← Book details Sai Ka Aureni Dole Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 95 OF 289

Sashe 95

Sai Ka Aureni Dole Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ya'yanta babu dare ba rana,allah yakawo yaranta sauki dan yanzu babu laifi abubuwa sun dan soma canzawa ba kmr da ba . hjy harira bata ba tasanya zuciyarta hkr da danga akan mugun nufinta daya koma kanta ita da yaya'ta ba. ta sake yunkurin ziyarta wani kungurimin boka dataji labarin akinsa naci tkmr yanka wuka . misalin karfe shida da rabi na safiya hjy harira tai shirin zuwa gurin boka dake kauyen jatau sbd anan ne boka kankeli yake zaune . ta nufi tashar motar dazata kai ta wannan kauyen. tafiyar awa biyar ta kai su wannan gari byn ta sauka a mota ta fara bin kwatance da aka yi mata nan ma sai datayi tafiya me tsawo cikin daji yake zaune gun cike makil da mata ba nmj ko daya dan hk itama tabi jerin masu son ganin boka lokacin dayazo kan hjy harira yasoma koro mata abinda ke tafe daita tayi matukar mamaki hkn boka yana gama koro mata bayani sai ya kece da wata muguwar dry hhhhhhhhhh hhhhhhhhhh wacce tasanya har sai da bukkar da suke ciki ta girgiza tsoro yayi matukar kama hjy harira . zaune kawai take agaban boka jikinta na tsuma wanda shi km tunda yagama muguwar dryarsa ya dukufa yana duban kasa dayake duba dashi. ban da zane da yatsun 3 babu abinda yake acikin yashin kasa . bayn yagama jero abinda ke tafe daita. to agurin wannan bokan ne ta dan samu saukin lamarin da yadda za'a yi arzikinsu ya dawo garesu. boka ya dago yacigaba dayi mata bayani kmr hk lallai asirin da kikayi abaya bazai taba karyewa ba. sai dai akwai mafuta ta hanya daya dazakibi jikinta na rawa da bakinta tace Allah ya taimaki boka meye shi..? ai ko wace hanya ce boka ina tabbar maka da zanbishi domin dawowa da arzikina dana ya'yana , shi wannan hanyar ba wata hanya bace face kisa jininki su dinga aurataya da jinin wanda talaucin bai tabashi ba acikin dakin ita matar da kikawa asirin . ta hk ne kawai arzikin dakika rasa zai dawo gareki har ma zai iya fin nada.. duk da tashiga rudu da tashin hankali jin abinda boka yace amman hkn bai hanata bayyanar da tsantsar farincikinta a filli ba. Allah ya taimaki boka duka naji bayaninka wannan bayanin naka shi yafi komai sauki da sanyaya min zuciya amman kafin nan boka ina son kabani lakanin da zan mallaki me arzikin cikinsu wanda shine yafi kowa shahara arziki acikinsu. ta yadda mgnta kadai zai dinga ji a duniya. zan baki lakanin da duk abinda kikace yayi zaiyi amman bazaki taba mallakeshi duka ba mkr yadda kike so. sbd akwai tsari sosai ajikinsa shi mutun ne me son ibada da kusanta kanshi ga allah hk ma mahaifiyarsa bata bacci gurin tsayuwar dare. amman zamu tura masa aljani lakatu wanda zai dinga shagalta dashi akan lamarin ibadarsa da zarar hkn ta kasance zamusan abu yi. sai abu nagaba boka ina son akawar mun da mahaifiyar yaran a doron duniya domin barinta a doron kasa zai iya jawowa aikina nakasu.nasan matsawar tana raye kudirina bazai taba yiwuwa ba akan yaran. . angama ai duk abinda mutun ya furta anan ya tabbatu ..tashi maza kije bukatarki zata biya ki ajiye kudi a can ya nuna mata wata tukunya dake cike da jini. hjy harira tace ciki zan saka kudin? yace eh ina ruwanki? yayi mgnr yana daka mata tsawa . ta razana matuka jikinta na kirma ta saka kudin cikin wannan tukunyar take kudin ya bace bat. ko tsaya batayi ba ta fice daga cikin bukkar. ta dawo gida ta shiga lamuranta yau kowa yaganta yasan tana cikin farinciki maramisaltuwa wanda yaushe rabon da anganta hk. duk inda ta wulga acikin gidan da idanu saratu da hjy babba suke binta dashi hk ma yaya'ta har da jikoki. " tmbyr duniya sukayi mata akan sabon yanayin da suka ganta ciki . sai dai tayi murmushi tace yau ina cikin farinciki.. farinciki nake ji. ina cikin farinciki kuma kuyi farinciki.. ba'acika kwana uku da zuwan hjy harira gurin boka ba, aiki yasoma aiki akan hjy babba . dan gama hirarta keda wuya a tsakar gidan nasu lokacin an kawo mata jinjirar jikarta aliyya. ta amshi yarinyar tare da mikewa tana mata wasa, warafah'na'u makanan alliyu ...!!! shi take ta maimaitawa har tashige uwar dakanta . wasa take yarinya amman yarinyar sai tsalla kuka take kmr ranta zai fita tace kai yar nan daga kawoki sai kuka bari na kira wace ta kawoki ta dawo ta daukeki nasan yanzu hk bata karasa gida ba. ta dan leko tana kwallawa jannat kira. jannat takaraso hjy gani ungo ki nemo number rashida ta dawo ta dauki yarinya nan. jannat ta amshi wayar da aliyya ahannuta tasoma nemam number rashida cikin sa'a tasamu tace ta dawo inji hjy babba sannan ta katse kiran. cikin minti goma rashida ta dawo ta dauki aliya dake tsalla kuka ai ko fita get din gidan ke da wuya yarinya tayi tsit har da ajiyar zuciya. to byn fitarsu ne fa ciwo , ranga ranga ya rufe hjy babba . nan aka kira mahaifina yazo jikinsa na rawa tare da motar hospital aka kwasheta sai hospital din babban birnin Cotonou ana zuwa daita kai tsaye special room aka nufa daita kasancewar matsayin da "danta" ke dashi a garin. likitoci suka zagayeta suna dubata tare da bata taimakon gaggawa . kafin kace me tuni gbdy koina a hospital din cika makil da yaya da jijikonta kowa ka kalli fuskarsa cike take da tsananin damuwa . iyayenmu sai kuka suke sbd ganin jikita ya mace har wuyanta ya karye wasu shashi na jikinta yasoma shanyewa idanunta a rufe gashi babu bakin mgn sai numfashi shima da kyar take fitar da shi. likitoci suka sakamata oxygen abin janyo numfashi gbdy hankalin ya'yan hjy babba ya sake tashi ganin yadda mahaifiyarsu take zabure zabure ga oxygen abakinta . abinci ma ta allura ake bata ta hanci . mahaifina yafi kowa shiga tashin hankali ya fashe da kuka agaban tarin dubban mutane abinda banta gani ba kenan ,a tun tasowata sai ranar. wannan shine Karo na farko da zanga hawaye a idanunsa koda hjy yusif ya rasu banga yayi irin wannan kukan ba. kuka yake sosai wanda yasa gbdynsu suka taru suna kuka mazansu da matansu tare da rungume junansu suna kuka suna rarrashin kansu tare da yiwa mahaifiyarsu addua likitoci ne ke kan basu hkr. su hjy saratu da hjy harira da ya'yansu duk son zo lokacin da hjy harira tazo addua ta dinga yi aranta Allah yasa hjy babba ta mutu ayanzu ayanxu. tsawon kwana uku kennan likitoci na kan kokarin ganin hjy babba ta dawo daidai amman ina ciwo sai gaba yake. gbdy a iya bincike likitoci sunyi amman basu gane kan ciwon dake damunta ba. dan hk suka ce zasuyi mata general check up hk aka sakata cikin computer tsawon lokaci sannan aka fito daita still the same result suka gani babu wani ciwo dake damunta byn hawan jini wanda km daman tana dashi . mahaifina yace zai fitar daita kasar waje alokacin likitoci sukace ya barta dan koina zai kaita the same result zasu fada masa . ya saka musu kuka idan baza barni na fita daita ba ku cire mata wannan oxygen din dake sata zabura kayi hkr babu yadda zamuyi wannan shine damar mu ta karshe idan aka cire mata komai zai iya faruwa ba. hk aka dinga jinyar hjy babba a hospital yayinda gbdy sorounding din hospital din koina ka kalla tarin jikoki ne da ya'ya ana jajantawa juna. su kansu likitocin sunyi mamakin tarin ya'yanta da jijikoki sbd alokacin kowani daki na ya'ya hjy babba a mata kawai ma akwai me yaya goma mazan kuwa akwai me sama da shabiyar tunda dukansu mata biyu biyu sukayi mahaifina ne kawai keda ya'ya bakwai da mata daya. ganin ciwon yaki ci yaki cinyewa sai ma tsamari dayayi yasa aka meidaita gidan mahaifina dake cikin birnin Cotonou. mahaifiyarmu tacigaba da jinyarta abinda ya bakantawa hjy harira zuciya kenan har da cewa meyasa gasu za'akaita wani guri su meye amfaninsu kenan idan ma mutuwar ce ai gara ta mutu adakinta hk dai su mahaifina da yan'uwansa suka toshe kunnnuwansu.ita ko hjy harira taso ne a dawo da hjy babba daita gidan tasamu damar karasata gbdy ta huta wani jinyace jinyace .mahaifina bai watsar da lamarin hjy harira da hjy saratu tare da ya'yansu ba duk mahaifiyarsa bata cikin gida bai fasa kai duk abinda yasaba ba tare tallafi da duk abinda suke so. umman su'ad taja dagon numfashi ta sauke sanda ta kawo nan tana kallon tilon diyarta hawaye na zubo mata me taba zuciya da ban tausayi su'ad tasanya hannuwanta duka tana goge mata hawayen dake tsiyayowa wasu na sake zubowa, batare da tace mata komai ba sbd itama kanta hawaye tausayi ne ke gangaro mata.. umman su'ad tacigaba byn wani lokaci a sirin da hjy harira tayi akan mahaifina shima yasoma tabashi koma nace yarigada ya taba mahaifina ,dan kusan yanzu sai abinda hjy harira tace masa gashi mahaifiyarsa babu yadda take sai godiya gurin Allah . da fari da nasiha da siyasa tasoma tun karar mahaifina akan su karfafa zumuncinsu,daman km ga mahaifina da tsananin son zumunci, wannan mgnr zumunci datayi yasashi jin dadi sosai har ya kai ga cewa tabbas zumunci abu ne me kyau duk wanda baiyishi anan duniya ba zaiyi shi alahira, alahiran ma acikin jahannama. ,mahaifinku har yakoma ga allah kalmarsa kenan kuyi zumunci atsakaninku inji cewar hjy harira shi dai mahaifina yayi mamakin jin ta fadi hk kasancewar lokacin da mahaifinsu ke jinya dukka ya'yansa mazane akasa . har ya cika da kallamatul shahada bai san lokacin da mahaifinsu yace hk ba amman ai abune me kyau din ya fadi hk aranshi. duk sanda zaije gurin hjy harira da hjy saratu dubo lfyrsu. ita hjy harira zata tsareshi da zance zumunci har dai ta kai ta kawo ta fito masa kiri kiri akan manufurta da take son ayi. dawood ..takira sunan mahaifina ina son karfafa zumunku da yan'uwanka yafi wanda kukeyi a yanzu . dan hk na zarta da wani hukunci batare da masaniyarka ba sbd aganina kai ma kmr dan dana haifa ne. hukuncin
Chapter 95 · 0% Book details