Sashe 80
Ana Dara Ga Dare Yayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bawai fita dasune bana so ba a, a yadda mutane ke fadan magana a kaina idan sun gamu tare tambayan farko da zasuyi a kaina shine amma dai wanan kafira ne kuka samo ko ? Idan sunce a, a zasuce tana shiga kamar kafira idan ka ganta a ina kuka samo wanan din zasu basu amsa da diyar abokon daddy mune tazo. Zakiga suna min wani irin kallo na kyama ko hattara a idanuwan su kai malam bahaushe dai akwai nuna bambamci koda kuwa sun yaba halittana sai naga wanan kallon a kwayan idon su kallon dana kasa fassara ko na meye suke min. Don ko ranan da mukaje gidan ya Abubakar na farko irin kallon banzan da matar tashi tayi min yasa naji bana son na kara zuwa gidan ga baki daya don tana fitowa fallo muna zaune na dauki wani takardan dana gani a kan table din dake tsakiyan falo ina karantawa ta fito. Suka mike suna gaida ita tana wani irin shan kamshi ban dago ba idon ta a kaina har ta kai zaune sai fa,iza ta dan dungureni na dago kai take fadin greet her now nace good morning. Bata amsa ba ta kawar da kai gefe daya tare da fadin ita wanan din wacece haka kuka samo kuma tana wani ya mutse fuska tana watsa min kallo mai kama da harara. Amsa daya ne dai shi suka bata ban kara kullata ba na mayar da kaina ga karatun da nakeyi kafin mai aikinta ta fito muna da abin sha. Na kula da yadda suke wani dari dari da ita kamar suna tsoronta dai sai wani magana take masu a cikin izza da isa da takama nuna wayewa a garesu. Ko kallon lemun banyi ba don duk inda nake a wani irin matsuwa nake da mubar gidan lokacin shiru shiru ba mai magana na dago kai ina fadin Anty Nabila may we go naw,. Tace dani not now dagawa nayi ina fadin i don tiear woo, if u no go now meet me at home na dago na fara shirin barin falon lokaci guda. Wanan kan yar iskace naji muryan ta tana fada kubar kwaso min irin yan iskan nan zuwa gida dan Allah ku barta ta tafi mana bata san hanya ba. Ban tsaya sauraren ta ba na sakai na fita sai a gida suka sameni don ko mommy bata san na dawo kai tsaye part din muna nufa. Saida suka dawo ne suke labari aka san na dawo shine mommy tazo tana maganan a part din mu wai ban kyaya ba ba gidan yayan mufa muka tafi na fito hakana. Su kuma su Fa,iza suka sakani gaba da fadin wai na taho ban tsaya na karbi turare data basu ba budan bakina nace dasu ko ta ban ma bazan karba ai don sam matar bata da maner tana kallon mutane a wullakance. Shine yau da mommy tacewa umma zamu gobe nake jin raina na baci umma ta kula da hakan yasa tace dani maza na shirya mu tafi kawai. Mun shirya tsab muka fito duk da baida nisa wai a mota zamu tafi muka shiga Nabila taja mu zuwa gidan mun samu kofan falon rufe mun dade muna nockig aka bude. Wanan yayan namune daya dauko mu ashe gidan shine wanan daga shi sai wata dogowar jallabiya mai ruwan makuba a jikin shi lokacin. Yana ganin mu ya jaye yana fadin ashema kune kuka tsaya kuna ta sallama haka ai kofan a bude yake kasa kasa Fa,iza tace min ba dole muyi sallama ba ranan da mukazo fa muka shiga kai tsaye koran mu matarshi tayi wai ba a bamu izini ba muka shiga mata gida. Baisan tare muke ba sai gani da fa,iza mun biyo bayan su mun shigo a karshe sai lokacin ya dan saki murmushi yana fadin u ? Broda na ur house be dis ? we come dat day i no see u, so that lady na ur wife be dis ? Ya danyi murmushi kawai muka karasa zuwa ciki tana zaune falon ta mike kafa saman dan table ashe duk wanan sallaman da mukeyi tana jin mu har ya fito daga daki yazo ya bude muna kofan duk tana zaune. Bayan mun kai zaune sukan a cikin dari dari suke sai da suka fara gaida ita suke fadin yaya kazo lafiya yace Alhamdullahi sai lokacin nace broda you are wellcome. Ya amsa da fadin Sahiba so now you are enjoyed d north side see how you look now sai na danyi murmushi yaci gaba da fadin ya umma da Amar suke suna lafiya ko ? Ba wani matsalan komai a yanzu ko, , , sai matar ta katse shi da fadin wai ya hakane don Allah ita kadai ka gani a wurin nan kome ? Ke ni kike dagawa harshe haka ko zaki hanani magana da itane kuma wanan fa kanwatace itama kuma yanzu kamar bakuwa take a cikin mu. Ni yarinyar batayi min bane tana wasu dabi,u na kabila ko kafirai innalillahi yace tare da fadin a cikin mamaki da Nazifa kin san wanan din ko wacece gare mu baki daya ? Da zaki danganta ta da kafira balle me yarinyar nan tayi na kafirci a yanzu ban son haka kuma kada ki kara don hakan zai iya jawo muna matsala a tsakanin mu sosai kuwa. Ba itaba duk wanda ke falon saida yayi shiru yana sauraren ta kafin ya juyo yana fadin ku tashi ku shiga ku dafa min abinci inci ya mike bai jira komai ba ya shige wani part da nake zaton nasa ne. Wani irin kallon tsana ta jefo min kafin ta mike tana fadin kada ku halaka min kaya ehhe ta shige tabi bayan shi Nabila ta bisu da kallo tana fadin Allah ya gani don mommy nazo gidan nan wallahi. Wanan yar rainin wayau din da kazo sai ta bata ma rai ta musgunawa mutum halan bamu taba ganin kaya bane da zamu bata wanan din. Ke ko ba tana takaman ba mai kudin ubanta bane kaf a dangi dole tayi muna haka mana yar rainin wayau kawai. Dole kuma suka mike zuwa yin girkin muna zaune falo da fa,iza mu muna kallon tashan da take kallo din muna kuma jiyo hayaniyansu ita dashi daga ciki. Fitowa tayi a fusace daga dakin a daidai lokacin da Fa,iza ta mike zuwa kitchen din ta duba sai ni kadai a wurin zaune na dan kame saman kujera. Tun kan ta karaso ta daka min wani irin uban tsawa tana fadin Ke tashi a nan nayi kamar banjita ba ban san me take nufi ba ta kara fadin. Stand, up f Who give you right to sit on my chairs don't ever and ever sit on this chair again look at you dity girl like , , , , Allah aka fada a bayan ta yana karasowa a cikin wani tako har ya karaso inda muke din tana tsaye ina kallon ta kafin yace lalai ashe ko hakan kuke dama ashe ba karya ake fada ba kan halin ku. Har ina kujeran yake a nan tunda ba kujeran zinare aka kawo ki dasu a gidan nan ba lalai babu dan uwana da zai kara hawa saman kujeran ki daga yau din nan . Sai dai ai zaki barsu dai su shigo gidan dan uwan su tunda gida na dan uwan su har su zauna saman kujeran dan uwam su ko ? Ya juyo ya kalli inda nake yana fadin Sahiba call your sister for me now nace yes broda na nufi hanyar da naga suna bi din sai na samesu a tsaye sunji hayaniya sun fito sun tatsaya dan nisa kadan dasu. Ina fada masu ne abinda yace ya hangoni kafin yace dasu kuzo in sauke ku gida yanzu zan dan fitane abincin fa yaya Nabila ta tambaya yace barshi kawai kuzo mu tafi. Haka kowa ya dauko gyaleshi muka bar gidan shi ya fara fitowa sai kuma ya koma ciki yana fadin yanzun za a kawo min kujeruna sai ki kwashe wanan din naki da kike hana yan uwana zama.. Tace aiga yan uwanka nan ka tambayesu idan na taba hanasu zama a kai ita wanan da kika hana a yanzu wacece tawa ki fada min ? Kaika sani don ni bansanta ba cikin dangi ta fada tana gyara zaman ta ya watsa mata wani kallon zaki gane kuren ki ya fita. Wani irin figan mota yayi don bamu bishi ba tunda munzo da mota da zamu zo gidan gaida ita ashe rabon tashin hankaline ke kiran mu. Gashi sai tambayana sukeyi a motan meya farune har hakan ya faru a tsakanin su Fa,izace tace wallahi ba abinda ya faru duk ina jinsu ta shiga daki ta samu yaya tace wai don me yake magana haka da Sahiba har yana dariya baiyi da sauran kannen shi ? Shine fa fada ya kaure sosai a tsakanin su suke wanan fitinan haka wai ko kishin sahiba takeyi ne ? Muka shiga get din gidan Aisha tace yar wahala ce kawai in bashi ba meya kawo wanan zancen haka wata sahiba kuma har zata tsaya kishi don kawai yaya yayi magana da ita yana dariya ba sabo bane a tsakanin su. Sai a lokacin Fa,iza ta tuna take fadin zancen zuwa gidan gwaggo Asiya din kuma fa ko an manta da zancen ne yanzu. Ina zamu gidan gwaggo a yau din nan wanan yar rainin hankalin ta bata zance don wani hauka nata can na daban nina rasa me yarinyar nan tayi mata. Don na fahinci sahiba idan baka taba, taba sam bata da rigima ko rawan kai ga komai saidai idan kaso raina mata wayau ne za a jiku yanzu da ita. A compound din gidan muka hango motan yaya ajiye saidai baya wurin motan shi hankan yasa muka fahinci yana cikin gidan ke nan. Saidai ko da muka shiga akace ai baishigo ba don su basu mansan yazo ba ai a ranan ashe yana garine mommy ta fada. Da yake yanzu ina dan shiga wurin su mu zauna sai banyi saurin komawa side din mu ba don don wayan Aisha dake hannu na ina kallon photuna a ciki. Nan nake jin Nabila na fadawa mommy