Sashe 3
Ana Dara Ga Dare Yayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
SAHIBAT yarinya ce matashiya yar kimanin shekaru sha hudu a duniya sahibat doguwa ce kyakyawan gaske.
Tana da wani irin halitta na daban da ba a faye samun irin su ba da yawa a cikin mutane sune ake kira ace mutum kamar shi ya zauna ya tsara kanshi don kyau.
Haka launin fatan jikinta yana da haske da sheki ga jikinta a murje yana walkiya wanda hakan baiwane da kuma gado a bangaren mahaifin ta.
Ba zaka san baiwa bane hakan sai kaga irin wahalan data taso a cikin shi amma wahala da wanan rintsin bai hana fatan jikin ta sheki ba.
Duk da Sahiban ba fara bace irin sol din nan sai kuma dole a sakata a cikin farare ko a hakan sai dai kuma ko a hakan samun mai kyaun fata irin nata yana da wuya hakama mahaifiyar ta duk da wahalan da suke fuskanta na rayuwa.
Yadda Sahiba take da kyau a baiyane haka kuma take da kyau hali a boye don akwai kyakyawan zuciya da kyakyawan hali a tare da ita.
Haka idan maganan hakkurine idan anzo gun sahibata azon gidan hakkuri da juriya duk tsanani da wuyan al,amari bai wuce Sahiba ta kalleshi tayi mai murmushi ba.
Amma fa ba kowa yasan da hakan ba sai irin su iya Muluka da maman Bisi da suka kwashi shekaru a tare ne suka san wanan halin nata na boye.
Don idan ka ganta tayi shiga na bat da kama ga mazan zamani mayaudara a wurin neman abincin su ba zaka taba cewa ita keda wanan halin ba.
Amma idan mutum yana son ya gane waye sahiban na gaskiya to yazo gidan su a lokacin tana gida zai san da hakan dana fada a yanzu.
Kowa na yabon hali irin na Sahiba har kaga yarbawa nawa diyan su kwatance da ita da irin halinta na taimakawa uwarta da dan uwanta tun tana yar ficiciyar ta kuwa.
Tun tasowan Sahiba a duniya ta bude ido a cikin talauci da wahala da kunci irin rayuwa tun tana karama har dan tasowan ta din nan bata taba ganin wani abin jin dadi na zamani a tare dasu ba.
Daga fannin abinci sutura ko wani abin jin dadi komai zasuyi a rayuwan su sai da kyar da sudin goshi zasuyi shi tun dai a fannin abinci ba karamin wahala suke sha ba kafin su hada abinda zasu ciwa ransu gasu har su ukku kuwa.
Don hakane ma basu damu da wai wani dafa abinci ba donko ko sunce zasuyi din abinda zai dafa abincin a garesu shine aiki kuma.
Don hakane suka kwanmace a sayo garin kwaki da dan mangyada a yamutsa aci a tashi sai idan sun gaji da ci ko ranan data samo kudi da dan yawa wurin yin buga bugan ta zata dan sayo masu wake da bread da iya bisi ke dafawa a kofan gidan suci.
Kamar yadda Sahiba ta bude ido ta tsunci kanta a cikin kangin talaici da kakanikayin rayuwa.
Don haka ta bude ido data fara wayo taga mahaifiyarsu tana faman yawon bara dasu a cikin birnin iko din.
Har izuwa yanzu da ta karbi uwar nata ta dauke mata duk wanan wahalan don ciwo dake son ya nakasa masu mahaifiyar nasu a yanzu.
Don ga ciwo ga rashin gatan dake damun umma din yasa tun bata karasa kai hakan ba take iya kokarinta wurin fita ta nemo masu abinda zasu ci ga kanin ta karami ne sai kafa kafa sukeyi dashi don yanayin garin n a iko da ba kyau.
Tsakanin Sahiba da mahaifiyar su akwai shakuwa mai yawa don bata taba yin komai sai da yardan mahaifiyar nata takan fita yawon buga buga abinda zasuci din.
Sahiba ita ta saka kanta karatun boko na addinine ta dan samu a wurin mahaifiyar ta a gida don yanzu hakama har takai jss two a makaranta gwaunati na diyan tallakawa irin su dake can dan kasa da unguwar su kadan.
Da hakan ma yanzu ta saka kaninta Amar irin wanda take zuwa din duk a cikin dan abinda take samowa suke wanan hidiman a rayuwan su a wahalce.
Karan wayan ta dake ruri daga gefen tane ya ankarar da ita da sauri ta mika hannu ta dauki wayan tana fadin dan halas yanzu nake maganan shi a raina fa sai gashi ya kira.
Kallon ta yarta Nabila dake gefen ta tayi cikin ya motse fuska yar tace halan ya Abubakar ne ko tana danna daukan wayan take fadin shine dai.
Yar ta wani kara tabe fuska tana kawar da kanta gefe daya ta dauki wayan tana fadin ni har ka ban tsoro da banji kiran ka ba tun jiya nasan kuma ku ba kiran ku akeyi ba idan baku kuka kira ba.
Yace wallahi tun jiya kina raina aikine kawai da yai min yawa da gajiya kuma ya hana in kira ku jiyan.
Sai kuma ya juya yana gaida ita da kwana tare da tambayan ta mutanen gida tace duk suna lafiya sun raka hjy karima unguwa dagani sai Nabila ce a gidan yau.
Yace dama abinda suke so ke nan fita yawo aje unguwa basu da wani abin yi sai gulma a rayuwan su.
Kai Modibo har yaushe ka zauna kasan abinda yaran nan suke so yanzu kai da kullun kana faman yawon bin jirgi zuwa kasa kasa.
Dariya abin ya bawa Abubukar wanda mahaifiyar shi ke kira da Modibo don sunan kakanshi yaci ta wurin uba.
Ni fa yanzun ba abinda ke damuna kamar inga ka tsaya da gaskiya kan zamcen auren nan naka shine muradina a kullun.
Hajja Addah har nawa nake da kike min zancen aure a yanzu duka duka fa ban ko kai talatin ba balle in fara zancen aure.
Zancen banza ke nan me kake nema a duniyan nan da baka samu ba a yanzu kudi ilimi duk Allah ya baka fiye da yadda ake zato.
So kake duniya ta samu a baki dagani har mahaifinka da abokan shi kema tayin yayan su ka aura ?
Ganin ran mahaifiyar nasu kamar ya baci abinda yaki jini ya gani ko yaji ke nan yasa a cikin wasa yace yanzu ni hajja Addah ina nake da lokacin neman wata yarinya can sai ki nema min ai wace ta dace dani ko ?.
Cikin jin dadin zancem shi uwar ta sake murmushi ta yadda har yake jiyo ta a waya tana fadin to kokai fa modibo ka tsaya kana wahal da kanka dana mutane.
Aure fa shine cikar kamalan mutum yanzu kana aure darajan ka zai kara hauhawa ko ga mutane zasuyi ma kallon cikkaken mutum a idon su sabanin hakan da kake zaune kai kadai.
Dariya yayi kafin yace da ita wai daddyn mu ya dawo kuwa ko har yanzu yana can ?
Wanan zance kakeyi ai sai lokacin da muka ganshi yanzu kuma don dama ya fada muna wanan karon zai dan dauki lokaci a can idan ya tafi.
Allah ya dawo dashi lafiya ya fada tace amin kadai kula da kanka a cikin arna kun nan don Allah.
Insha Allahu hjy Addah babu abinda zasuyi dani sai Allah na zauna ma acikin wa yanda suka fisu zama arna Allah ya fito dani lafiya balle nan da suke da surkin musulmai a tare dasu ga hausawan mu ma ko ina a garin kamar kana arewa.
Allah ya tsare tayi mai kafin suyi sallama dashi tana jin tausayin dan nata da son shi yana karuwa mata a zuciya.
Idan bata manta ba haka mahaifin su ya tashi shima ya fara dan buga buga har yakai yanzu yana ketarawa waje ya saro kaya.
Shima a bangaren Abubakar din yana aje wayan nisawa yayi yana shafo kanshi zuwa fuska kafin ya furzo da iska mai zafi daga bakin shi.
Yana ci gaba da tunanen matsalan gidan su din da yayi yawa a yanzu koba a fada ba yasan iyayyen nasa mata suna hakkuri da halin mahaifin su a yanzu da can din ma da sam daddy din baida lokacin su sam sai idan yaso.
Tana da wani irin halitta na daban da ba a faye samun irin su ba da yawa a cikin mutane sune ake kira ace mutum kamar shi ya zauna ya tsara kanshi don kyau.
Haka launin fatan jikinta yana da haske da sheki ga jikinta a murje yana walkiya wanda hakan baiwane da kuma gado a bangaren mahaifin ta.
Ba zaka san baiwa bane hakan sai kaga irin wahalan data taso a cikin shi amma wahala da wanan rintsin bai hana fatan jikin ta sheki ba.
Duk da Sahiban ba fara bace irin sol din nan sai kuma dole a sakata a cikin farare ko a hakan sai dai kuma ko a hakan samun mai kyaun fata irin nata yana da wuya hakama mahaifiyar ta duk da wahalan da suke fuskanta na rayuwa.
Yadda Sahiba take da kyau a baiyane haka kuma take da kyau hali a boye don akwai kyakyawan zuciya da kyakyawan hali a tare da ita.
Haka idan maganan hakkurine idan anzo gun sahibata azon gidan hakkuri da juriya duk tsanani da wuyan al,amari bai wuce Sahiba ta kalleshi tayi mai murmushi ba.
Amma fa ba kowa yasan da hakan ba sai irin su iya Muluka da maman Bisi da suka kwashi shekaru a tare ne suka san wanan halin nata na boye.
Don idan ka ganta tayi shiga na bat da kama ga mazan zamani mayaudara a wurin neman abincin su ba zaka taba cewa ita keda wanan halin ba.
Amma idan mutum yana son ya gane waye sahiban na gaskiya to yazo gidan su a lokacin tana gida zai san da hakan dana fada a yanzu.
Kowa na yabon hali irin na Sahiba har kaga yarbawa nawa diyan su kwatance da ita da irin halinta na taimakawa uwarta da dan uwanta tun tana yar ficiciyar ta kuwa.
Tun tasowan Sahiba a duniya ta bude ido a cikin talauci da wahala da kunci irin rayuwa tun tana karama har dan tasowan ta din nan bata taba ganin wani abin jin dadi na zamani a tare dasu ba.
Daga fannin abinci sutura ko wani abin jin dadi komai zasuyi a rayuwan su sai da kyar da sudin goshi zasuyi shi tun dai a fannin abinci ba karamin wahala suke sha ba kafin su hada abinda zasu ciwa ransu gasu har su ukku kuwa.
Don hakane ma basu damu da wai wani dafa abinci ba donko ko sunce zasuyi din abinda zai dafa abincin a garesu shine aiki kuma.
Don hakane suka kwanmace a sayo garin kwaki da dan mangyada a yamutsa aci a tashi sai idan sun gaji da ci ko ranan data samo kudi da dan yawa wurin yin buga bugan ta zata dan sayo masu wake da bread da iya bisi ke dafawa a kofan gidan suci.
Kamar yadda Sahiba ta bude ido ta tsunci kanta a cikin kangin talaici da kakanikayin rayuwa.
Don haka ta bude ido data fara wayo taga mahaifiyarsu tana faman yawon bara dasu a cikin birnin iko din.
Har izuwa yanzu da ta karbi uwar nata ta dauke mata duk wanan wahalan don ciwo dake son ya nakasa masu mahaifiyar nasu a yanzu.
Don ga ciwo ga rashin gatan dake damun umma din yasa tun bata karasa kai hakan ba take iya kokarinta wurin fita ta nemo masu abinda zasu ci ga kanin ta karami ne sai kafa kafa sukeyi dashi don yanayin garin n a iko da ba kyau.
Tsakanin Sahiba da mahaifiyar su akwai shakuwa mai yawa don bata taba yin komai sai da yardan mahaifiyar nata takan fita yawon buga buga abinda zasuci din.
Sahiba ita ta saka kanta karatun boko na addinine ta dan samu a wurin mahaifiyar ta a gida don yanzu hakama har takai jss two a makaranta gwaunati na diyan tallakawa irin su dake can dan kasa da unguwar su kadan.
Da hakan ma yanzu ta saka kaninta Amar irin wanda take zuwa din duk a cikin dan abinda take samowa suke wanan hidiman a rayuwan su a wahalce.
Karan wayan ta dake ruri daga gefen tane ya ankarar da ita da sauri ta mika hannu ta dauki wayan tana fadin dan halas yanzu nake maganan shi a raina fa sai gashi ya kira.
Kallon ta yarta Nabila dake gefen ta tayi cikin ya motse fuska yar tace halan ya Abubakar ne ko tana danna daukan wayan take fadin shine dai.
Yar ta wani kara tabe fuska tana kawar da kanta gefe daya ta dauki wayan tana fadin ni har ka ban tsoro da banji kiran ka ba tun jiya nasan kuma ku ba kiran ku akeyi ba idan baku kuka kira ba.
Yace wallahi tun jiya kina raina aikine kawai da yai min yawa da gajiya kuma ya hana in kira ku jiyan.
Sai kuma ya juya yana gaida ita da kwana tare da tambayan ta mutanen gida tace duk suna lafiya sun raka hjy karima unguwa dagani sai Nabila ce a gidan yau.
Yace dama abinda suke so ke nan fita yawo aje unguwa basu da wani abin yi sai gulma a rayuwan su.
Kai Modibo har yaushe ka zauna kasan abinda yaran nan suke so yanzu kai da kullun kana faman yawon bin jirgi zuwa kasa kasa.
Dariya abin ya bawa Abubukar wanda mahaifiyar shi ke kira da Modibo don sunan kakanshi yaci ta wurin uba.
Ni fa yanzun ba abinda ke damuna kamar inga ka tsaya da gaskiya kan zamcen auren nan naka shine muradina a kullun.
Hajja Addah har nawa nake da kike min zancen aure a yanzu duka duka fa ban ko kai talatin ba balle in fara zancen aure.
Zancen banza ke nan me kake nema a duniyan nan da baka samu ba a yanzu kudi ilimi duk Allah ya baka fiye da yadda ake zato.
So kake duniya ta samu a baki dagani har mahaifinka da abokan shi kema tayin yayan su ka aura ?
Ganin ran mahaifiyar nasu kamar ya baci abinda yaki jini ya gani ko yaji ke nan yasa a cikin wasa yace yanzu ni hajja Addah ina nake da lokacin neman wata yarinya can sai ki nema min ai wace ta dace dani ko ?.
Cikin jin dadin zancem shi uwar ta sake murmushi ta yadda har yake jiyo ta a waya tana fadin to kokai fa modibo ka tsaya kana wahal da kanka dana mutane.
Aure fa shine cikar kamalan mutum yanzu kana aure darajan ka zai kara hauhawa ko ga mutane zasuyi ma kallon cikkaken mutum a idon su sabanin hakan da kake zaune kai kadai.
Dariya yayi kafin yace da ita wai daddyn mu ya dawo kuwa ko har yanzu yana can ?
Wanan zance kakeyi ai sai lokacin da muka ganshi yanzu kuma don dama ya fada muna wanan karon zai dan dauki lokaci a can idan ya tafi.
Allah ya dawo dashi lafiya ya fada tace amin kadai kula da kanka a cikin arna kun nan don Allah.
Insha Allahu hjy Addah babu abinda zasuyi dani sai Allah na zauna ma acikin wa yanda suka fisu zama arna Allah ya fito dani lafiya balle nan da suke da surkin musulmai a tare dasu ga hausawan mu ma ko ina a garin kamar kana arewa.
Allah ya tsare tayi mai kafin suyi sallama dashi tana jin tausayin dan nata da son shi yana karuwa mata a zuciya.
Idan bata manta ba haka mahaifin su ya tashi shima ya fara dan buga buga har yakai yanzu yana ketarawa waje ya saro kaya.
Shima a bangaren Abubakar din yana aje wayan nisawa yayi yana shafo kanshi zuwa fuska kafin ya furzo da iska mai zafi daga bakin shi.
Yana ci gaba da tunanen matsalan gidan su din da yayi yawa a yanzu koba a fada ba yasan iyayyen nasa mata suna hakkuri da halin mahaifin su a yanzu da can din ma da sam daddy din baida lokacin su sam sai idan yaso.