← Book details Ana Dara Ga Dare Yayi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 278 OF 337

Sashe 278

Ana Dara Ga Dare Yayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Na rasa me zancewa umma a lokacin don haka na zauna kawai ina sake sake a raina kafin na nisa na dago kai ina fadin wai umma kinji mutumin nan ya kara bugo min waya cewa ki tafi ai maki visa ke da ammar har ma da wasu mutum goma a bangaren mu. Don za a tafi aiwa mahaifin mu addu,ane a saudiya wai kuma tare dani zaku tafi har mahaifiyar shi da yan uwan shi za ayi wanan tafiya. Kafin in gama fadi umma takai gwiwan ta biyu a kasa tana addu,a ga Allah tare da daga hannayen ta biyy sama fuskanta yana kallon sama ga hawaye na zuba tana godiya ga ubangijin talikai taci gaba da jeru addu,a a cikin harshen yarbanci . Dole muda muke wurin muke amsawa amin amin ya Allahu har takai ga mikewa tsaye zakace ita din haihuwan kurciyan lagos ne a yadda ta juye yanzu zuwa al,adunsu . Bayan gama adduan ne nikan na tashi na shiga daga ciki falo na zauna na kunna tv saidai ba kallon nakeyi ba don tunanen daya rinjayeni a lokacin. A kan wa zamu zaba a cikin dangin mu ke nan don banga na zaba nikan a idona a iya sani na dai danayi masu a kaduna saidai idan mamaki zan basu a dauki wasu tsofi uku na nan da ba ruwan su mata yan uwan mune na sosai su din sai dai kamar ba a cikin dangi suke ba don talauci. Amma na kudurta komai ritsi dole inje da faiza da Amira ko fatima daya dai daga cikin su dolene saboda kaunan da suka nuna min a zamana dasu kaduna har yanzu kuma. Haka a bangaren maza zamu dauki baffah hamza da baffah Abdullahi Abdul makwabcin mu sai wasu biyu daga can yola yan uwan umma. Jikina na mayar bayan kujera ina sauke numfashi tare da fadin anya umma zata yarda da wanan zabin nawa kuwa ko zata sauya idan ta shigo. Matsala dayane na sani akan su faiza da Amirah amma in anyi duba da dubina sun cancanci tafiyan bayan dubana su din adduan su da alaman haske a yanzu. Idanuwana a lumshe suke umma ta shigo ta sameni hakana a zaune na mike kafafuwana idona a rufe bina tayi da kallo kafin tace dani lafiya nake kuwa ko wani abin kuma ya faru ? Ba komai na furta lokaci guda ina bude idona na sauke a kanta dakinta ta nufa ta dan dade a ciki nasan ta kewayane lokacin. Tana fitowa tun daga kofa take fadin nayi nazarin wanda ya dace ace mun tafi dasu din nace eh to ina dan dagowa tare da fuskantar ta nace . A kwai dai maza din na shiga lissafo mata su tare da dalilin sakasu din tana dan gyada min kai a hankalu alaman gamsuwa. Kafin na dawo wurin mata ina lissafo mata su din suma tare da mata bayani ko zata iya tunawa dasu tsofin dana saka din da ban tantance sunayen su ba a yanzu. Saidai kamar yadda nayi tunane haka din ne ya faru akan su Faiza din dana kawo kansu don taso ta musa din nayi mata bayanin dalilina ta gamsu aka aje maganan a haka. Bayan fitan umma zuwa shagon ta na fara neman layin ya Abubakar wanda yake jigo a garemu cikin family yanzu don in sanar dashi . Kiran ya katse bai kira ba ashe lokacin suna gun daddy ana wanan maganan da sukayi din a lokacin bayan ya fitone yaga miscall dina a lokacin ya dauka. Bayan mun gaisa nake fadin idan ba damuwa zan iya samun passport din uncle hamza dana uncle Abdullahi faiza na dai lissafo mai sunan su kaf . All dis peoples da kika lissafo min me zakiyi da passport din su haka ko zaki kaisu makka ne ya fada a cikin gatse da zolaya. Eh gaskiyane umurah dai zamu tafi tare muyiwa Abbah mu addua a can masha Allahu wai da gaake kikeyine wallahi da wasa da na fadi hakan da farko. Ashe abindana canka din gaskiyane yanzu haka muna tare dasu uncle hamza din ma zanyi magana dasu insha Allahu ba zai wuce yau din ba. Ba a kwana ba a ranan saida suka turo min passport din da duk wani abinsu nan dai na tura mai kamar yadda yace din. Haka ban garen ya Abubakar dai baiyiwa kowa bayanin komai ba akan photunan daya karba din don haka ba wanda yasan da wanan zancen . Haka kuma shima din tun rana dana tura sakon banji shi ba don bai kira ba akan yaga sakon ba sai wajajen tara na dare ya kira wayana da vedio call ina online a lokacin muna hira da Felix da yemisi da suke rokona na dawo wurin aikina na kyale Alaja bata san me takeyi ba a yanzu. Har felix din ke fada min cewa Aisha ma ta kawo mai karan zata bar Alajan ta dawo nigeria ko wani kasa. Da kyat na lalashe ta har ta bari yayanta ya dawo daga tafiyan nan da yayi kada hakan ya kara daga mai hankali don ana fama da naki case din yanzuma haka. Alaman ina ruwana na tura mashi karshe sai ga kiran wanan mutumin ya shigo min dama kuma ina mamakin rashin kiransa kada ya buda muna kasa a ido muzo muji kunya a karshe da banga kiran nasa ba na fara tunanen hakan a zuciyana saida na samu su yemisi muna hira na dan sha,afa da zancen lokavisa Na dan dade ina bin wayan da kallo tare da mamakin kirana da vedio call a wanan lokacin don me ba zaiyi kirana ba sai vedio call yana kallona. Sam babu damuwa a gareni don rigan barcin dake jikina ganin kiran zai iya katsewa a lokacin yasa mm a daga da sauri sai ga photon shi ya fito a wayan. Yana dauka yace mai tsiwa ya kika wuni ko har kin kwantane ko na kiraki duk da nasan yan mata kamar ku samari basu barin ki kwanta a wanan lokacin. Fuska na bata nake fadin sakon ya shigo dazun don su nake ganin sun dace a tafi dasu din a wanan lokacin. Dan murmushi yayi yana shafo fuskan shi alaman gajiya a tare dashi yace nagani saidai kamar har da yara a ciki kuma addua zamujeyiwa marigayi ai ? Eh shi zasuje suyi suma don suma din musulmaine adduan su kuma zaifi na wasu manya din nake gani alright as you wish. Bari na barki kici gaba da charting din ki kada saurayin ki ya tuhumi ko kin samu sabon saurayine ya zargeki. Zaki jini zuwa gobe zan turo da duk wani abinda zasuyi visa dashi inaga hakan zaifi sauki sosai har na umma din saiki turo min da account number dinki yanzun nan idan kin sauka daga hakan yace good night ya kashe wayan . Nan ya barni da guntun tunanen maganganun shi gareni kwanci nayi ban dauki hakan a komai ba na dauki hakan dai kamar yana son ne sabo ya dan shiga tsakanina dashi a yanzu. Har aka turo min da kudin da zasuje suyi visa har da dori wasu a sama kudin don nasan wanan kudin yafi karfin wanan laluran suma din na basu daidai gwagwado don ban kyataci kowa a cikin su ba lokacin. Sai lokacin labarin tafiyan ya bazu a dangi daddy kan mamakine ya kashe shi don bai san ta ina kudi ya fito muna haka da wanan alherin ba. Gashi ba lokaci don baifi kwana hudu ya rage yanzu ga tafiyan namu don haka ba lokacin wani kwana kwana ga kowa ko wani nazari don baffah Abdullahi yayi tsaye kan yaran zasu tafi tunda tare dashine. Haka suka shirya muka hadu a logos din don tacen muka tashi sai kasa mai tsarki gaba dayan mu zamu kai ziyara a ka,idance . Wanda nake tunanen wata kila iya mune tafiyan dama badashi ko wani nasa ba ko lokaci zama dasu Faiza bamu samu ba lokacin don da yamma suka iso sai batun tafiya wanan yana cikin shirin ya Abubakar ne don kada a dora muna wahala yace. Shigan safiyane ana asalatu muka sauka birnin jiddah inda baffah hamza ke jagorantan mazan a lokacin don wayewan shi a cikin mu duk da nidashi ne muna a tsaye lokacin. Har motar da zata kwashe mu zuwa masauki mu huta kafin mu wuce zuwa madina washegari kamar yadda suka tsara muna din a cewan wanda yazo daukan mu din. Ba laifi mun samu masauki mai kyau da nagarta gaskiya don munji dadi sosai a ranan don haka tun jidda mun sauke gajiyan mu a nan. Mun bar magana caaaa a kaduna don kowa da irin yadda yake fassara zancen tafiyan namu don wasu na fadin nice ai na kaisu umurah din da kaina don nayi karfi yanzu na rika sosai. Wasu kuma na fadin a, a gadon ne ai aka fara bamu muka fara banzatar da kudin dama ai kudin gado haka yake komai yawan shi a banza da wofi yake tafiya. Wasu kuma na fadin idan ba kudi yai muna yawa ba na rasa wanda zan kai umurah sai su iyan Amina da dije da inna ma,u. Inda wasu kuma suke ganin dacewan abinda nayi din don inbada su faiza da fatima babu wanda bai bukatan zuwa wannan kasan dama a cikin su basu samu mai kaisu ba idan ba uncle hamza dake da karfin zuwa ba sai idan bai so ba dai. Haka dai zancen yai ta yawo kowa na fadin albarkacin bakin shi kan tafiyan namu lokacin a gidan daddy kan basu da bakin magana yanzu don kowa dai na dauki dan dakin shi sai kaji baki ya mutu murus. Basu da abin fada sai saka albarka tundai anty amarya dake fadin kai yarinya ba abinda ya dameta ai an mata ha,inci ta saka muna da alheri yanzu don bata mace halarci ba. Washe gari kuma sakko mukayi zuwa birnin madina a can ma wanda zamu hadu dashi yazo ya taremu ya kaimu masaukin da zamu sauka. A wani katafaren hotel ne mai kyau da tsada komai na wurin sam barka sai a lokacin muka samu kwarin kiran yan gida don a gaisa dasu su faiza suka shiga photuna suna turawa
Chapter 278 · 0% Book details