Sashe 95
Ana Dara Ga Dare Yayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
Gidanne ya koma shiru na dan lokaci kowa da abinda rayuwan shi ke raya masa kan abinda ya faru a lokacin .
Don mommy kan rayuwan ta ya gama baci da halin hjy karima wace bata yarda da Allah kan diyanta ko ita ba dan abu kadan zai faru yanzu Anty amarya zatace ai ai mata ne ture kishiya tayi mata don kawai taga bayan ta.
Yar uwa kokece a irin wanan rayuwan ki zauna ki binki imanun ki anya bakiyi zurfi ga shirka ga aikin sabawa Allah ba.
Tunda baki yarda da kaddara da duk ya sauka a kanki sai ki manta da cewa Allah mai yi a duk lokacin da yaso hakan a gareki
Ko ki koma kina dariya kan abinda ya samu wani na sheri karki manta wata rana kema yana tafe a kanki yar uwa don haka lamarin Allah yake .
Anty ko tana part din ta sai faman tunane da tsuki take ja tare da fadin jimin wanan yar iskar yar da zata lauyeni a gaban mutane tana fadin wai cikine dani har na wata uku har yaushe na gama wanka da zata kira min ciki a jikina yanzu.
Allah na tuba koda zanyi ciki ai ba yanzu ba dama kwadayin da namiji yasaka na haifo wa yan nan kai a kai don kawai ina zaton samun da namiji a lokacin.
Haka kawai zan zauna ina zuba yaya ga wanan tsohon karfina yazo ya kare na koma jagwal a cikin abokaina.
Tun tana yawan tunanen hakan har yakai ta daina zargin hakan ta gaji ta ba kanta shawara saidai washe gari saida takai kanta asibiti don bata yarda da awon da tayiwa kanta a gida ba.
Suka kara tabbatar mata da cewa su basuga komai ba a jikin ta daya danganci ciki ajikin ta don haka ta dawo gida da yamma sai gata dakin mu daidai mun dawo islamiyan yamma ke nan ina zaune.
Sallama tayi bata tsaya komai ba ta fara fadin wa umma nazo injawa yarki kunne a gidan nan kafin Alh ya dawo da ta shiga hankalin ta dani a gidan nan.
Idan ba rainin wayau ba ta yaya kamar Sahiba zata saka baki a cikin zancen mu har tana kira min wai ciki ne a jikina idan cikine ta fini sanin yadda ake daukan cikine ko kawai ta nunawa mutane ita yar zamani ne bata da kunya tasan komai.
Kamar ya tasan komai tace aiki tambayeta yadda har yakai tasan mace mai juna biyu da harta iya yanke min hukuncin ciki a jikina na dai fada maki ki mata kashedin hakan a kaina don bani da dadi idan na saka mutum a gaba tana fadin haka ta juya ta fita daga part din mu.
Umma ta jiyo ta kalleni tana fadin na fada maki ki kiyayi wanan matar Sahiba na dago ina fasin umma menayi mata ni da zata zo tana fadin wanan maganan haka a kaina sai umma tayi shiru.
Tun wanan lokacin sai naji kawai na tsani wanan matar na daina zuwa gaishe ta na daina kula diyan ta saidai hakan baisa yaran su rabu dani ba don dole na dan kama kula dasu saidai ba sosai ba.
A bangaren Alh Nuhu kuwa abin ya fara bashi mamaki yana tambayan kanshi har Alh Ali zai gagareni duk da nasan shima a tsaye yake kamar shi .
Don a zaton shi shima daddy irin abinda yakeyi daddy din keyi shima don ya kasa cin ma daddy din ya nakasa shi yadda ya saba nakasa duk wanda ya shiga mai hanci da kudundune.
A wanan halin kumane ya koma gwadawa ta wani hanya da yake ganin itace mafita na karshe da zai iya gwadawa a kan daddy din.
Yaron shi aminin shi kuma yardaden shi ya kira ya sameshi a gidan hutun shi a nan suka kulla abinda suke shitin aiwatarwa akan daddy din ya ciro kudi masu yawa ya bayar wanda abubuwan zasu kankama a gareshi yadda yake so da sauri.
Ranan ko iyalin shi sun san yana cikin farin ciki don yadda yake masu idan yana cikin nishadi haka ya kasance dasu a gidan.
Yau a falon da anty ta hanasu zama a baya a gidan, muke zaune tana dakin ta bata san da muna falin zaune ba har yakai anty hauwa ta kunna muna kallo sai hankalin mu ya dauke ga hakan.
Fa,izace ta dauko zaren kitso na kama mata kai don haka muka fara duk da ni hankalina ba a kan kallon yake ba na mayar da hankali ga kitson da mukeyi din sai jin muryan Anty mukayi a daidai lokacin da fa,iza ke fadin kan ya fara mata ciwo na dan sasauta mata kitson nake fadin hakana iya nima.
Ai yau kuma kun dawo da iskancin zaman naku nan falon ke nan ba na kashe wanan zaman naku a nan ba dama ta fada tana wani zare idanu a garesu.
Ban kula da ita ba a irin sai dariyan da nakewa fa,iza a lokacin ta juyo gareni tana fadin ga yar iska ina magana kina dariya kin daukeni mutumiyar banza ke nan.
Ni nice yar iskan na fada a cikin hausan da ba daidai ba nace look woo don abuse me with dat name again wooo.
Da mamaki anty ta bude ido tana kallona kafin tace ke bude idon ki ki dubeni banyi kama da wanda zaki raina ba a nan .
Duk barikin ki keda uwarki kar nake kallon ku gidan nan don ba zan dauki iskacin yancin arziki ba yan gida basu raina ni ba .
A wurin ki ne nake yarcin arziki amma wurin daddy da mommy ni ba yarcin arziki bane don diya nake a garesu kamar kowa.
Idan kika bincika har nafi diyan ki power a gidan nan don su din ba a san ya aka samesu ba ma a gidan nan .
Muko da kike kira da yan bariki da asalin mu da kuma nasaban mu don nasan munfi wata yar a cikin gidan nan.
Fa,iza zata tashi nace ina zaki bana zuwa ko ina a nan zan zauna tunda ba gidan uban wani naje ba a gidan uban mu muke zaune kuma daddy bai hanamu zama a nan din ba shida keda gidan sa.
Na fada ina murguda baki son na fahinci matar kanta kawai ta sani sai diyan ta bayan shi kowa ba mai mutunci bane a idonta gidan yasa na rufe ido nayi mata hakan nidana saba fada da su iya bisi ko iya wale balle anty da albarkacin daddy ta samu a wurina dama .
Sallaman gwaggo hari ne tare da danta suka shigo tun kan ta karasa shigowa gidan take fadin wai hayaniyan me nake ji haka yana tashi tun muna waje ?
Gara da Allah ya kawo ki wanan tsuntattan mage din nan daba wanda yasan asalin su tazo ta samu wuri tana son fin yan gida iya shege.
Kai hjy karima me ya hadaki da wanan kuma kike irin wanan maganan haka gaskiya haka bai dace ba don Allah ai wanan kamar yar mijinki take a wurin ki.
Yau mutanen nan suke zaune tare daku a gidan nanb ai inda sabo an saba a yanzu kun zama daya dasu haka gaskiya bai kamata ba.
Shiru falon yayi kafin gwaggo hari ta juyo kaina tana min fada nayi shiru a daidai lokacin ya shigo gidan aka shiga yi mashi sannu ana gaida shi.
Yau kam shigar kayan hausawa yayi duk da rigan irin dinkin zamanin nan ne mai tsayawa maza iya cinya din nan yayi matukar kyau dashi.
Don kwarjin shi ya fito fili ga wanan shiga da yayi don shigar ta karbe shi matuka.
Gashi da ganin shi kasan naira tayi aikinta wurin don ko shigar gwaggo hari itama abin kallo ne a lokacin.
Nan falon suka zauna daga shi har mahaifiyar shi mommy dake daki tana jin abinda ke faruwa a falon ta fito tana masu sannu da zuwa tare da gaisawa.
Wayan shine yayi kara ya dauka yana fadin ya akayi arrow duk akai shiru ana sauren shi shima din dai shirun yayi yana sauraren abinda jibrin arrow din ke fada mai take yanayin shi ya dan sauya.
Yace Okey kana jina kada kowa yayi yunkurin yin komai gani nan zuwa kana jina zan biyo jirgi yanzu inzo lagos din in sameku.
Na fadama kada kuyi komai sai idan nazo din don dama nasan da hakan zai faru ai don haka ku jirani inzo.
Yana fadin hakan ya kashe wayan shi yana dago kanshi ranshi a bace sai mahaifiyar shi tace dashi meya faru ne kuma, ?
Yayi saurin dawowa daidai yana fadin wai kayan mu aka kama shine suke son su tayar masu da rikici nace su bari inzo dai.
Gara daisu bari kazo don jami,an tsaron nan wani lokaci ba tausayi ke garesu ba anjima zan je inji meke faruwa ya fada kafin ya mayar da hankalin shi wurin mommy yana fadin.
Mommy nacewa mama ta kawoni wanan karon ina jin nauyin korafin da kike min na rashin zumunci idan mun hadu .
Mommy tayi murmushi tana fadin ka kyauta wallahi baba ko kaifa ace mutum ko yaushe kamar injin ku bakwa samun lokacin hutune a rayuwan ku wai kaida dan uwan ka kullun a zurce kuke kan aiki.
Mommy kuyi hakkuri wallahi yanayin ne na yanzu ya koma hakan ya fada yana dan sune kan shi kasa saboda nauyi ya kasa ci gaba da magana.
Amar ne dake fitowa daga part din mu ummace ta toro shi ya kirani idon the boy ne ya sauka a kan yaron haka ya kara tabbatar mai da ba karya nidin daice ya gani a kaduna.
Tunda ga kanina ya gani a gaban shi yanzu da yarbanci yaron ke fada min na mike a lokacin ne kuma Amar shima ya juya zai koma part din mu.
Alokacin na Ya mustapha din yace dashi ya abokina zo mana haka baisa ya tsaya din ba nace a harshen yaruba bakajin ana magana sai yaton yaje wutin shi inda yake zaune ga kamshin turaren shi har ya fara hawa min kai a lokacin.
Ya rike shi yana mai dan magana kus, kus wanda ba lalai bane wani yaji me yake fada mai a lokacin ga falon yayi shiru kafin ya kai hannun shi daya cikin aljihu yana ciro kudi masu yawa ya mikawa Amar din.
Mukan gaskiya munci gajiyan wa yan nan mutanen don ba zamuce mun shiga duniya mun dawo hannu sake ba ko yanzu aka bukaci wani abu a wurin mu za a samu sosai kuwa duk da ba kidayawa nakeyi abinda muke samu din ba.
Kowa falon ya fiddo da ido yana mamakin wanan kyautan daya bawa yaron daga gani daya da yayi mashi a yanzu zai bashi wanan kudin haka.
Muryan gwaggo hari ce ke fadin kai har yanzun dai kana nan da son yaran ka ashe saidai maza sune abokan shi ai mommy ta fada suka dan kwashe da dariya a iya nan na bar wurin banji sauran maganan su ba kuma na dai fito na samu sun tafi ya bada alheri mai yawa yace a raba.
Har ni an cirewa nace lah dakun barshi ai tunda amba Amir mun gode na fada a karshe naji Nabila na fadin shi ya mustapha har yanzu ba zancen aure gareshi ga yan uwan shi duk sunyi aure a dangi.
Idan lokaci yayi shima ai yi zaiyi ko ita uwar nasa data damu da hakan da farko ai yanzu naji ta sake sai a lokacin Anty Amarya ta fito kallon kowa batayi ba a falon haka tasa kai tafice daga gidan.
Falon yayi shiru bayan fitar ta Allah da ikon shi ba wanda yai maganan ta a falon har ta gaji da tsayuwa tana saurare ko zataji anyi maganan ta sai taji shiru sai hiran hausana dana fara koyo sukeyi ana kwasan dariya.
Don mommy kan rayuwan ta ya gama baci da halin hjy karima wace bata yarda da Allah kan diyanta ko ita ba dan abu kadan zai faru yanzu Anty amarya zatace ai ai mata ne ture kishiya tayi mata don kawai taga bayan ta.
Yar uwa kokece a irin wanan rayuwan ki zauna ki binki imanun ki anya bakiyi zurfi ga shirka ga aikin sabawa Allah ba.
Tunda baki yarda da kaddara da duk ya sauka a kanki sai ki manta da cewa Allah mai yi a duk lokacin da yaso hakan a gareki
Ko ki koma kina dariya kan abinda ya samu wani na sheri karki manta wata rana kema yana tafe a kanki yar uwa don haka lamarin Allah yake .
Anty ko tana part din ta sai faman tunane da tsuki take ja tare da fadin jimin wanan yar iskar yar da zata lauyeni a gaban mutane tana fadin wai cikine dani har na wata uku har yaushe na gama wanka da zata kira min ciki a jikina yanzu.
Allah na tuba koda zanyi ciki ai ba yanzu ba dama kwadayin da namiji yasaka na haifo wa yan nan kai a kai don kawai ina zaton samun da namiji a lokacin.
Haka kawai zan zauna ina zuba yaya ga wanan tsohon karfina yazo ya kare na koma jagwal a cikin abokaina.
Tun tana yawan tunanen hakan har yakai ta daina zargin hakan ta gaji ta ba kanta shawara saidai washe gari saida takai kanta asibiti don bata yarda da awon da tayiwa kanta a gida ba.
Suka kara tabbatar mata da cewa su basuga komai ba a jikin ta daya danganci ciki ajikin ta don haka ta dawo gida da yamma sai gata dakin mu daidai mun dawo islamiyan yamma ke nan ina zaune.
Sallama tayi bata tsaya komai ba ta fara fadin wa umma nazo injawa yarki kunne a gidan nan kafin Alh ya dawo da ta shiga hankalin ta dani a gidan nan.
Idan ba rainin wayau ba ta yaya kamar Sahiba zata saka baki a cikin zancen mu har tana kira min wai ciki ne a jikina idan cikine ta fini sanin yadda ake daukan cikine ko kawai ta nunawa mutane ita yar zamani ne bata da kunya tasan komai.
Kamar ya tasan komai tace aiki tambayeta yadda har yakai tasan mace mai juna biyu da harta iya yanke min hukuncin ciki a jikina na dai fada maki ki mata kashedin hakan a kaina don bani da dadi idan na saka mutum a gaba tana fadin haka ta juya ta fita daga part din mu.
Umma ta jiyo ta kalleni tana fadin na fada maki ki kiyayi wanan matar Sahiba na dago ina fasin umma menayi mata ni da zata zo tana fadin wanan maganan haka a kaina sai umma tayi shiru.
Tun wanan lokacin sai naji kawai na tsani wanan matar na daina zuwa gaishe ta na daina kula diyan ta saidai hakan baisa yaran su rabu dani ba don dole na dan kama kula dasu saidai ba sosai ba.
A bangaren Alh Nuhu kuwa abin ya fara bashi mamaki yana tambayan kanshi har Alh Ali zai gagareni duk da nasan shima a tsaye yake kamar shi .
Don a zaton shi shima daddy irin abinda yakeyi daddy din keyi shima don ya kasa cin ma daddy din ya nakasa shi yadda ya saba nakasa duk wanda ya shiga mai hanci da kudundune.
A wanan halin kumane ya koma gwadawa ta wani hanya da yake ganin itace mafita na karshe da zai iya gwadawa a kan daddy din.
Yaron shi aminin shi kuma yardaden shi ya kira ya sameshi a gidan hutun shi a nan suka kulla abinda suke shitin aiwatarwa akan daddy din ya ciro kudi masu yawa ya bayar wanda abubuwan zasu kankama a gareshi yadda yake so da sauri.
Ranan ko iyalin shi sun san yana cikin farin ciki don yadda yake masu idan yana cikin nishadi haka ya kasance dasu a gidan.
Yau a falon da anty ta hanasu zama a baya a gidan, muke zaune tana dakin ta bata san da muna falin zaune ba har yakai anty hauwa ta kunna muna kallo sai hankalin mu ya dauke ga hakan.
Fa,izace ta dauko zaren kitso na kama mata kai don haka muka fara duk da ni hankalina ba a kan kallon yake ba na mayar da hankali ga kitson da mukeyi din sai jin muryan Anty mukayi a daidai lokacin da fa,iza ke fadin kan ya fara mata ciwo na dan sasauta mata kitson nake fadin hakana iya nima.
Ai yau kuma kun dawo da iskancin zaman naku nan falon ke nan ba na kashe wanan zaman naku a nan ba dama ta fada tana wani zare idanu a garesu.
Ban kula da ita ba a irin sai dariyan da nakewa fa,iza a lokacin ta juyo gareni tana fadin ga yar iska ina magana kina dariya kin daukeni mutumiyar banza ke nan.
Ni nice yar iskan na fada a cikin hausan da ba daidai ba nace look woo don abuse me with dat name again wooo.
Da mamaki anty ta bude ido tana kallona kafin tace ke bude idon ki ki dubeni banyi kama da wanda zaki raina ba a nan .
Duk barikin ki keda uwarki kar nake kallon ku gidan nan don ba zan dauki iskacin yancin arziki ba yan gida basu raina ni ba .
A wurin ki ne nake yarcin arziki amma wurin daddy da mommy ni ba yarcin arziki bane don diya nake a garesu kamar kowa.
Idan kika bincika har nafi diyan ki power a gidan nan don su din ba a san ya aka samesu ba ma a gidan nan .
Muko da kike kira da yan bariki da asalin mu da kuma nasaban mu don nasan munfi wata yar a cikin gidan nan.
Fa,iza zata tashi nace ina zaki bana zuwa ko ina a nan zan zauna tunda ba gidan uban wani naje ba a gidan uban mu muke zaune kuma daddy bai hanamu zama a nan din ba shida keda gidan sa.
Na fada ina murguda baki son na fahinci matar kanta kawai ta sani sai diyan ta bayan shi kowa ba mai mutunci bane a idonta gidan yasa na rufe ido nayi mata hakan nidana saba fada da su iya bisi ko iya wale balle anty da albarkacin daddy ta samu a wurina dama .
Sallaman gwaggo hari ne tare da danta suka shigo tun kan ta karasa shigowa gidan take fadin wai hayaniyan me nake ji haka yana tashi tun muna waje ?
Gara da Allah ya kawo ki wanan tsuntattan mage din nan daba wanda yasan asalin su tazo ta samu wuri tana son fin yan gida iya shege.
Kai hjy karima me ya hadaki da wanan kuma kike irin wanan maganan haka gaskiya haka bai dace ba don Allah ai wanan kamar yar mijinki take a wurin ki.
Yau mutanen nan suke zaune tare daku a gidan nanb ai inda sabo an saba a yanzu kun zama daya dasu haka gaskiya bai kamata ba.
Shiru falon yayi kafin gwaggo hari ta juyo kaina tana min fada nayi shiru a daidai lokacin ya shigo gidan aka shiga yi mashi sannu ana gaida shi.
Yau kam shigar kayan hausawa yayi duk da rigan irin dinkin zamanin nan ne mai tsayawa maza iya cinya din nan yayi matukar kyau dashi.
Don kwarjin shi ya fito fili ga wanan shiga da yayi don shigar ta karbe shi matuka.
Gashi da ganin shi kasan naira tayi aikinta wurin don ko shigar gwaggo hari itama abin kallo ne a lokacin.
Nan falon suka zauna daga shi har mahaifiyar shi mommy dake daki tana jin abinda ke faruwa a falon ta fito tana masu sannu da zuwa tare da gaisawa.
Wayan shine yayi kara ya dauka yana fadin ya akayi arrow duk akai shiru ana sauren shi shima din dai shirun yayi yana sauraren abinda jibrin arrow din ke fada mai take yanayin shi ya dan sauya.
Yace Okey kana jina kada kowa yayi yunkurin yin komai gani nan zuwa kana jina zan biyo jirgi yanzu inzo lagos din in sameku.
Na fadama kada kuyi komai sai idan nazo din don dama nasan da hakan zai faru ai don haka ku jirani inzo.
Yana fadin hakan ya kashe wayan shi yana dago kanshi ranshi a bace sai mahaifiyar shi tace dashi meya faru ne kuma, ?
Yayi saurin dawowa daidai yana fadin wai kayan mu aka kama shine suke son su tayar masu da rikici nace su bari inzo dai.
Gara daisu bari kazo don jami,an tsaron nan wani lokaci ba tausayi ke garesu ba anjima zan je inji meke faruwa ya fada kafin ya mayar da hankalin shi wurin mommy yana fadin.
Mommy nacewa mama ta kawoni wanan karon ina jin nauyin korafin da kike min na rashin zumunci idan mun hadu .
Mommy tayi murmushi tana fadin ka kyauta wallahi baba ko kaifa ace mutum ko yaushe kamar injin ku bakwa samun lokacin hutune a rayuwan ku wai kaida dan uwan ka kullun a zurce kuke kan aiki.
Mommy kuyi hakkuri wallahi yanayin ne na yanzu ya koma hakan ya fada yana dan sune kan shi kasa saboda nauyi ya kasa ci gaba da magana.
Amar ne dake fitowa daga part din mu ummace ta toro shi ya kirani idon the boy ne ya sauka a kan yaron haka ya kara tabbatar mai da ba karya nidin daice ya gani a kaduna.
Tunda ga kanina ya gani a gaban shi yanzu da yarbanci yaron ke fada min na mike a lokacin ne kuma Amar shima ya juya zai koma part din mu.
Alokacin na Ya mustapha din yace dashi ya abokina zo mana haka baisa ya tsaya din ba nace a harshen yaruba bakajin ana magana sai yaton yaje wutin shi inda yake zaune ga kamshin turaren shi har ya fara hawa min kai a lokacin.
Ya rike shi yana mai dan magana kus, kus wanda ba lalai bane wani yaji me yake fada mai a lokacin ga falon yayi shiru kafin ya kai hannun shi daya cikin aljihu yana ciro kudi masu yawa ya mikawa Amar din.
Mukan gaskiya munci gajiyan wa yan nan mutanen don ba zamuce mun shiga duniya mun dawo hannu sake ba ko yanzu aka bukaci wani abu a wurin mu za a samu sosai kuwa duk da ba kidayawa nakeyi abinda muke samu din ba.
Kowa falon ya fiddo da ido yana mamakin wanan kyautan daya bawa yaron daga gani daya da yayi mashi a yanzu zai bashi wanan kudin haka.
Muryan gwaggo hari ce ke fadin kai har yanzun dai kana nan da son yaran ka ashe saidai maza sune abokan shi ai mommy ta fada suka dan kwashe da dariya a iya nan na bar wurin banji sauran maganan su ba kuma na dai fito na samu sun tafi ya bada alheri mai yawa yace a raba.
Har ni an cirewa nace lah dakun barshi ai tunda amba Amir mun gode na fada a karshe naji Nabila na fadin shi ya mustapha har yanzu ba zancen aure gareshi ga yan uwan shi duk sunyi aure a dangi.
Idan lokaci yayi shima ai yi zaiyi ko ita uwar nasa data damu da hakan da farko ai yanzu naji ta sake sai a lokacin Anty Amarya ta fito kallon kowa batayi ba a falon haka tasa kai tafice daga gidan.
Falon yayi shiru bayan fitar ta Allah da ikon shi ba wanda yai maganan ta a falon har ta gaji da tsayuwa tana saurare ko zataji anyi maganan ta sai taji shiru sai hiran hausana dana fara koyo sukeyi ana kwasan dariya.