Sashe 18
Ana Dara Ga Dare Yayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read
Tunda suka fito sallah asuba hankalin ta ya dauku ga wata macen bahausa da ta gani a dayan dakin dake kusa dasu tana jinyar dan ta.
Sai kuma yanzu da suka sake haduwa da matar a bakin famfo zata dauraye cups da plate da sukai amfani dashi wanda itama shi din tazo yi a wurin.
Yanayin shigar matar ne ya kara daukan hankalinta zani da rigane na atamfa a jikinta sai gyalen da keda ruwa da shigen kayanta data yafa ya rufe mata jiki sai shigan yaiwa Sahiba kyau ainun har ya dauke mata hankali.
Ga kunshin a hannayen ta gwanin ban sha,awa zanen sun fito shar dasu a hannayen ta ga zobbuna dasa a yatsunta hudu a hannun da bangus sai walkiya takeyi shar da ita.
Tana tsaye a gefen su tana kallon rigiman da akeyi a cikin yarbanci wanda bakin sahibace ke tashi tana fada da wace ta fara zagin ta a wurin.
Dan dagowa tayi don ta gyara gaban rigan ta daya dan fado bata son aga tsiraicin ta yasa take ta faman gyaran don rigan Okirki dake jikin tana suka hada ido da wanan matar dake tsaye tun dazun a wurin.
Har ta mayar da kai ta duka sai kuma taga rashin dacewan hakan don ko banza matar yanayin ta ya nuna ita din musulmace kuma bahaushiya.
Gashi har lokacin matar bata motsa ba ga wasu tafe bayan su wanda tasan matar zata dade a wurin nan ke nan don ba mutunci kega mutanen nan ba sai ka nuna masu kaima ka iya zaku zauna daidai.
Roban ta ta tara kafin ta juya zuwa wurin matar ba tare datayi magana da ita ba ta karbi kayan dake hannun ta tun dazun ta juya.
Yanzu kan da aka juya harshe hjy halima taji me suke fada don taji suna fadin Ajayi so na house girl de do dis for us since.
Sai Sahiban data kwarai da zama a cikin su tace eh even house girl na human ben if i no sebe do am , i no go do ta fada ta duka tana zubawa kayan morning fresh din wanke wanken data gani a cikin kayan ta fara wankewa a hankali.
Har ta gama hjy Halima na kallon yadda ta wanke su tsab ta nufo ta dasu ta mika mata bata tsaya jin komai ba ta juya ta dauki kayan ta data riga ta wanke su ko.
Don dokar asibitin ne haka kada a wanke masu komai a ciki akwai famfo a waje idan bukatan hakan ya tasowa mutum a lokacin zama asibitin.
Hanyan daki daya suka nufa tare sai lokacin hjy ta samu bakin yiwa yarinyar da tunanen ta ya addabi zuciyar ta tana fadi a cikin zuciyan ta.
Ga yarinya har yarinya da zubin irin na musulunci amma kuma da gani ba musulma bace ga kyau ga wanan yar kamar ita ta halici kanta sai dai doti ya hana komai ya fito fili.
Sai gashi sun hada hanya da ita zuwa ciki tace da sahiban thank you very much for what you did for me.
Dont mind tace tana tafiya sai dan kayan matar ya tashi barewa tace subbahanallahi ina can ina mamaki har zan fadi.
Jin hakan yasa Sahiban dan tsayawa a cikin mamaki tana fadin hjy dama kema hausace a cikin hausan da baka saba yi kullun ba dole harshe ya juya saboda rashin sabo dayi din.
Au shike nan ashe kina jin hausa ta fada cikin mamaki tana kallon yarinyar dan murmushi sahiba tayi tana fadin me na hausa sai dai ba sosai ba irin naku amma ina ji deye deye.
Ke kice kina jin hausa kawai wallahi ni na zata kema irin suce ai danaji kun juya harshe a cikin su kunayi.
Ta sake danyin murmushi da har kumatun ta suka lutsa lokaci guda yan hakoranta masu kyau da basu samun gyaran daya kamata suka dan baiyana a lokacin.
Kuna jinyan wanine kuma a nan ta tambayi sahiban tace eh kanina ne baida lafiya shine muka kawoshi tare da umman mu tana ciki.
Allah sarki nima kinga danane baida lafiya shine muke nan ta fada a daidai lokacin da suka shiga ta cikin dan dogon dakin dake dauke da dakunan kwana na majinyata.
Daki dayane a tsakanin su dana su sahiban don haka sukai sallama kowa ya shiga dakin sa da yake.
Umma na samu zaune bakin gado tana magana da Amar daya farka ina shigowa yaron ya bini da idanu na aje kayan ina fadin .
Amar ka falka ya jikin naka na nufo wurin gadon ina dan duba jikin yaron muryan ummane naji tana fadin anya sahiba abinda mutumin nan ke muna baiyi yawa ba kuwa.
Da sauri na kallo umma ina fadin umma anyi wani abune kuma yanzu da hannu ta nuna min baske din abincin dake gefen mu aje.
Na juya da mamaki ina kallon wurin naji taci gaba da fadin yanzu likita ya fita dakin nan shi da nurse wai zasu dubani yadda ya dace an biya suyi min haka din.
An biya umma na fada a cikin mamaki kafin in dora da fadin towa ya biya din bai fada maki wanda ya biya din ba umma ?
Kai ta fara girgizawa kafin tace nima nayi wanan tambayan ai yace ai tare ya ganmu da maishi wanda ya kawo mune ya biya kudin.
Umma karde zancen ki ya zama gaskiya akwai abinda yake son yi damu yake muna hakan don ni nafi tsoron sherin ojuju da komai a lokacin.
Tace ban tsamanin hakan don likitan ya fada min wai yace mu din ai yan uwan shi ne musulmai .
To kinga kenan shi musulmi ne koda yake musuluncin mutanen kasan nan baikai ciki ba ai koma meye Allah ba zai bashi ikon da zai cutar damu ba insha Allah.
Dauki abincin kici kada haka ya zama barnan dukiya don mu da zuciya daya muka dauki ko waye a yanzu.
Na nufi wurin abincin na fara budewa egede kwamo da dan kalin turawa sai kwai soyayye sune cike a cikin takewa din sai abin sha kuma a cikin kwalayen su.
Har na mika hannu zan dauka mukaji sallaman wanan matar bahausan a kofan dakin mu tana fadin nace bari nazo na duba yaron nan a cikin hausa.
Mikewa nayi ina wasan baki kamar naga ta gida a lokacin sallamanta umma ta karba suka fara gaisawa tana tambayan jikin Amar umma tace da sauki.
Take fadi kamar yadda ta fada min da farko dantane baida lafiya suke jiyan shi a nan itama don yau kwanasu biyu kenan cikin asibitin .
Umma tai mata ya maijikin ta amsa da sauki saidai yanayi na skilar sai a hankali don lafiya muka haifishi sai daga baya da yaki lafiya muka gane laluran dake damun shi.
Oh subbanallah ubangiji Allah ya yaye masa ya bashi lafiya idan da rabo wata rana sai ya mike kamar bashi ba.
Tace to Allah yasa umma tana kallona a fakaice don tana mamakin ko wacece don matar ta cika mata ido sosai da gani dai ita din watace ko matar wani.
Kamar ta gane mai umma din ke kiystawa a zuciyar ta tace yar nan taki tana da mutunci sosai wallahi ta sanadin kirkin ta na gane kudin hausawa ne yan uwan mu ai.
Nan taba umma labarin dan haduwan mu ina jin lokacin da umma ke ajiyan zuciya da jin hakan barin kawo maku abincin yanzu aka shigo muna dashi yayi muna yawa.
Ai da ki barshi don ga wani nan wani bawan Allah da yake taimakon mu shine ma ya kawo mu asibitin nan yake daukan dawainiyar mu da komai namu a yanzu.
Allah sarki dama haka duniya ya gada duk inda kake baka rasa na Allah ai nima ba gashi mutumiyar ta hadamu a yanzu ba umma tayi murmushi.
Tace bari a kawo ko kadan ne kila shi mara lafiyan zai danci don abincin marasa lafiyane ga baki daya don mahaifiyar maigidana ne a tare damu itama dai sai a hankali.
Kin san halin tsofin nan da jiki taki ta zauna gida saboda shakuwan da sukayi da dan nawa sosai
Fita tayi tana dan dariya bayan ta fadi hakan na dukar da kaina kasa muryan umma naji tana fadin .
Sahiba idan banyi hankali ba zaki dauko min magana a garin nan muna zaune cikin rufin asirin Allah.
Umma taimakon ta nayi kawai don naga bata iyawa shine na taimaketa na fada a sanyaye kaina a duke.
Taimako ke kadaine kika san hanyar taimako nace umma hausace fa ita din shine yasa na taimaketa.
An fada maki duka hausawa ne yan uwan juna sahiba wani bai san garin wani ba wani bai taba jin yaren wani ba ko a cikin hausan.
Ba zan kara ba umma na fada zaki kara don taimako a jininki yake sahiba ba zaki san lokacin da kikai hakan ba.
Kawai abin da nake so dake shine ki san wa yanda a yanzu kike dauko muna kiyi hankali dasu sahiba ki kula da kanki da mutuncin ki a duk inda kika samu kanki.
Nagode umma na fada sai ga nurse ta shigo dakin da file din umma tace ta taso su tafi da ita likita zai fara ranan.
Umma ta dan kalkeni tana fadin ki kula ki zauna min dashi kada ki yarda kije ko ina sai na dawo don nasan halin ki da rigiman tsiya ki fita azo a sace min yarona.
Na dago da sauri na kalleta kafin in mayar da kaina kasa suka fita umma na fita saiga matar hausa din nan ta shigo da katon kulan abinci da plate na tashi da sauri na karbe ta.
Ina maman taki ta tafi tambayeni ni nace ta tafi ganin likita au itama ba lafiyane ko kan matsalan dan uwan kine ?
Itace ba lafiyan za a dubata na fada na koma na zauna ta dan kali Amar tana fadin zakaci abinci ko ya kura mata ido saida nayi mai yarbanci ya dan kada kai kadan alaman eh.
Hakan yasa ta kalleni tana fadin ki zuba mai kadan ya danci na mike don bin umurnin ta ina bude warmer din wani irin kamshi ya bugine dafa dukan anta ne don shi yafi yawa a cikin abincin sosai.
Na dan debo na kawowa yaron a irin hikimar su na uwaye ta bashi yana karba a hankali har yaci sosai.
Ta dan jima a wurin mu zaune tare damu tace sunyi barci kada ta tashe su ni kuma ban yarda na gusa a dakin mu ba don tsoron da umma ta bani da zata fita.
Na kasa na tsare tare da zubawa wanan hjy idon da zaman datayi a dakin mu din kafin inji ta jefo min tambayan dayasa na dago da sauri.
Cewa tayi dani meye sunan ki ne yata na dago ina fasin Sahiba ta kara maimaita sunan Sahiba kafin tace ok.
Ku mutanen wani garine wai don yanzu hausan ku ya juye ya hade da harshen kasan nan kamar ku din ba hausawa bane don kun saje dasu tsab a yanzu.
Sai dai kamanin ki dake nuna zubin fulani ko shine kawai za a yarda ku din hausawane da kuma mahaifiyar ku da nagani a yanzu ya kara yardan min da hakan.
Kin san su fulani zubin su na daban ne tundai fulanin shiyan sokoto adamawa da da bauchi ta kalleni.
Wallahi mama ban san mu ko daga ina muke ba umma dai tace a arewa muke mukazo nan tun ina karama kafin a haifi amar.
Cikin mamaki tace kina nufin mamanku bata fada maki daga inda kuke ba har wanan lokacin da kika fara girma ?
Kai na gyada a cikin dan damuwa nace ba a fada muna ba kuma ina son in sani amma umma tace sanin baida amfani a wurin mu a yanzu.
Don me zata fada maku haka idan ma wani abune ya faru a can ta bargida ta dawo nan ya kamata ace ta fada maku.
Sai kuma yanzu da suka sake haduwa da matar a bakin famfo zata dauraye cups da plate da sukai amfani dashi wanda itama shi din tazo yi a wurin.
Yanayin shigar matar ne ya kara daukan hankalinta zani da rigane na atamfa a jikinta sai gyalen da keda ruwa da shigen kayanta data yafa ya rufe mata jiki sai shigan yaiwa Sahiba kyau ainun har ya dauke mata hankali.
Ga kunshin a hannayen ta gwanin ban sha,awa zanen sun fito shar dasu a hannayen ta ga zobbuna dasa a yatsunta hudu a hannun da bangus sai walkiya takeyi shar da ita.
Tana tsaye a gefen su tana kallon rigiman da akeyi a cikin yarbanci wanda bakin sahibace ke tashi tana fada da wace ta fara zagin ta a wurin.
Dan dagowa tayi don ta gyara gaban rigan ta daya dan fado bata son aga tsiraicin ta yasa take ta faman gyaran don rigan Okirki dake jikin tana suka hada ido da wanan matar dake tsaye tun dazun a wurin.
Har ta mayar da kai ta duka sai kuma taga rashin dacewan hakan don ko banza matar yanayin ta ya nuna ita din musulmace kuma bahaushiya.
Gashi har lokacin matar bata motsa ba ga wasu tafe bayan su wanda tasan matar zata dade a wurin nan ke nan don ba mutunci kega mutanen nan ba sai ka nuna masu kaima ka iya zaku zauna daidai.
Roban ta ta tara kafin ta juya zuwa wurin matar ba tare datayi magana da ita ba ta karbi kayan dake hannun ta tun dazun ta juya.
Yanzu kan da aka juya harshe hjy halima taji me suke fada don taji suna fadin Ajayi so na house girl de do dis for us since.
Sai Sahiban data kwarai da zama a cikin su tace eh even house girl na human ben if i no sebe do am , i no go do ta fada ta duka tana zubawa kayan morning fresh din wanke wanken data gani a cikin kayan ta fara wankewa a hankali.
Har ta gama hjy Halima na kallon yadda ta wanke su tsab ta nufo ta dasu ta mika mata bata tsaya jin komai ba ta juya ta dauki kayan ta data riga ta wanke su ko.
Don dokar asibitin ne haka kada a wanke masu komai a ciki akwai famfo a waje idan bukatan hakan ya tasowa mutum a lokacin zama asibitin.
Hanyan daki daya suka nufa tare sai lokacin hjy ta samu bakin yiwa yarinyar da tunanen ta ya addabi zuciyar ta tana fadi a cikin zuciyan ta.
Ga yarinya har yarinya da zubin irin na musulunci amma kuma da gani ba musulma bace ga kyau ga wanan yar kamar ita ta halici kanta sai dai doti ya hana komai ya fito fili.
Sai gashi sun hada hanya da ita zuwa ciki tace da sahiban thank you very much for what you did for me.
Dont mind tace tana tafiya sai dan kayan matar ya tashi barewa tace subbahanallahi ina can ina mamaki har zan fadi.
Jin hakan yasa Sahiban dan tsayawa a cikin mamaki tana fadin hjy dama kema hausace a cikin hausan da baka saba yi kullun ba dole harshe ya juya saboda rashin sabo dayi din.
Au shike nan ashe kina jin hausa ta fada cikin mamaki tana kallon yarinyar dan murmushi sahiba tayi tana fadin me na hausa sai dai ba sosai ba irin naku amma ina ji deye deye.
Ke kice kina jin hausa kawai wallahi ni na zata kema irin suce ai danaji kun juya harshe a cikin su kunayi.
Ta sake danyin murmushi da har kumatun ta suka lutsa lokaci guda yan hakoranta masu kyau da basu samun gyaran daya kamata suka dan baiyana a lokacin.
Kuna jinyan wanine kuma a nan ta tambayi sahiban tace eh kanina ne baida lafiya shine muka kawoshi tare da umman mu tana ciki.
Allah sarki nima kinga danane baida lafiya shine muke nan ta fada a daidai lokacin da suka shiga ta cikin dan dogon dakin dake dauke da dakunan kwana na majinyata.
Daki dayane a tsakanin su dana su sahiban don haka sukai sallama kowa ya shiga dakin sa da yake.
Umma na samu zaune bakin gado tana magana da Amar daya farka ina shigowa yaron ya bini da idanu na aje kayan ina fadin .
Amar ka falka ya jikin naka na nufo wurin gadon ina dan duba jikin yaron muryan ummane naji tana fadin anya sahiba abinda mutumin nan ke muna baiyi yawa ba kuwa.
Da sauri na kallo umma ina fadin umma anyi wani abune kuma yanzu da hannu ta nuna min baske din abincin dake gefen mu aje.
Na juya da mamaki ina kallon wurin naji taci gaba da fadin yanzu likita ya fita dakin nan shi da nurse wai zasu dubani yadda ya dace an biya suyi min haka din.
An biya umma na fada a cikin mamaki kafin in dora da fadin towa ya biya din bai fada maki wanda ya biya din ba umma ?
Kai ta fara girgizawa kafin tace nima nayi wanan tambayan ai yace ai tare ya ganmu da maishi wanda ya kawo mune ya biya kudin.
Umma karde zancen ki ya zama gaskiya akwai abinda yake son yi damu yake muna hakan don ni nafi tsoron sherin ojuju da komai a lokacin.
Tace ban tsamanin hakan don likitan ya fada min wai yace mu din ai yan uwan shi ne musulmai .
To kinga kenan shi musulmi ne koda yake musuluncin mutanen kasan nan baikai ciki ba ai koma meye Allah ba zai bashi ikon da zai cutar damu ba insha Allah.
Dauki abincin kici kada haka ya zama barnan dukiya don mu da zuciya daya muka dauki ko waye a yanzu.
Na nufi wurin abincin na fara budewa egede kwamo da dan kalin turawa sai kwai soyayye sune cike a cikin takewa din sai abin sha kuma a cikin kwalayen su.
Har na mika hannu zan dauka mukaji sallaman wanan matar bahausan a kofan dakin mu tana fadin nace bari nazo na duba yaron nan a cikin hausa.
Mikewa nayi ina wasan baki kamar naga ta gida a lokacin sallamanta umma ta karba suka fara gaisawa tana tambayan jikin Amar umma tace da sauki.
Take fadi kamar yadda ta fada min da farko dantane baida lafiya suke jiyan shi a nan itama don yau kwanasu biyu kenan cikin asibitin .
Umma tai mata ya maijikin ta amsa da sauki saidai yanayi na skilar sai a hankali don lafiya muka haifishi sai daga baya da yaki lafiya muka gane laluran dake damun shi.
Oh subbanallah ubangiji Allah ya yaye masa ya bashi lafiya idan da rabo wata rana sai ya mike kamar bashi ba.
Tace to Allah yasa umma tana kallona a fakaice don tana mamakin ko wacece don matar ta cika mata ido sosai da gani dai ita din watace ko matar wani.
Kamar ta gane mai umma din ke kiystawa a zuciyar ta tace yar nan taki tana da mutunci sosai wallahi ta sanadin kirkin ta na gane kudin hausawa ne yan uwan mu ai.
Nan taba umma labarin dan haduwan mu ina jin lokacin da umma ke ajiyan zuciya da jin hakan barin kawo maku abincin yanzu aka shigo muna dashi yayi muna yawa.
Ai da ki barshi don ga wani nan wani bawan Allah da yake taimakon mu shine ma ya kawo mu asibitin nan yake daukan dawainiyar mu da komai namu a yanzu.
Allah sarki dama haka duniya ya gada duk inda kake baka rasa na Allah ai nima ba gashi mutumiyar ta hadamu a yanzu ba umma tayi murmushi.
Tace bari a kawo ko kadan ne kila shi mara lafiyan zai danci don abincin marasa lafiyane ga baki daya don mahaifiyar maigidana ne a tare damu itama dai sai a hankali.
Kin san halin tsofin nan da jiki taki ta zauna gida saboda shakuwan da sukayi da dan nawa sosai
Fita tayi tana dan dariya bayan ta fadi hakan na dukar da kaina kasa muryan umma naji tana fadin .
Sahiba idan banyi hankali ba zaki dauko min magana a garin nan muna zaune cikin rufin asirin Allah.
Umma taimakon ta nayi kawai don naga bata iyawa shine na taimaketa na fada a sanyaye kaina a duke.
Taimako ke kadaine kika san hanyar taimako nace umma hausace fa ita din shine yasa na taimaketa.
An fada maki duka hausawa ne yan uwan juna sahiba wani bai san garin wani ba wani bai taba jin yaren wani ba ko a cikin hausan.
Ba zan kara ba umma na fada zaki kara don taimako a jininki yake sahiba ba zaki san lokacin da kikai hakan ba.
Kawai abin da nake so dake shine ki san wa yanda a yanzu kike dauko muna kiyi hankali dasu sahiba ki kula da kanki da mutuncin ki a duk inda kika samu kanki.
Nagode umma na fada sai ga nurse ta shigo dakin da file din umma tace ta taso su tafi da ita likita zai fara ranan.
Umma ta dan kalkeni tana fadin ki kula ki zauna min dashi kada ki yarda kije ko ina sai na dawo don nasan halin ki da rigiman tsiya ki fita azo a sace min yarona.
Na dago da sauri na kalleta kafin in mayar da kaina kasa suka fita umma na fita saiga matar hausa din nan ta shigo da katon kulan abinci da plate na tashi da sauri na karbe ta.
Ina maman taki ta tafi tambayeni ni nace ta tafi ganin likita au itama ba lafiyane ko kan matsalan dan uwan kine ?
Itace ba lafiyan za a dubata na fada na koma na zauna ta dan kali Amar tana fadin zakaci abinci ko ya kura mata ido saida nayi mai yarbanci ya dan kada kai kadan alaman eh.
Hakan yasa ta kalleni tana fadin ki zuba mai kadan ya danci na mike don bin umurnin ta ina bude warmer din wani irin kamshi ya bugine dafa dukan anta ne don shi yafi yawa a cikin abincin sosai.
Na dan debo na kawowa yaron a irin hikimar su na uwaye ta bashi yana karba a hankali har yaci sosai.
Ta dan jima a wurin mu zaune tare damu tace sunyi barci kada ta tashe su ni kuma ban yarda na gusa a dakin mu ba don tsoron da umma ta bani da zata fita.
Na kasa na tsare tare da zubawa wanan hjy idon da zaman datayi a dakin mu din kafin inji ta jefo min tambayan dayasa na dago da sauri.
Cewa tayi dani meye sunan ki ne yata na dago ina fasin Sahiba ta kara maimaita sunan Sahiba kafin tace ok.
Ku mutanen wani garine wai don yanzu hausan ku ya juye ya hade da harshen kasan nan kamar ku din ba hausawa bane don kun saje dasu tsab a yanzu.
Sai dai kamanin ki dake nuna zubin fulani ko shine kawai za a yarda ku din hausawane da kuma mahaifiyar ku da nagani a yanzu ya kara yardan min da hakan.
Kin san su fulani zubin su na daban ne tundai fulanin shiyan sokoto adamawa da da bauchi ta kalleni.
Wallahi mama ban san mu ko daga ina muke ba umma dai tace a arewa muke mukazo nan tun ina karama kafin a haifi amar.
Cikin mamaki tace kina nufin mamanku bata fada maki daga inda kuke ba har wanan lokacin da kika fara girma ?
Kai na gyada a cikin dan damuwa nace ba a fada muna ba kuma ina son in sani amma umma tace sanin baida amfani a wurin mu a yanzu.
Don me zata fada maku haka idan ma wani abune ya faru a can ta bargida ta dawo nan ya kamata ace ta fada maku.