Sashe 97
Ana Dara Ga Dare Yayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Daddy ya iso muna murna da dawowan shi lafiya sai layi mukeyi muna zuwa masa sannu da zuwa yana zaune da alaman agajiye yake a lokacin yake hakan kuma yake amsa muna.
Mommy da Anty suna zaune daga gefen shi tare da yaran anty din dukkan su a cikin kulawa sai hakan ya ban mamaki.
Ban taba jin kewan namu mahaifin ba sosai sai a wanan ranan yadda naga daddy din zaune tare da iyalin shi a falon shi sai tausayin mu dana umman ya kamani lokaci guda.
Juyawa nayi zuwa part din mu na samu umma zaune tana shafa magani a kafanta dakan dan mata ciwo take tambayana ya dawo lafiya nace lafiya kalau umma na shige ta bini da kallo.
Can ta fara jin kukana sama sama har yakai ta mike ta leko kuryan dakin da nake nayi rub da ciki ina barza kuka .
A hankali umma ta tako zuwa inda nake ta kai zaune tare da tambayana tana kai hannu saman kadana tace ke lafiya kike wanan kukan ?
Ban iya magana ba naji ta kara matsowa gareni tana fadin ba zaki fada mkn meke damun ki ba ko anyi wani abune kuma na gurgiza kai.
Sai dai ba magana don yadda nake jin zuciyana tana min kuna a lokacin na rashin mahaifin mu a tare damu don ban taba sanin dadin mahaifi ba sai yanzu da nake zaune a gidan daddy din.
A wana lokacin nasan muhinmanci uba a tare da iyalin shi wanda mu muka rasa wanan gatan tun muna kanana bamu san dadin mahaifi a tare damu ba.
Mikewa naji umma tayi ta fita daga falon can sai gata dauke da goran ruwa da cup a hannun ta tana fadin ki karbi ruwa kisha komai ke damun ki Allah ya yaye maki shi kiyi bissimillah kisha ruwan ta fada tana tsiyayawa a cup din.
Dole na karba na dan kurba kadan nasha na mika mata cup din har lokacin tana tsaye a kaina ta kasheni da idanun ta alaman tambaya.
A dan maraice nace umma ba komai bane fa na koma na kwanta a yadda nake da farko din naji tace Allah ya kyauta ta fita.
Ban kara fitowa ba kuma bata kara lekoni ba sai wajajen la,asar na fito umma na zaune a falo saman kujera two setter Ammar yayi filo da cinyar umma din yana buga game.
Gaida ita nayi take fadin kin tashi ke nan ga abinci can ki dauka na bata rai tare da fadin umma banjin yunwa na kai zaune.
Naji tana fadin Fa,iza ta shigo sau biyu kina kwance har na zauna sai kuma na mike zuwa wurin faiza din in duba me take nemana dashi lokacin.
Ba kowa a falon nasu na bude dakin su na samu duk suna ciki anty Nabila zaune wurin mirrow tayi tagumi sai Fa,iza da hauwa dake saman gado fa,iza na kwance hauwa ta zauna ta mike kafa tana kadawa a cikin tunane nayi sallama na shigo ina kallon yanahin su da mamaki har lokacin.
Saida nakai zaune na dan sake kallon su kafin ince lafiya anty Nabila a cikin turancin nageria ta dan muskuta tana fadin wallahi ke dai Sahiba ba lafiya.
Mommy aka bugo waya cewa yayanta yayi hatsari dazun yana asibiti rai a hannun Allah shine kika ganmu haka.
Ikon Allah sai gashi sam banji komai ba ga hakan sai cewa danayi Allah bashi lafiya na juya inajawa kawata kafa Sahiba.
Ta dan dago kai ta kalleni kafin tace dani kin tashi ke nan sau biyu ina zuwa part din ku kina kwance nace shine umma ta fada min yanzu ai nazo.
Muryan mommy ne ta shigo duk suka mike zuwa falon wurinta nima na bisu a baya muna gaida ita da dawowa .
Ta dai amsa takai zaune zuciya ba dadi don yadda ta bar dan uwanta din a cikin wani hali mara dadi Nabila ce takai zaune kusa da uwar nasu take fadin mommy ya jikin nasa ?
Tace bari Nabila saidai ace da dama don har yanzu bai farfado ba baima san wanda yaje kansa ba har wanan lokacin.
Ikon Allah kawai wanan abin nan ne fama cikin gari daga badarawa zuwa unguwarsu ya fito gidan yaya Nuhu abin ya samesa motar tayi kaca kaca ba kyace mutum ya fita a cikin motar nan ba wallahi.
Daddy ya dawone ta dan bata rai kafin tace yadawa tare muka dawo ai shikuma wai yake fada min in barwa karima girki yau tayi.
Naga yaran sun kalleta da sauri Hauwa tace amma daddy din nan mommy me kikace masa ke tace umhumm hauwa ke nan mezan ce dashi tunda baya bukatan ni inyi.
Gaskiya gaskiya abinda daddy ke maki baida kyau mommy kullun sai aita tauye maki hakkin ki don kawai ita taji dadi tanawa mutane iskan ci a cikin gida.
Kyaleshi yana da daman fadin hakan tunda Allah yace in kayi tafiya ka dade ka dawo kana da right di kwana wurin wace kakeso a cikin iyalin ka ai.
Amma mommy wanan abin fa gaskiya yayi yawa don da ba haka daddy yake ba ai koma me tayi din kanta kanta take daukarwa alhakin haka bata sani ba .
Ni yanzu matsalan dan uwana yafi damuna don inda sabo ai yanzu na saba da wanan halin da suke min ba sabon abu bane kuma a wurina.
Sun danyi maganganu ina jin su duk da bana fahintar wani abin amma kuma ina fahintar wani inda na gane akan abinda suke magana a kai.
Na dago kai na dan kalli sama kamar mai tunane kafin ince itama din ai zasu samu matsala dashi ne ai .
Da sauri Fa,iza ta kalloni tana fadin da Anty din nace eh mana kilama a yau din nan ai na mike na shiga dakin su na dauko takardan Fa,iza saman gado na fito ina fadin zanje nayi karatu don mun fara jerabawa a lokacin.
Wait for me tace na tsaya tare muka nufi part din mu da ita muna can har dare bayan munyi sallah ta fito ta koma part din su.
Mukan muka rufe dakin mu ashe bamu dade da rufewa ba fada tsakanin Anty da daddy ya rikice akan yarta Suraiya dake makaranta zancen ya taso masu.
Har abin ya kaisu ga zage zage a tsakanin su ta fito rai bace har waje tana zage zage kowa najin ta a gidan mukan muyi barci a jikin umman mu a lokacin kamar yadda muka sabayi.
Tun safe sai ga mommy a dakin mu tashiga tana saye da hijjab din sallanta da gani daga wurin sallah take sallamta yasa umma bude kofan mu ta shigo.
Tambaya tayi ina sahiba gata nan ta koma kwanciya umma ta nuna mata ni tana fadin lafiya dai ko hjy ?
Wallahi lafiya kalau yar nan daine da abin al,ajabi jiya fa muke magana a gabanta ashe wai tace da Fa,iza itama ai ba zatayi girkin ba sai gashi kuwa sunyi fada sosai da Alh har da tonon asiri a jiya din shine Fa,iza ke fada min abinda tace din.
Umma ta nisa tana fadin ni lamarin Sahiba ya fara daure min kai sai kiga yarinya tayi magana kamar a cikin wasa sai kuma hakan ya zamo gaske ni wanan abin ya fara damuna gaskiya.
Nata baiwan ke nan ita kuma mommy ta fada tana kallona sai sukai shiru can umma take fadin ai naga kamar kece da girki din mana idan ya dawo.
Sai mommy ta nisa tana fadin hakane ni din ya kamata nayi amma jiya mun dawo daga dinan ya gyade yake fadin wai na barwa karima girki kai tsaye .
Ya jikin Alh din umma ta tambaya to da sauki yanzu na buga masu waya kafin in fito sunce har yanzu dai bai farfado ba sai dai likita yace ba komai bane wai zai farfado da yardan Allah Allah ya sauwaka umma ta fada.
Ina jin su na lafe banyi magana da kowan su ba don kada su gane idona biyu a lokacin naji umma tace kai ita kuma wanan kishiyar taki da takalan magana take wallahi.
Don me zatace itace zatayi gitki bayan tasan kece da girki kuma nifa kinga abinda ke ban tsoro da kishiyoyin zamanin nan ke nan hjy.
Kana zaune kalau da iyalin ka sai su shigo su bata zama a karshe su kuma din ba zaman zasuyi ba koda sun zauna din a cikin fita kowa na kusa dasu zai zauna.
Bari ke dai Mairo wallahi da farko Alh baya biyewa iskancin ta amma a yan shekarun nan yanzu kan ya biye mata wallahi.
Zama dai kawai nake a cikinsu ina hakkuri amma komai ban ganewa yanzu wurin Alh duk abinda nayi shi dai banyi daidai bane a wurin shi.
Kiyi hakkuri hjy duba ma ga yadda yaran nan a yanzu duk sun girma hakkuri kawai yanzu ya rage kuma ai don mazan yanzu sun fison haka suma.
Shine ai tunda dai ina zaune cikin iyalina ai ita ta rage da daukan nauyi a wuyan ta yanzu kumabarin je ina son a hada abin kari a aika masu asibiti ta fada tana mikewa tsaye.
Na dade a wurin idona biyu bayan fitan mommy din daga part din ban kuma daga ba balle umma tasan idona biyu lokacin.
Mommy da Anty suna zaune daga gefen shi tare da yaran anty din dukkan su a cikin kulawa sai hakan ya ban mamaki.
Ban taba jin kewan namu mahaifin ba sosai sai a wanan ranan yadda naga daddy din zaune tare da iyalin shi a falon shi sai tausayin mu dana umman ya kamani lokaci guda.
Juyawa nayi zuwa part din mu na samu umma zaune tana shafa magani a kafanta dakan dan mata ciwo take tambayana ya dawo lafiya nace lafiya kalau umma na shige ta bini da kallo.
Can ta fara jin kukana sama sama har yakai ta mike ta leko kuryan dakin da nake nayi rub da ciki ina barza kuka .
A hankali umma ta tako zuwa inda nake ta kai zaune tare da tambayana tana kai hannu saman kadana tace ke lafiya kike wanan kukan ?
Ban iya magana ba naji ta kara matsowa gareni tana fadin ba zaki fada mkn meke damun ki ba ko anyi wani abune kuma na gurgiza kai.
Sai dai ba magana don yadda nake jin zuciyana tana min kuna a lokacin na rashin mahaifin mu a tare damu don ban taba sanin dadin mahaifi ba sai yanzu da nake zaune a gidan daddy din.
A wana lokacin nasan muhinmanci uba a tare da iyalin shi wanda mu muka rasa wanan gatan tun muna kanana bamu san dadin mahaifi a tare damu ba.
Mikewa naji umma tayi ta fita daga falon can sai gata dauke da goran ruwa da cup a hannun ta tana fadin ki karbi ruwa kisha komai ke damun ki Allah ya yaye maki shi kiyi bissimillah kisha ruwan ta fada tana tsiyayawa a cup din.
Dole na karba na dan kurba kadan nasha na mika mata cup din har lokacin tana tsaye a kaina ta kasheni da idanun ta alaman tambaya.
A dan maraice nace umma ba komai bane fa na koma na kwanta a yadda nake da farko din naji tace Allah ya kyauta ta fita.
Ban kara fitowa ba kuma bata kara lekoni ba sai wajajen la,asar na fito umma na zaune a falo saman kujera two setter Ammar yayi filo da cinyar umma din yana buga game.
Gaida ita nayi take fadin kin tashi ke nan ga abinci can ki dauka na bata rai tare da fadin umma banjin yunwa na kai zaune.
Naji tana fadin Fa,iza ta shigo sau biyu kina kwance har na zauna sai kuma na mike zuwa wurin faiza din in duba me take nemana dashi lokacin.
Ba kowa a falon nasu na bude dakin su na samu duk suna ciki anty Nabila zaune wurin mirrow tayi tagumi sai Fa,iza da hauwa dake saman gado fa,iza na kwance hauwa ta zauna ta mike kafa tana kadawa a cikin tunane nayi sallama na shigo ina kallon yanahin su da mamaki har lokacin.
Saida nakai zaune na dan sake kallon su kafin ince lafiya anty Nabila a cikin turancin nageria ta dan muskuta tana fadin wallahi ke dai Sahiba ba lafiya.
Mommy aka bugo waya cewa yayanta yayi hatsari dazun yana asibiti rai a hannun Allah shine kika ganmu haka.
Ikon Allah sai gashi sam banji komai ba ga hakan sai cewa danayi Allah bashi lafiya na juya inajawa kawata kafa Sahiba.
Ta dan dago kai ta kalleni kafin tace dani kin tashi ke nan sau biyu ina zuwa part din ku kina kwance nace shine umma ta fada min yanzu ai nazo.
Muryan mommy ne ta shigo duk suka mike zuwa falon wurinta nima na bisu a baya muna gaida ita da dawowa .
Ta dai amsa takai zaune zuciya ba dadi don yadda ta bar dan uwanta din a cikin wani hali mara dadi Nabila ce takai zaune kusa da uwar nasu take fadin mommy ya jikin nasa ?
Tace bari Nabila saidai ace da dama don har yanzu bai farfado ba baima san wanda yaje kansa ba har wanan lokacin.
Ikon Allah kawai wanan abin nan ne fama cikin gari daga badarawa zuwa unguwarsu ya fito gidan yaya Nuhu abin ya samesa motar tayi kaca kaca ba kyace mutum ya fita a cikin motar nan ba wallahi.
Daddy ya dawone ta dan bata rai kafin tace yadawa tare muka dawo ai shikuma wai yake fada min in barwa karima girki yau tayi.
Naga yaran sun kalleta da sauri Hauwa tace amma daddy din nan mommy me kikace masa ke tace umhumm hauwa ke nan mezan ce dashi tunda baya bukatan ni inyi.
Gaskiya gaskiya abinda daddy ke maki baida kyau mommy kullun sai aita tauye maki hakkin ki don kawai ita taji dadi tanawa mutane iskan ci a cikin gida.
Kyaleshi yana da daman fadin hakan tunda Allah yace in kayi tafiya ka dade ka dawo kana da right di kwana wurin wace kakeso a cikin iyalin ka ai.
Amma mommy wanan abin fa gaskiya yayi yawa don da ba haka daddy yake ba ai koma me tayi din kanta kanta take daukarwa alhakin haka bata sani ba .
Ni yanzu matsalan dan uwana yafi damuna don inda sabo ai yanzu na saba da wanan halin da suke min ba sabon abu bane kuma a wurina.
Sun danyi maganganu ina jin su duk da bana fahintar wani abin amma kuma ina fahintar wani inda na gane akan abinda suke magana a kai.
Na dago kai na dan kalli sama kamar mai tunane kafin ince itama din ai zasu samu matsala dashi ne ai .
Da sauri Fa,iza ta kalloni tana fadin da Anty din nace eh mana kilama a yau din nan ai na mike na shiga dakin su na dauko takardan Fa,iza saman gado na fito ina fadin zanje nayi karatu don mun fara jerabawa a lokacin.
Wait for me tace na tsaya tare muka nufi part din mu da ita muna can har dare bayan munyi sallah ta fito ta koma part din su.
Mukan muka rufe dakin mu ashe bamu dade da rufewa ba fada tsakanin Anty da daddy ya rikice akan yarta Suraiya dake makaranta zancen ya taso masu.
Har abin ya kaisu ga zage zage a tsakanin su ta fito rai bace har waje tana zage zage kowa najin ta a gidan mukan muyi barci a jikin umman mu a lokacin kamar yadda muka sabayi.
Tun safe sai ga mommy a dakin mu tashiga tana saye da hijjab din sallanta da gani daga wurin sallah take sallamta yasa umma bude kofan mu ta shigo.
Tambaya tayi ina sahiba gata nan ta koma kwanciya umma ta nuna mata ni tana fadin lafiya dai ko hjy ?
Wallahi lafiya kalau yar nan daine da abin al,ajabi jiya fa muke magana a gabanta ashe wai tace da Fa,iza itama ai ba zatayi girkin ba sai gashi kuwa sunyi fada sosai da Alh har da tonon asiri a jiya din shine Fa,iza ke fada min abinda tace din.
Umma ta nisa tana fadin ni lamarin Sahiba ya fara daure min kai sai kiga yarinya tayi magana kamar a cikin wasa sai kuma hakan ya zamo gaske ni wanan abin ya fara damuna gaskiya.
Nata baiwan ke nan ita kuma mommy ta fada tana kallona sai sukai shiru can umma take fadin ai naga kamar kece da girki din mana idan ya dawo.
Sai mommy ta nisa tana fadin hakane ni din ya kamata nayi amma jiya mun dawo daga dinan ya gyade yake fadin wai na barwa karima girki kai tsaye .
Ya jikin Alh din umma ta tambaya to da sauki yanzu na buga masu waya kafin in fito sunce har yanzu dai bai farfado ba sai dai likita yace ba komai bane wai zai farfado da yardan Allah Allah ya sauwaka umma ta fada.
Ina jin su na lafe banyi magana da kowan su ba don kada su gane idona biyu a lokacin naji umma tace kai ita kuma wanan kishiyar taki da takalan magana take wallahi.
Don me zatace itace zatayi gitki bayan tasan kece da girki kuma nifa kinga abinda ke ban tsoro da kishiyoyin zamanin nan ke nan hjy.
Kana zaune kalau da iyalin ka sai su shigo su bata zama a karshe su kuma din ba zaman zasuyi ba koda sun zauna din a cikin fita kowa na kusa dasu zai zauna.
Bari ke dai Mairo wallahi da farko Alh baya biyewa iskancin ta amma a yan shekarun nan yanzu kan ya biye mata wallahi.
Zama dai kawai nake a cikinsu ina hakkuri amma komai ban ganewa yanzu wurin Alh duk abinda nayi shi dai banyi daidai bane a wurin shi.
Kiyi hakkuri hjy duba ma ga yadda yaran nan a yanzu duk sun girma hakkuri kawai yanzu ya rage kuma ai don mazan yanzu sun fison haka suma.
Shine ai tunda dai ina zaune cikin iyalina ai ita ta rage da daukan nauyi a wuyan ta yanzu kumabarin je ina son a hada abin kari a aika masu asibiti ta fada tana mikewa tsaye.
Na dade a wurin idona biyu bayan fitan mommy din daga part din ban kuma daga ba balle umma tasan idona biyu lokacin.