← Book details Ana Dara Ga Dare Yayi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 275 OF 337

Sashe 275

Ana Dara Ga Dare Yayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kai ya fara dan juyawa yana fadin unbelieveble da ace a bakin wani naji wanan zancen da zance karyane don ita Alaja tafi kowa sanin muhinmancin zaman danta dake a yanzu. Wanda ke kanki baki san suna amfana haka dake ba dan karacin shekarun dakeki don mutanen mu suna karin magana da suke fadin sai arziki ya hadu akanci gaba irin amfanin da danta ke samu a yanzu tasan bai taba samun irin sa ba ai. Idan ban bar mata danta ba duk abinda ta fada min nan gaba kuma fa duk dashi nasan yana kyautata min sosai fiye da tsamani ma. Gaskiyane ya fada a sanyayye kukan umma da mukaji shine ya sakatar damu daga maganan da mukeyi muka juyo hankalin mu tashe . Ta daga hannayenta biyu sama a lokacin tana fadin oho Allah mun tuba ka yafe muna laifin da mukai maka bada sanin mu ba ya Allah. Sahiba idan kika bar aikin nan yanzu ina kuma zamu dafa muna cikin rufin asiri da aikin nan naki wanan matar kuma yanzu ta kawo muna matsala. Duk a vikin harshen yarbanci umma ke wanan maganan duk da naji wani iri har kasan zuciyana fiye da yadda ma nakeji da farko. Amma haka na daure ina bawa umma hakkuri tare da irin abinda na hango zama a karkashin oga Sha,aban zai iya jawo min nan gaba don nasan halin su na yarbawa da rashin yarda da Allah. Shima Abdul din dukda baiso hakan dana yanke ba da farko a karshe dana nuna mashi matsalan da hakan zai iya jawo min sai ya yarda da zancena din . Yayi min adduan Allah ya kawo min wani mafita a cikin gagawa shima yanzu zai taimaka min da addua da kuma neman min inda zan dan laba in samu aiki tunda zaman gidan haka baiyi ga mutum. Haka kawai na shirya washe gari nacewa umma zan tafi unguwa sai bayan fitana ne ashe na manta da wayana gida lokacin na jona a caji. Unguwar su Asabe na tafi semi boda duk da wurin ya dan canza a yanzu anyi gine ginen zamani da benaye sosai amma na gane gidan na Asaben. Gidan yana nan da ginan shi na tallakawa zan iyacewa tun bayan barin mu kaduna da muka dawo lagos wanan ne karo na ukku da nakawo mata ziyara. Tana waje gidin iccen dake kofan gidan nata tsufa ya kamata a yanzu gaskiya amma hakan ta shedani bayan dan tambayan da taimin na wacece ? Sahiba na bata amsa zan ci gaba da bayani tace a, a, a, sahiba dai ina maman ki ina dan uwanki nace duk suna lafiya gashi duk ta rude da murnan ganina lokacin. Na fito da dan tsaraban dana kawo mata yanzu babu kowa a gidan kamar lokacin da mukai zama gidan da yake da mutane dayawa sosai don masu zuwa cirani sunfi son irin gidajen nan da yafi saukin kudi su zauna a cikin shi. Sai mutane kalilan ne kuma yare ke zama da ita a gidab dako kamar gidan zai dinke da jama,a don haka yanzu ban san kowa ba a unguwar sabbin fuska nake gani. Saidai halin dan adam da gulma yasa suna ganina da mota haka lafiyayya sai suka fara zuwa muna gaisawa dasu itako tana fada masu ai jikantane tazo wurinta. Muka shiga gausawa dasu gaskiya a ranan nayiwa ya Abubakar addu,a yafi a kirga kafin na kawo gida yadda ya tsamomu daga wanan rayuwan kaskancin har ya nuna muna ahalin mu . Yayi muna kuma sanadin fita cikin kangin irin na rayuwan talauci da wahalan rayuwa tare da rashin galihu haka yasa na kudurta a raina insha Allahu zan zauna da Asabe ta fada min garin su itama in sadata da danginta na jini koba dadi irin namu dai ansan da tana raye a duniya ai. Saidai kuma ina dawowa gidan labarin yasha bambam da wanda na baro wurin Asabe dashi din don na dawo na samu umma a gida tana murna da farin ciki. Nima na shigo da murnana gida tun kan umma ta shigone Ammar ke ban labarin cewa ai wai wanan mutumin da akace yaron daddy mune yayi waya da umma tun dazun take jin dadi. Waya sai kuma na tuna da zancen wayana dana bari a gida yana caji lokaci guda na mike da sauri zuwa dakina wayan na dauko na samu miscall har sha na dinga dubawa daga office din mune yafi yawa sai kiran shi oga shaaban da kansa sai number wanan mutumin kuma da Amar ke fada min. Ban kira kowan su ba don a gajiye nake lokacin ga yunwa kuma dake cina duk da hakan wanka nayi don sauke gajiyan kafin na fito na nemi abinda zanci. Ummane ta shigo take fadin kin fita kin manta da waya yana ta ringing tundazun ake kiran layin saidai ba wanda ya daga saina Abdul ne Ammar ya daga yake fada mai kin fita wayan yana gida kin barshi a caji. Sanan wanan mutumin fa ya kirani yau din nan yana sheda min cewa zamu tafi umar a satin nan mai zuwa gobe zai aiko aimuna komai har ya tambayeni idan kin taba fita waje nace masa kwarai kuwa. Kinje dubai da wasu kasashe na duniya harma sai kuma tayi shiru ganin irin kallon da nake mata mai kama da tuhuma a lokacin. Itama dai shiru tayi tana kallona kafin na girgiza kai ina fadin gaskiya umma ki bar saurin yarda da mutane haka yanzu. Don yanzu duniya abin tsorone shi yana nufin zaizo muna da yaudarane ya koma muna wani cuta ko me ? Ni sam hankalina bai kwanta da wanan mutumin ba yabar abin shi ina da wanan plan din dama a shekaran nan insha Allah dake cikin makkan bana da za ayi. Makka fa kikace sahiba nace insha Allahu abinda naketa tara kudina ke nan tun wancan shekaran naso kije Allah bai nufa ba sai bana insha Allahu har an gama komai na tafiyan saura yan abubuwan da zasu kiraki nan gaba kiyi. Hannu ta daga don yanzu ta saba da dabi,an yarbawa tana godewa Allah cikin jero min albarka muna amsawa da Amin. A fannin oga shaaban kuma tsab oga jimoh ya fada mai kamar yadda na labartawa Abdul komai hankalin shi yai matukar tashi yake fada mashi yanzu basu tare da Alaja shi yana asia sai idan ya dawo zuwa wani sati zai shigo nageria din a zauna. Oga Abdul ya dawo yana fada muna abinda yace din sam banji komai ga hakan bani don har a bada na daina hurda dasu zan nuna mata tallakama mutum ne mai mutunci daya san zafin kan shi. A can kaduna kuma dai daddy ne ya kirasu uncle hamza dasu baffah Abdul da tsofin nan biyu da suka rage cikin iyayyen su yace yana da magana dasu. Bayan sun zaunane din anyi abinda ya dace a tsakani ya kora dalilin kiran su din da yayi nacewa yanzu lokaci yayi da yake son ya mayarwa magada da dukiyan su a hannun su shi dama bai rike da wani manufa ba yana gudun ne ya bada a hamdame komai mu rasa a lokacin da aka gane mun bayana ya zamanto babu komai da zamu gada. Nan yan uwa suka fara fadin albarkacin bakinsu kan abinda ya fada din baffah hamza dai yana kurum harsai da yaji anyi shiru ya dauka da gyaran murya yana fadin. Amma sai naga bai dace ace irin wanan halin da aka fito akan wanan maganan yanzu ace wai a gida za a mika masu gadon nan daga mu sai mu ba wani shedun hakan na gwaunati daya shigo cikin zancen. Shiru falon yayi na dan lokaci kafin baffah Abdullahi yace wanan kuma shawarane mai kyau hakan ka kawo muna don mu nan idan munyi shedan hakan karshe komaina iya tasowa mu jefa jan mu a cikin wani rikicin kuma. Nan suka fara fadin albarkacin bakin su daddy dai yana kurun baiyi magana ba hakama modibbo da zuwa yanzu abinduniya ya dameshi kan fahintar waye daddy din nasa a yanzu da yayi. Don ko wanan taron daya tara din saida ya kara tuntubanshi kan zancen yayi wanan kiran da yanzu suke zama a kanshi din. Muryan daddy din ne yayi gyaran murya yake fadin hamza don na fahince ka yanzu kamar baka yarda da abinda zan basu ba ko hakan bai maka ba da zanyi ? Eh to gaskiyane baffah hamza din ya fada yace kasan sha,ani na gado wuyan lamarine a cikin sa balle duba ga yadda yanzu na fahinta cewa mutanen ban sun ba duk wani abu da yanzu ake magana akanshi baya. Ma,ana kamar sun yafe zancen dukiyan dake hannun ku dama su bukatansu kawai a daina farautansu din da akeyi su fito fili kowa yasan dasu a cikin dangine. Daddy ya bude baki zaiyi magana ta hanyar kiran sunan baffah hamza din yana fadin watau hamza baka fahinta ba. No daddy maganan uncle gaskiyane fa dole sai hukuma sun sanda za ai hakan kaima kasanda hakan don haka maganan uncle ba wani abu bane ai yanzu nagani modibbo ya fada daga can inda yake zaune a takure. To shike nan tunda haka kukace sai a gaiyato wanda zaku gaiyato din shike nan ko a zauna lafiya ba wani wanda zamu gaiyato a nan baffah hamza ya fada wanan karon a tsatsaye don ya hasala zuwa lokacin. Can dai kotun da akai maku sharia dasu za a koma a zauna a tsara komai yadda sharia ta tanada final ya mike don barin wurin saboda kirkiri ya hango an shuka rashin gaskiya ga al,amarin a filin Allah lokacin. Dakata mana hamza tsohon guda ya dakatar dashi ya koma ya zauna yake fadin idan kai haka yanzu kamar ka dauko wani barakane kuma a tsakanin ku ai da dan uwanka. Kallon inda daddy din yake zaune dagashi sai babban riga babu yar ciki a cikin ta ya zauna ya mike kafafuwan shi saman kujeran. Kafin yace no ba wani barkan da zai faru a tsakanin mu aishi yasan halina niko yaushe a bayan gaskiya nake ba zan yarda na goyi bayan karya ba har abada. Da akwai inda zanje daurin aurene dama ai su sun sani yana nuna su baffah Abdullahi
Chapter 275 · 0% Book details