Sashe 265
Ana Dara Ga Dare Yayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali na tako zuwa inda wayan ke jone a jikin chargi dana shigo na samu akwai wuta a lolacin na makala wayan a caji na shiga bandaki. Kallon layin dake kirana a lokacin nakeyi don ban san wanan layin dake shigowa dakiran a lokacin. Na dauka da sallama ina karawa a kunnuwa na a daidai lokacin da me kiran nawa yayi sallama shima a bangaren shi jin muryan na mijine yasa na kara mamakin haka ina sauraron maishi lokacin. Gaisawa mukayi da harshen turanci saidai duk da hakan ban sheda muryan maishi ba kafin maishi din yake fadin nasan baki san mai kiraki ba ko nace eh a sanyayye. Ok kina magana da mahaifin Al,mustaphane mijin gwaggom ki harira daga nan kaduna da fatan kuna lafiya. Fadin hakan da yayi yasa na kara mai wani sabon gaisuwa na mutunci da girmamawa lokacin guda don ina ganin mutuncin mutumin a idona gashi duk kotun da muke shiga tare dashi muke zuwa kotu din. Da zaran mun fito kuma zamu gaisa yayi muna bangajiya tare da bamu kwarin gwiwa akan abinda muke tunkara a gaban mu. Tambayana yayi ina umman mu da dan uwan mu nace dashi suna lafiya kalau ya furta masha Allah kafin dan shiru ya sake biyowa baya. Kafin kuma yace Sahiba dalilin da yasa na kiraki akan zancen danane mustapha dan uwan ki da fatan zaki natsu ki saurareni. Wani abu ya farune da mustaphan na tare shi da tambaya a dan razane yace no no na yana lafiya saidai ba lau ba saboda ke sahiba. Mustapha yana sonki yana kuma ra,ayin auren ki a matsayin matar shi ku zauna tare wanda idan hakan ya kasance zamu fi kowa farin ciki da hakan. Shiru nayi ina jin abinda dattijon ke fadi a lokacin wanda yazo min a bazata idan danshi yana sona shine zai fada min ba dan nasa ba ko haka su sukeyi a nasu al,adan koko son danne yasa shi ya tunkareni da zancen haka kai tsaye. Ban iyacewa komai ba sai lokacin da naji yaci gaba da fadin zamuyi maraba dake a cikin family din mu zamu rikeki tankar irin rikon da mukewa dan mu mustapha dan daya kuke dashi a garemu. No uncle ida kace kai zan yarda da hakan don zuciyat ka akan mu me kyaune da kaida danka nasani amma ita gwaggon mu akwai wani fassara da tayiwa rayuwana da take kallona dashi a idon ta. Saidai kamar yadda ka fada din ni yace a wurin ka uncle na sheda hakan a gareka gara dai in zauna a hakan a matsayin ya a wurin ka wace ko yaushe matsala ya tunkaromu zaka iya tsaya muna akanshi. Amma aure ko wani alaka irin haka ban taba jinshi a zuciyana ba face kallon dan uwa da nake masa akoda yaushe a idanuna. Shiru yayi kafin yace dani ki dai kara tunane akan maganata don yanzu haka akan wanan maganan a halin nan da ake ciki mustapha yana fuskantar barazan sonki a zuciyar shi sosai kuwa. Aiko ya daina uncle don shi din yayane kawai a gareni wani abu mai kama da so ko wani so uncle na gode amma wanan bamai yuyuwa bane ka tambayi matarka abinda suka fada ita da mommy ta gidan daddy a kaina ranan. So nagode da kulawan ka garemu da fatan wanan maganan bai bata ma rai a yanzu ba sai anjima na kashe wayana ina sauke numfashi don mamakin daya cika min zuciya a lokacin. Wayane a hannunta tanayi a lokacin da gani wayane mai muhinmaci sosai a gareta don yadda ta maida hankali tana sauraron wayan a lokacin. Har yarta babban tazo ta bugeta tana fadin maza mai aiki ta wuce dasu zuwa garden din gidan kafin ta fito yaran suna kuka haka mai aikin ta kwashesu. Amma bai taba nuna min alaman hakan ba sam saidai nasan da cewa yana yawan kulasu don kusan ma shine wanda ya dawo dasu gida suke fada ta a bangaren ta . To ki kula ki mai da hankali don abinda zuciyana ya fara zarga min ke nan a yanzu duk da yanzu din ba komai a tsakanin su. Zaune kawai take tana jin wani irin masifa yana taso mata wanda bata iyama controling din kanta a lokacin don yadda take jin kanta din. Wayan ne ya katse ba don sun gama fadan zancen da sukeyi ba lokacin hankalinta ya tashi ta mike daga zaunen da take ta fara yawo a dakin a cikin masifa. Abincin ranama gashi tana kallon an dafa irin abinda take son ci amma ya gagareta ci a lokacin sai faman kutawa da takeyi tana hadawa da tsuki. Wanan wayan na mahaifiyar ta ya tayar mata da hankali sosai a ranan duk da tasan cewa shi din mutum ne da baida ra,ayin yin mata biyu a rayuwan shi yasha fadan haka tanaji. Idan wani abu ya hadata dashi yakan ce da ace nime ra,ayin kara matane a rayuwana Nazifa da yanzu na dade dayi maki kishiya a gidan nan . Wanan kalamin yasa take masa duk wani iya shegen da takanyi wani lokaci tunda taji yana furta hakan tasan ta rufe kofa ke nan babu wata shegiyan da zata shigo mata gidan mijin ta a lokacin kuma da sunan aure. Tsuki taja a karo na barkatai a inda take din kafin ta dauki waya tana laluban layin yarta dake aure abuja kuma abokiyan shawaranta. Ta samu layin ya shiga sun gaisa suka dan taba hira akan mahaifin su inda yar nata ke fada mata cewa ke dai jiya an barmu munga su baba wallahi. Au wai dama ko ganin su ba,a barin ayi ne ta tambaya cikin mamaki sai yar nata tace wai keko kinga irin matakan da aka daukane akansu kuwa ? Kissa fa ake zargin su dasunyi tare da hamdame dukiyan mamacin mu dai kan ai su baba sun bar muna abin fade a cikin rayuwan mu. Gashi zancen ya karade ko ina don har wata yar mijina ta kirani don iskanci tana fada min wai ashe abinda ya faru da mahaifin mu ke nan ana zargin shi da kisan dan uwan shi. Inko hakane gaskiya dai munyi hasara sosai ace mahaifin mu yayi kisan dan uwan shi saboda arzikin shi, , , , Naziface ta katse ta da fadin keme kikace da ita anty tace Nazifa me zan fada kuwa tunda sun ja muna wanan bakin sunan a duniya kuma. Mu dai yar iskan yarinyar nan ita da uwarta ai sunja muna tsiya yanzu yan iskan mutane kawai da basu san mutuci ba a rayuwan su. Haba nazifa don me zaki zagesu akan gaskiyan su suke fa su don su babane basu kyauta ba kema kin sani a kaddara mu akaiwa hakan zaki iya kyalewa kiga suna cun dukiyan mahaifin ki suda iyalin su kiyi shiru alhalin kikai lokacin da zaki iya ja dasu. Kuma jiyan naji ai su baffah hamza na maganan cewa ita madam din tace zata kira a sassauta akan yadda aka dauko tsarun ai kinga kuwa intai haka ta kyauta muna gaskiya. Wai wata madam ke nan nazifa ta tambaya cikin son jin amsa tace yarinyar mana ai haka ake kiranta da madam sahiba . Wai kinsan ko akanta dama na kiraki yanzu wai ashe son baban su maryam takeyi yasa ta lake mashi haka ashe soyayya suke dashi ban sani ba ? Ke nazifa waya fada maki wanan maganan kuma yanzu ana wanan halin wake ta batun wani soayya can kuma ? Anty ke nan dama aiba mutuwan mahaifim nasu ya damesu banesu bane su zancen dukiya ya damesu a yanzu don haka a sake muna mahaifin mu suje suci dukiyan su daya dama. Idan fa gaskiya tazo ana cire son kai a cikinsane nazifa kindai san su Abba basu kyautawa zumunci ba gaskita koda ace sun jawosu ajiki kuwa suna kyautata masu ba su watsar dasu irin hakan da sukayi kai koma ace din suna a hannun su basu dai kyauta ba gaskiya sai dai kawai ayi sha,ani a yanzu kawai . Anty kardai ace kin fara yarda da lamarin wanan munafukan yar iskan yarinyar nan a yanzu har kima tausayin su nifa har yanzu ban yarda cewa su baba suka kashe masu mahaifin ba Allah ko. Amma kinsan baba zai iya aikaya fiye da hakan dai ko to don me yanzu zaki tsaya kina wani konkonto a zuciyar ki akan haka . Sun dauki lokaci duk inda ta fito sai yar nata ta hasaka mata saidai hakan baisa ta yarda da abinda yar uwar nata ke fada mata ba a lokacin. Mommy ne zaune bayan fitan yaranta daga dakin da kowa ya dawo daga aiki ya shigo mata da dan tsaraban da sukan kawo mata duba ga ranan ayi albashi yasa ko wace ta shako mata leda da abubuwan bukatansu wanda suka san zasu nema a ranan. Dama tana tunane akan hakan sai yanzu gashi yaran sun shigo mata da abin arziki irin haka wasu hawayen tausayi yazo mata lokaci guda. Ashe akwai ranan da zatazo masu irin haka duk irin dukiyan da take ganin sun tara a gaban su amma sai gashi ba aje ko ina ba har rayuwa ta fara juya masu baya haka ? Yau badon yaran sunyi tunanen irin haka ba ai da bata san yadda zasuyi a rayuwan su duk da modibbo na iya taimaka masu sosai tun ranan da mijin nasu ya tafi. Saidai duba ga yanayi da kuma yawan su ba lalai bane komai ya wadatace su a yanzu yadda suke so don dole kudin da yake bata tayi wani lalura dashi ai. Gashi kamar yadda sukayo mata sayayya haka suka dan kwatanta suka sayowa hjy karima da yaranta itama suka kai mata. A zaton mommy din hjy karima ba zata karba sai gashi sun dawo suna fada mata cewa ta karba a cikin jin dadi kuma har da godiya ga hakan da sukai mata. Da alama kuma sun bata kudi duk da basu fada mata hakan ba amma tunda suka iya aje mata kudi itama tasan zasu kwatanta hakan ga abokiyar zaman nata. Ashe ko wani mutum da Allah ya hadaka dashi yana da ranan shi a duniyan nan yau itace ta sanadin Sahiba alheri ya shigo