Sashe 24
Binteee Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
.......Zaitun zama tayi kan tabarmin nan bayan ta kwantar da su batare da ta warware su ba ta zubawa ttitin idanu wanda zuwa lokacin daidaikun motoci ke wucewa har suka zo suka daina wucewan ma gari yayi 'dib, ko'ina shiru kake ji, tana nan tana tunanin duniya tana tunanin irin tata kalar rayuwar, ada kafin Mufee ta shigo rayuwar ta ba haka komai yake tafiya mata ba, amma tun daga ranar da 'kaddarar Mufee ta same ta shikenan rayuwar ta ta canza salo...amma har yau 'din nan har yanzu da take zaune bakin titin bata ji tana danasanin kasancewa da yarinyar ba, bata sani ba, bata kuma san dalili ba amma tana ji har cikin ranta cewa duk rintsi duk tsananin wuya tana tare da yarinyar...tasan jarrabawa ce ta yiwu kuma alhaki ce ta wata fannin, amma Insha Allahu zata jure zata daure komai da zai sameta, tasan dole inda rai watarana Allah zai dube su, Allah zai yaye musu wannan kuncin suma suyi farin ciki.
A kullun adduar ta shine ko da allah yasa rayuwar ta gajera ce to ya sada Mufeeda da ingantacciyar rayuwa inda zatai farin ciki inda za'a kula mata da ita tunda ita ta gaza sama mata farin cikin.
Sosai ta zurfafa a tunani har bata san tana 'kwalla ba, bata kuma san da wanzuwar wasu matasan samari har guda uku ba tsaye a kanta, irin street boys din nan ne fitsararru marasa imani.
Tsaye suke kowa na kallon ta ta hasken da farin watan ke haskawa.
Motsin da Mufeeda tayi ne ya dawo da ita hayyacin ta, hannu ta kai ta share hawayen fuskar ta da ta fahimci ya jike, yayin da 'daya hannun ta kai bayan ta tana bubbuga bayan Mufee alamar rarrashi.
Cire hannun da ke kan idanun nata ke da wuya sai taga tamkar tsayuwar mutun a gaban ta sake goge idanun tayi gami da waro su dan tabbatar da abinda idanun suka gani tabbas mutun ne rungume da hannun sa a kirjin sa tsaye jingine da Pillarn Varandar ya kwantar da kansa jikin pillar.
Da gaske Mutun ne ba ma 'daya ba har su uku jere suna kallon ta.
Zabura tayi kamar zata tashi amma yadda tsoro ya riga ya karya mata zuciya haka taji kafafun ta ma sun karye sunyi sanyi sun gaza daukan nauyin ta.
Dur'kushewa tayi kan gwiwoyin ta ta saki kuka mai tsuma zuciya hannayen ta duk biyu ta kai kan bakin ta tana kuka wanda duk rashin imanin ka daka ji sa kasan cewa abin a tausaya wa ce a lokacin, domin cike da rauni take kukan gami shashsheka duk zaton ta mutanen Hajjaju ne suka biyo bayan ta, dan haka cikin kukan ta fara rokon su..." dan Allah kuji kaina bayin Allah, ku dubi girman Allah da manzon sa ku rabu da mu, wlh yarinyar nan marainiya ce, in kuka rabani da ita bazan taba jin dadi ba dan Allah ku bar mu muyi tafiyar mu, na muku alkawari Insha Allahu bazan sake waiwayar gidan Hajjaju ba har abada.."
Babu wanda yace mata ko _'kala_ cikin samarin nan uku illah 'daya cikin su da ya 'daga siraran 'kafafun sa ya matso gaban ta, ya tsaya a saitin kanta, tsabar tsoro Zaitun rintse idanu tayi da karfi take fadin" Dan Allah kar ku rabani da ita, dan Allah ku bar min yarinya ta, kuji tausayin mu bayin Allah..."
Dukkanin ilahirin jikin Zaitun rawa yake.
_Fiiit.._ taji an fizge mata Hijab a bazata daga kanta...wani zabura ta sake yi da niyyar yin baya take ta bude idanun ta...nan taga ashe har duk su ukun sun matso kusa da ita sun gewaye ta..." BK bayan ta goyo fa...?"
Karo na faro da 'daya daga cikin su yayi magana.
Wanda aka kira da BK 'din ne da wata kalar murya irin ta 'yan 'kwaya yace " ta kwance mana...in kuma bazata iya ba a kwance mata...".
Jin hakan yasa Zaitun tayi wani kukan kura ta zabura zata gudu ta tsakanin su, da sauri wanda ke daga bayan ta ya rike mata hannaye duk biyu wanda hakan yasa ta kasa guduwan kamar yadda tayi niyya, 'daya mai suna BK 'din ne ya sa hannu ya kwance goyon ta gaban ta, jin Mufeeda na shirin fa'di ne ya sanya ta 'dan gwada yunkurin fizgan jikin ta daga hannun mutumin amma ta kasa, zuwa lokacin kuwa tsab kukan ta ya tsaya hawayen ma tuni ta neme su ta rasa tuni zuciyar ta bushe, bata kuma sake yunkurin rokon su ba dan ta lura ba fahimtar rokon nata suke ba.
Ganin da suka yi tana musu fizge- fizge ya sa 'daya daga cikin su rike mata 'kafafu yayin da Bk da ke tsaye kanta ya sauke mata wata lafiyayyar mari, sosai marin ya shige dan har jini sai da yan 'dan fito daga hancin ta amma duk da hakan bata bar fizge- fizgen ba, so take ta gwada iya iyawar ta ko Allah ze taimake ta ta iya tseratar da su dan har yanzu a tunanin ta mutanen Hajjaju ne.
Fizgo Mufee wanda ke bayan tan yayi wanda hakan ya firgita yarinyar har yasa ta sakin kuka mai karfi a razane.
Kukan Feefy shi ya dawo wa Zaitun da nata hawayen, dagaske ta tsorata cin sun cire mata yarinyar a bayan ta, bata fatan wannan ya kasance shine karshen ganin ta da Mufeeda.
Take ya dangwarar da yarinyar gefe ya kuma sa hannu ya farke bayan rigar Zaitun 'din daga sama har 'kasa batare da yayi la'akari da Zip da rigar ke dauke da shi ba.. nan take kuwa ya raba rigar biyu wanda jin haka ne yasa Zaitun dawo da hankalin ta waje ta guda sa6anin da data raba dan kula da yadda zasu yi mata da yarinya.
Fahimtar abinda mutanen nan ke nufi ya sanya ta jin mafi girman tsoro ya shige ta, yau ka'dai taga illar kwanan titi.
Iya kokari tayi wajen ganin ta kwaci kanta amma abin ya gagara kawai sai ta saki kuka, irin kukan nan mai cin zuciya, kuka na rashin mafita, cikin ranta take rokon Allah tseratar da ita ya tseratar da su baki 'daya...
Wanda ke tsaye daga bayan tan ne ya fisgi hannayen ta baya da nufin kwantar da ita sai akayi rashin sa'a 'kafar sa ta bige Mufeeda take ta 'karawa kukan ta volume lokaci guda tamkar wanda a gutsiri wani sashe daga jikin ta, karan da ya ratsa kaf kewayan wajen baki 'daya, dai-dai tahowan wata ba'kar mota da gudu ta wuce musamman da yake babu kowa sai su kadai so babu wata mota da zatai musu shamaki da gudun da suke shararawa....har motar ta gota sai kuma ya tsaya cak....
_Salmerh_ 😘
[20/9/2022, 12:32 pm] Author...🖊️: 💕 *BINTEE*💕
*( 'Yata ce)*
*Salmerh MD*
🅿️ *...16*
_Shiiit_ ...shine abin da ya bayyana daga sautin muryar sa at same time yana me bugan sitiyarin motar da hannun sa 'daya...da alamu bai so tsayawan ba...amma kunnen sa sun jiye masa kukan yarinya 'karama.
Baya ya dawo da motar ya bu'de ya fito, sai a sannan ma yaji ashe ba yarinya kadai ke kuka ba har da wata mace sakamakon jiyo sauti bibbiyu da yayi.
Da hanzari ya nufi inda suke domin yana iya hangosu daga inda yake tsayen, dai dai lokacin ne kuma wadannan matasan suka tarwatse kowa yayi hanyar sa, bai bi ta kansu ba hankalin sa na ga mata da yarinyar da ya gani durkushe a wurin ne yake kuma jiyo kukan su, lokaci 'daya 'kwa'kwalwar sa ta basa abinda ke shirin faruwa a wurin duba ya yadda yaga duk sun hargitse riga a rabe, wanda ga dukkan alamu kiris ya rage mai afkuwa ta afku in ba dan ikon Allah da ya kawo su ba.
Baya baya ta fara ja tana me sake sakin kuka sbd a halin nan da take ciki bata iya banbance mugu da wanda yake sa6anin haka.
"....Dan Allah!... dan Allah..."
Take ta fadi batare da ta iya karasa abinda take da niyyan furtawa ba.
Ganin kamar shima tsoron sa take yasa shi daka mata tsawa" _Nutsu da Allah..._ "!
'Dif Zaitun ta shanye kukan ta tare da rintse idanu da karfin gaske.
Batare da yasan wace ba ya jefa mata tambaya yana me kokarin kare ma fuskar ta kallo"..Me kk yi waje da wannan uban daren..?"
Shiru ba amsa illa baya da ta kara saurin matsawa sakamakon tsawar da ya sake mata, gaba 'daya ta firgice.
Jin ta iso kusa da Mufee yasa tai saurin rarumo ta ta gurme ta tamkar zata maida ta cikin ta...
Ido ya tsura mata cike da mamaki wanda sai alokacin ma ya fahimci wace ita gami da tunano inda ya santa, in bai manta ba ya ga wannan fuskar tare da wannan 'yar yarinyar a mabanbantan wurare har sau biyu.
...Ido ya 'dan zaro cike da mamaki yana nuna ta yatsa"...You!..what ar u doing here?..ina zaki je da wannan lokacin?"
Zaitun dai ba fahimtar sa take ba dan har a lkcn bata dawo hayyacin ta ba, d fact that za'a raba ta da Feefy da kuma fyaden da aka so yi mata shine ka'dai ya tsaye mata.
Hijab 'din ta dake yashe gefen kafarcsa ya dauka ya jefe mata.." sa mayafin ki..".
Ya fa'da da murya mai 'dan sanyi..hakan ne ya sa ta lalu6i abinda taji ya jefa matan ta suturta jikin ta da shi, ita kanta tafi son hakan duk da yake tana cikin yanayi na rudu amma data suturta jikin nata sai ta dan ji dama..kuma har a wannan lokacin bata bude ido ba balle ta ga wanda ke mata maganar.
Fatan ta kawai shine taji yayi tafiyar sa shima batare da ya cutar da ita ko Mufeeda ba.
Muryar da take ji nayi mata maganr yai mata kama da wata murya da ta ta6a ji sai dai a a wannan halin bata da nutsuwar iya tuna inda ta san muryar bazata iya tunawa ba.
A kullun adduar ta shine ko da allah yasa rayuwar ta gajera ce to ya sada Mufeeda da ingantacciyar rayuwa inda zatai farin ciki inda za'a kula mata da ita tunda ita ta gaza sama mata farin cikin.
Sosai ta zurfafa a tunani har bata san tana 'kwalla ba, bata kuma san da wanzuwar wasu matasan samari har guda uku ba tsaye a kanta, irin street boys din nan ne fitsararru marasa imani.
Tsaye suke kowa na kallon ta ta hasken da farin watan ke haskawa.
Motsin da Mufeeda tayi ne ya dawo da ita hayyacin ta, hannu ta kai ta share hawayen fuskar ta da ta fahimci ya jike, yayin da 'daya hannun ta kai bayan ta tana bubbuga bayan Mufee alamar rarrashi.
Cire hannun da ke kan idanun nata ke da wuya sai taga tamkar tsayuwar mutun a gaban ta sake goge idanun tayi gami da waro su dan tabbatar da abinda idanun suka gani tabbas mutun ne rungume da hannun sa a kirjin sa tsaye jingine da Pillarn Varandar ya kwantar da kansa jikin pillar.
Da gaske Mutun ne ba ma 'daya ba har su uku jere suna kallon ta.
Zabura tayi kamar zata tashi amma yadda tsoro ya riga ya karya mata zuciya haka taji kafafun ta ma sun karye sunyi sanyi sun gaza daukan nauyin ta.
Dur'kushewa tayi kan gwiwoyin ta ta saki kuka mai tsuma zuciya hannayen ta duk biyu ta kai kan bakin ta tana kuka wanda duk rashin imanin ka daka ji sa kasan cewa abin a tausaya wa ce a lokacin, domin cike da rauni take kukan gami shashsheka duk zaton ta mutanen Hajjaju ne suka biyo bayan ta, dan haka cikin kukan ta fara rokon su..." dan Allah kuji kaina bayin Allah, ku dubi girman Allah da manzon sa ku rabu da mu, wlh yarinyar nan marainiya ce, in kuka rabani da ita bazan taba jin dadi ba dan Allah ku bar mu muyi tafiyar mu, na muku alkawari Insha Allahu bazan sake waiwayar gidan Hajjaju ba har abada.."
Babu wanda yace mata ko _'kala_ cikin samarin nan uku illah 'daya cikin su da ya 'daga siraran 'kafafun sa ya matso gaban ta, ya tsaya a saitin kanta, tsabar tsoro Zaitun rintse idanu tayi da karfi take fadin" Dan Allah kar ku rabani da ita, dan Allah ku bar min yarinya ta, kuji tausayin mu bayin Allah..."
Dukkanin ilahirin jikin Zaitun rawa yake.
_Fiiit.._ taji an fizge mata Hijab a bazata daga kanta...wani zabura ta sake yi da niyyar yin baya take ta bude idanun ta...nan taga ashe har duk su ukun sun matso kusa da ita sun gewaye ta..." BK bayan ta goyo fa...?"
Karo na faro da 'daya daga cikin su yayi magana.
Wanda aka kira da BK 'din ne da wata kalar murya irin ta 'yan 'kwaya yace " ta kwance mana...in kuma bazata iya ba a kwance mata...".
Jin hakan yasa Zaitun tayi wani kukan kura ta zabura zata gudu ta tsakanin su, da sauri wanda ke daga bayan ta ya rike mata hannaye duk biyu wanda hakan yasa ta kasa guduwan kamar yadda tayi niyya, 'daya mai suna BK 'din ne ya sa hannu ya kwance goyon ta gaban ta, jin Mufeeda na shirin fa'di ne ya sanya ta 'dan gwada yunkurin fizgan jikin ta daga hannun mutumin amma ta kasa, zuwa lokacin kuwa tsab kukan ta ya tsaya hawayen ma tuni ta neme su ta rasa tuni zuciyar ta bushe, bata kuma sake yunkurin rokon su ba dan ta lura ba fahimtar rokon nata suke ba.
Ganin da suka yi tana musu fizge- fizge ya sa 'daya daga cikin su rike mata 'kafafu yayin da Bk da ke tsaye kanta ya sauke mata wata lafiyayyar mari, sosai marin ya shige dan har jini sai da yan 'dan fito daga hancin ta amma duk da hakan bata bar fizge- fizgen ba, so take ta gwada iya iyawar ta ko Allah ze taimake ta ta iya tseratar da su dan har yanzu a tunanin ta mutanen Hajjaju ne.
Fizgo Mufee wanda ke bayan tan yayi wanda hakan ya firgita yarinyar har yasa ta sakin kuka mai karfi a razane.
Kukan Feefy shi ya dawo wa Zaitun da nata hawayen, dagaske ta tsorata cin sun cire mata yarinyar a bayan ta, bata fatan wannan ya kasance shine karshen ganin ta da Mufeeda.
Take ya dangwarar da yarinyar gefe ya kuma sa hannu ya farke bayan rigar Zaitun 'din daga sama har 'kasa batare da yayi la'akari da Zip da rigar ke dauke da shi ba.. nan take kuwa ya raba rigar biyu wanda jin haka ne yasa Zaitun dawo da hankalin ta waje ta guda sa6anin da data raba dan kula da yadda zasu yi mata da yarinya.
Fahimtar abinda mutanen nan ke nufi ya sanya ta jin mafi girman tsoro ya shige ta, yau ka'dai taga illar kwanan titi.
Iya kokari tayi wajen ganin ta kwaci kanta amma abin ya gagara kawai sai ta saki kuka, irin kukan nan mai cin zuciya, kuka na rashin mafita, cikin ranta take rokon Allah tseratar da ita ya tseratar da su baki 'daya...
Wanda ke tsaye daga bayan tan ne ya fisgi hannayen ta baya da nufin kwantar da ita sai akayi rashin sa'a 'kafar sa ta bige Mufeeda take ta 'karawa kukan ta volume lokaci guda tamkar wanda a gutsiri wani sashe daga jikin ta, karan da ya ratsa kaf kewayan wajen baki 'daya, dai-dai tahowan wata ba'kar mota da gudu ta wuce musamman da yake babu kowa sai su kadai so babu wata mota da zatai musu shamaki da gudun da suke shararawa....har motar ta gota sai kuma ya tsaya cak....
_Salmerh_ 😘
[20/9/2022, 12:32 pm] Author...🖊️: 💕 *BINTEE*💕
*( 'Yata ce)*
*Salmerh MD*
🅿️ *...16*
_Shiiit_ ...shine abin da ya bayyana daga sautin muryar sa at same time yana me bugan sitiyarin motar da hannun sa 'daya...da alamu bai so tsayawan ba...amma kunnen sa sun jiye masa kukan yarinya 'karama.
Baya ya dawo da motar ya bu'de ya fito, sai a sannan ma yaji ashe ba yarinya kadai ke kuka ba har da wata mace sakamakon jiyo sauti bibbiyu da yayi.
Da hanzari ya nufi inda suke domin yana iya hangosu daga inda yake tsayen, dai dai lokacin ne kuma wadannan matasan suka tarwatse kowa yayi hanyar sa, bai bi ta kansu ba hankalin sa na ga mata da yarinyar da ya gani durkushe a wurin ne yake kuma jiyo kukan su, lokaci 'daya 'kwa'kwalwar sa ta basa abinda ke shirin faruwa a wurin duba ya yadda yaga duk sun hargitse riga a rabe, wanda ga dukkan alamu kiris ya rage mai afkuwa ta afku in ba dan ikon Allah da ya kawo su ba.
Baya baya ta fara ja tana me sake sakin kuka sbd a halin nan da take ciki bata iya banbance mugu da wanda yake sa6anin haka.
"....Dan Allah!... dan Allah..."
Take ta fadi batare da ta iya karasa abinda take da niyyan furtawa ba.
Ganin kamar shima tsoron sa take yasa shi daka mata tsawa" _Nutsu da Allah..._ "!
'Dif Zaitun ta shanye kukan ta tare da rintse idanu da karfin gaske.
Batare da yasan wace ba ya jefa mata tambaya yana me kokarin kare ma fuskar ta kallo"..Me kk yi waje da wannan uban daren..?"
Shiru ba amsa illa baya da ta kara saurin matsawa sakamakon tsawar da ya sake mata, gaba 'daya ta firgice.
Jin ta iso kusa da Mufee yasa tai saurin rarumo ta ta gurme ta tamkar zata maida ta cikin ta...
Ido ya tsura mata cike da mamaki wanda sai alokacin ma ya fahimci wace ita gami da tunano inda ya santa, in bai manta ba ya ga wannan fuskar tare da wannan 'yar yarinyar a mabanbantan wurare har sau biyu.
...Ido ya 'dan zaro cike da mamaki yana nuna ta yatsa"...You!..what ar u doing here?..ina zaki je da wannan lokacin?"
Zaitun dai ba fahimtar sa take ba dan har a lkcn bata dawo hayyacin ta ba, d fact that za'a raba ta da Feefy da kuma fyaden da aka so yi mata shine ka'dai ya tsaye mata.
Hijab 'din ta dake yashe gefen kafarcsa ya dauka ya jefe mata.." sa mayafin ki..".
Ya fa'da da murya mai 'dan sanyi..hakan ne ya sa ta lalu6i abinda taji ya jefa matan ta suturta jikin ta da shi, ita kanta tafi son hakan duk da yake tana cikin yanayi na rudu amma data suturta jikin nata sai ta dan ji dama..kuma har a wannan lokacin bata bude ido ba balle ta ga wanda ke mata maganar.
Fatan ta kawai shine taji yayi tafiyar sa shima batare da ya cutar da ita ko Mufeeda ba.
Muryar da take ji nayi mata maganr yai mata kama da wata murya da ta ta6a ji sai dai a a wannan halin bata da nutsuwar iya tuna inda ta san muryar bazata iya tunawa ba.