Sashe 179
Sai Ka Aureni Dole Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ya lalace dan kotu ce zata rabamu da kai.. ko kallon mama ak baiyi ba yafige motarsa aguje yabar gidan. da gudu mama ta koma ciki ta dauko key mota da ruwa a cup takaraso inda zainba ke kwance tmkr matacciya tashiga zuba mata ruwa amman shr kake jin zeey bata motsa ba me gadi da direbanta tasa suka taimaka mata aka saka zeey cikin mota sai promise hospital dake dopemu road suna isa aka a turo gadon marasa lfy aka daura zeey aka nufi dakin doctor daita aka shiga bata taimakon gaugauwa da kyar likitoci suka samu nasarar dawo da numfashinta wanda zuwa lokacin hankalin kowa a dagin ya tashi asibiti makil da dangi ana taya juna jimami tare da son sani dalilin dayasa AK yayi wa zeey irin wannan duka kmr ma yaso kasheta ne. yana barin gidansu zeey kai tsaye gidansu ya nufa yashige part dinsa ya kulle kansa ciki yana kuka me taba zuciya kmr wani karamin yaro duk wuni ranar babu inda yaje km babu wanda yasan yana cikin gidan har dare a ranar sam kasa bacci yayi tashin hankali dayake ciki zuciyarsa tayi rauni tunani abinda ya dauki tsawon lokaci yana aikatawa yake zuwan masa daki da tsaya masa arai ,shi bai taba kusantar matar kowa ba sai gashi an kusanci matarsa wace yafi yarda daita , wace yake tunani yar iska ce yar jagaliya tantira yar gaba da fatiha wai ita ce ta kawo masa abinda yafi bukata daga diya mace wayyohhly Allah kaicona ni abdulkabir tun yanzu an soma fancewa akan matar aurena Allah na tuba kayafemin kuskurena dana aikata abaya yana kuka har da shesheka .. tsawon sati daya zeey na jinyar kanta a hospital batare da ansan dalilin dayasa ak ya nemi kasheta ba ,kwananta goma aka sallamota kai tsaye daga hospital gidan dady akayo daita kmr yadda dady yabada umarni.. parlour 'n dauke da mutane mafi kusanci da juna, dady ne sai alhj garba da maman zeey wace take cika tana batsewa sai ammi da hjy kakar AK itama acike take fam dan sai surutai take yadawa tana zagin AK tare da tsine masa albarka . da kyar dady yasamu ya shawo kanta tayi shr sannan yasoma tmbyr AK abinda ya hadusu da zeey har yayi mata irin wannan lahanin batare da yasoma zuwa garesu ba . yana huci kmr kumurcin maciji yake kallon zeey ransa a matukar bace dan shi kwata kwata bai so wannan zaman ba "ki gaya musu abinda kikayi..... yayi mgnr yana nunta da hannusa kuka tashigayi tana basa hkr "dan ubanki hakurin uwar me keki bani byn kin cuceni wallahi idan baki gaya musu ba sai miki dukan mutuwa agabansu sannan km da bakinki zaki gaya musu abinda kika min yayi kanta zaiyi kwallo daita har ya daga kafarsa daya ammi da dady suka buga masa tsawa "kana hauka ne abdul ka dawo hankalinka man kabar yarinyar tasamu natsuwar zuciya, duk ka wani firgitata inji cewar ammi yaja baya yana huci tare da jingina goshinsa da bango wasu zafafan hawaye ne suka shiga gangarowa bisa kuncinsa yana jin daci yadda ya riski zeey wace ya yarda daita ya amincewa fiyye da komai magangun akil ne suka shiga zuwan masa daki daki cikin zuciyarsa da kunnuwansa suna masa kuwa zeey ce tasoma nemana akan na dinga biya mata bukata ..... hjy ranta yafi na kowa baci ganin yanayi har gagin da AK yake dan hk ranta a bace tace "ke dan ubanki baxaki fadi abinda ya hadaku ba tun da shi mara kunyar yaki fada . "kiyi mana bayani asan ta inda za'a karbar miki yancinki dan ke ba jakar gidan uwarsa da ubansa bace balle yayimiki irin wannan dukan ,ko wace tayi prison yar gaba da fatiha ma ba'ayi mata hk ba sai ke da kike da gata da galihu za'a nemi awulakantaki wallahi bazan yarda ba sai idan karfina ya kare takarasa mgnr tana zabgawa ak harara .. zeey ta sake rikecewa tana matso ruwan hawaye daga idanunta masu dumi tana yarfe hannuwanta gbdy ta rude ta gigice ta fita cikin haiyacinta ,ta ina zata fara bayani abinda ya hadasu ganin da ak yayi bata da niyyar cewa komai yasa ya juyo a fusace on expect zeey taji ya dauketa da wani gigitaccen mari "ki gaya musu abinda kikayi nace..... ammi ta zabura ta mike tsaye jikinta na rawa tana kallon idanunsa bata taba ganinsa cikin bacin rai irin hk ba amman duk da hk bazatabari yaciwa zainab mutunci agabanta ba duk irin cin fuskar da suka mata, dan hk bakinta na rawa" abdul kalleni nan sai lokacin AK ya waigo inda ammi take yana kallonta yana kuka "ni mahaifiyarka ce ina umartaka daka gaya mana abinda ya hadu da zainab ..... banason ka boye min komai bi son aikata abinda ammi ta umarcesa amman bazai iya kunyatata cikin dagin mahaifinsa ba dan ya koma da baya da baya ya jingina bynsa da bango parlour 'n ammi takarasa garesa ta janyo hannunsa zuwa mazaunenita ta zaunar dashi tana sake tmbyrsa "ina sauraronka abdul ..ahankali ya dago yana kallon gbdy mutane dake zaune a falon wadan ke jiran jin abinda zai ce idanunsa na sauka akan zeey yaji damuwarsa ta ninku zuciyarsa ta harzuka ya dinga jin kmr ya kamota ya shake mata wuya ta mutu kowa ya huta domin haihuwar irinsu asara ne ya kawar da idanunsa zuwa kan ammi "ammi ya kira sunan mahaifiyarsa "ina jinka abdul. " ban samu zeey acikakkiyar mace ba ammi sauran wanina na aura batare da na sani ba. "maganar banza mgnr iska zance banza inji mutane banza wannan ai zance iska ce yau tsawon wata uku da wasu satinnai da kai maka mata gidanka amman baka tashi zuwa wa mutane da zance iskar ba sai yau to ni jikata ba yar iska bace irinka sai dai kaje can ka nemi yar iska wannan yar mutunci yar asali ce takowani bangare dan hk kasake tauna zancenka akanta dan bazan lamunta ba ehhe.. ai gama jin zantukkan hjy ke wuya ya mike tsaye a tunzure ya shiga kwance belt dinsa ya dinga laftawa zeey a gbdy jikinta yana furta tayi mgn tagaya musu yadda ya sameta ,hjy da maman zeey sukayi kansa suna ihu da kururuwa, hjy "na ihun zaka kashe min ita ne? adamu kana kallon danka zai yi kisan kai wallahi idan ka kasheta baxan yarda ba yadda ka kasheta hk kai zan kaika koto anyeke maka hukuncin kisa, yayinda ammi da dady suka shiga tashin hankali gbdy suka dawo tmkr mutun mutumi azaune idanunsu ne kawai akan ak. hjy da maman zeey da alh garba ne suke kokarin amsarta a hannu AK amma su ammi hnklinsu gbdy baya gangar jikinsu sbd mgnr ak ya shigesu ya taba musu zuciya har yaso ya tarwatsa zuciyoyinsu. tsawo mint 15 hjy na kiciniyar tare zeey daga dukan AK sannan dady ya yunkura yayi karfin halin yin mgn a sanyaye "abdul cak ak ya tsaya yana huci kmr zaki "kar ka sake dukan yarinyar mutane AK ya furzar da iska me dumi daga bakinsa yana aunawa zeey wani kafirin kallo me tattare da tsagwaron tsana. hjy kiyi hkr ki zauna musan yadda za'a yi da lamarin sannam ya fuskanci zeey"zainab yakira sunanta kinji abinda mijinki yace meye gsky la.....tun kafin dady yakarasa mgnrsa AK yace "no no dady kayiwa girman allah ka daina cewa mata domin tun jiya na saketa bazan taba iya cigaba da zama daita ba . hjy tayi saurin dafe kirji bakinta ya shiga furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun shima dan taji mutane dake gurin suna furtawa ne takama kalma tashiga furtata tana maimaitawa "amman anyi takadirin yaro byn wannan dukan dakayi mata kmr zaka kasheta har da saki ? "kwarai kuwa hjy na saketa domin saki shine ya cancaci wannan muguwar azalumar mayaudariyar me fuska biyu ... "ni kake gayawa mgn ina mgn kana meida min to badani kake da wadan dake zaune agabanka dasu kake badani shiryayye dan bazance tsinane ba.. " kima ce min tsinanne ko kin tsine min ai bazai kama ba ga wanda zai kama nan " a matukar tsawace dady ya katseshi ta hanyar cewa "bana son sake jin bakinka matsawar bani na lamunce maka ba inji cewar dady. AK yaja numfashi da ajiyar zuciya atare yana kallon inda ke zeey yana jin wani irin bacin rai na ratsashi tare da tsagwaron kiyayyarta na huda kahon zuciyarsa "ina jinki zainab kiyi mana bayani abinda abdulkabir ya fada akanki gaskiya ne ko karya ne ? ta matso ruwan hawaye tare da sa hannuta ta goge hawayen dake bin kuncinta abubuwa dayawa ne suka shiga kai kawo cikin zuciyarta tunani abinda zata fada cikin sauki takeyi ,take wani dabara yazomata dan hk cikin muryar kuka tace "gskiya ya fada dady.. " gsky fa kikace zainba ta girgiza kai ala'mun eh. . "laila a illallahu muhammadur rasulillahi salillahu alaihi wa salam. gsky ne zainba abinda abdulkabir ya fada mana gsky ne zeey ta sake daga kanta "gsky na fada amman akira su'ad agabanta komai ya faru lokacin da ta saka yan daba suka tafi dani alokacin komai ya faru da fari naso nagayamuku amman na rasa ta inda zan soma," dana san hk abdulkabir zai qalubanceni da tun a wannan lokaci na sanar masa da komai. "karya kike munafuka algunguma idan kika sake kiran sunan matata anan sai na balleki na tattara katsuwanki na watsar a teku kowa ya huta haihuwar irinki ko asarar rayuwa wata razananniyar tsawa dad'y ya buga masa " bance kar na sake jin mgnrka ba . alhaj garba ne yace akira su'ad din aji tabakinta take ammi wace jikinta ke rawa takira layin su'ad . cikin mintina da ba wuce goma ba sai gata tashigo sanye cikin bakaken kaya sai sheki sky din ke tana baza kamshi , tana karasa shigowa taji gabanta ya bada rasss yashiga faduwa zuciyarta tashiga tsalle duk da tasan akwai meeting din daake gabatarwa amman batasan musababbin taron ba. alhj garba ya umarci zeey data sake maimaita abinda ta fada dazu babu kunya balle tsoron Allah zeey tashiga zayyano karya da gsky . Jin furuncin zeey dake shiga cikin kunneta yasa tasoma yin Kasa kasa daga tsayen datake wanda kadan