewa Smart yana bala'i kaunar Pretty, dan kuwa ita ce mace ta farko bayan ita da mom ɗinsa and Auta da taɓa shiga rayuwarsa har ta zauna kusa da shi, abin gaskiya yakamata ta ɗauki mataki.
Tana can tana tinani sai ji ta yi Pretty ta miƙe zata bar jikinta tana faɗin. "Bari in je in faɗawa Zunaira abin da Yah Omerish ya yi mun"..... Ita fa Pretty bata ma san dik gurmin da ake yi a kan Auta ta mutu ba, dan tana waya da ita idan ta je wajen Smart, so dik bala'in da ake yi a kingdom ɗin ko a slippers ɗinta, hankalinta a kwance..