Sashe 92
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Yana kwancen yake tambayar zuciyar sa" miye dalilin hakan? Ashe 'dan uwa bazai ta6a sakin ransa ya rayu da 'dan uwan sa cikin amana da gaskiya ba?
Kuma wai duk akan dukiya da Allah ne ke bada ita..."
Zuciyar sa nawi yake jinta ga numfashin sa take ya sar'ke sa yake fita da 'kyar, banda hawaye babu abinda yake iya yi a wannan halin.
Cikin ransa sa yake jin kamar ya tashi yayi ta jibgan yayan nasa har sai ya illata shi saboda cin amanar da yayi masa, ya nuna masa dukiya tafi masa komai a rayuwar nan ciki kuwa harda zumuncin da Allah ne ya ha'da tsakanin su yayo su daga tsatso 'daya, to laifi ne dan Allah ya fifita 'dan uwanka akan ka? Laifi ne dan Allah ya bawa 'dan uwanka dukiya kai bai baka ka? Shin kasan naka kyautar da ya ajiye maka?
'Kilan duk zafin neman ka ba zai ta6a baka dukiyar ba saboda babu ita cikin 'kaddarorin rayuwar ka ta duniya to meyasa zaka takurawa kanka?
Idan kayi ha'kuri ma kabi Allah kabi manzon sa kayi tawakkali babu mamaki ka dace da samun taka dukiyar acan matabbata tana jiran ka, inda ko wani abu zakayi da shi ba zai ta6a 'karewa ba sannan Allah ba zai ta6a gajiya da baka ba, haka nan kuma ba zai ta6a raba ka da aljannar sa ba..to menene yafi wannan fisabilillahi..?"
( ALLAH KASA MU DACE DA NI'IMAR KA DUNIYA DA LAHIRA)
" Amma wannan wace iriyar rayuwa ce, ashe mutun ba zai iya ri'ke 'kaddarar da Allah ya 'dora masa ba sai ya nuna nasa ikon ta hanyar da be dace da karantarwar musulunci ba, me yasa muke zalunci muke dagewa da cewa sai mun yi arzi'ki ko ta halin 'ka'ka bacin a littafin 'kaddarar mu Allah bai tsara hakan ba?.
Hawaye yake ta zubowa amma bai iya ya furta komai ba yana jin muryar Hajiya Kareema nata 'kiran sunan sa" Alhaji 'karami!..Alhaji 'karami!!.." amma sam ba zai iya amsa mata ba kamar yadda ya kasa motsa koda 'dan yatsan sa ne dake jikin sa.
Har a lokacin kuma bai ji muryar Alhaji Mamman yace komai ba yayin da shi kuma ta 6angaren sa ido kawai yake iya rolling amma haushin ganin wan sa tsaye akan sa sai ya hanashi sake bu'de idanun illah hawaye da yake fitarwa.
Ganin haka ya sanya Hajiya Kareema a rikice ta mi'ke tana fa'din " Alhaji akai shi asbiti mana ga dukkan alamu fa yana jin jiki..."
Shiru bai kulata ba saboda damuwar dake cikin ransa ta isheshi, imaging yanda zakaji idan an kama ka da hannu dumu-dumu bisa cin amana, amanar ma ta jinin ka, 'kanin ka, mabiyin ka da kuka fito ciki 'daya, bayan ko Allah ya san irin 'dawainiyar da yake yi maka amma duk da haka ka ci amanar sa kuma ya kama ka...ya zaka ji please?...kun san ba sau'ki.."
Wannan dalilin ne ya sanya shi komai ya tsaya masa cak ya kasa aiwatar da komai a 'adakin hatta maganar da Hajiya Kareema tayi ma bai ji ta ba hakan yasa bata samu amsa daga gare shi ba.
Ganin hakan ya sanya ta jijjiga shi da 'karfi tana sake maimaita abinda ta fa'di domin tunanin ta ko duk ya ru'de ne saboda ganin 'kanin sa kwance babu lafiya.
Jijjiga shin ke da wuya kuwa take sai ya dawo hayyacin sa, kallo 'daya yai mata sai ya 'dauke idanun sa daga kanta, kowa ma yanzu kunyar sa yake ji gani yake tamkar itama ta san abinda ya aikata.
Baya yayi ya zauna bisa kujera yana sakin numfashi mai mugun numi...batare da ya furta komai agare ta ba.
Da fahimci kamar baya hayyacin sa sai tayi hanzarin barin 'dakin da gudu Hajiya Kareema tayi waje ta 'kira driver mai gadi da masu aikin ta suka cicci6e shi suka kai mota, sannan ta tafi ta zaro mayafin ta suka wuce asbiti da shi while Alhaji Mamman na nan inda yake bai ko motsa ba, kallo 'daya zaka yi masa ka fahimci ba'a hayyacin sa yake ba wanda in baka sani ba dagaske zakayi zaton ko tashin jikin 'kanin nasa ne ya sanya shi hakan...sai dai shi ka'dai ya san girman kunya da takaicin da yake ciki a wancan lokacin.
Sai da ya tabbatar sun bar gidan gaba 'daya kafin ya samu ya sawa ransa 'kwarin gwiwa ya sake 'dauko wayar sa a inda ta fa'di, harha'dawa yayi wannan karan sai da ya 'dan le'ka gudun kar wani ya sake jin sa, duk da kuwa yasan cewa kishiyar Hajiya Kareema bata gari a lokacin amma hakan bai hana shi tunanin itama kar tazo ta jishi ba abinku da marar gaskiya.
'Kira yayi ya bada umarnin akai Husnah 'kofar gidan mahaifin ta a sau'ke ta nan kawai suyi tafiyar su yace daga baya zamu ha'du mu kammala deal 'din.
Hakan kuwa akayi, domin mahaifiyar Husnah na nan zaune tayi tagumi tana jiran isowar 'yar ta da yake tasan mahaifin ta ya fita da ku'din amsar tata(ransom), tare suke zaune da wasu 'yan taya ta jaje 'kalilan daga dangi sai da wasu makwabtan ta mafi kusa.
Kamar daga sama ta fara jiyo tashin kukan Husnah yana tunkaro ta ai kuwa da gudu ta tashi ta fita itama tana kukan ta rungume ta.
Sun 'dauki tsawon lokaci suna a haka tana ta godewa mahallici a fili da zuci...sai da ta 'karashi murnar ta saura na tayata kafin ta tambayi Husnah ina mahaifin nata kuma ya tsaya ganin har a lokacin bai shigo ba kuma bata ga motar sa ba a harabar gidan.
Husnah ce tace itama bata ganshi ba...tace mutanen sune suka kawo ta har gida.
Sauran dake tare da Mummyn Husnah wasu salati suka sanya da mamaki suke fa'din" Har gida suka kawo ki da kasu..tashin hankali?"
Mummyn Husnah kam batayi mamaki ba da jin cewa sun san har gidan su damuwar ta mai gidanta ne kawai.
Amma menene abin da zai sa ta dami kanta dan sun har gidan su, tunda kam har suka iya sace ta a makaranta ai zuwa har gidan mahaifin ta ma ba zai gagare su ba...duk kuwa da tasan cewa yanda suka yi abin ba abu ne mai 'daure kai ba.
Drivern da yake 'dauko Husnah aka tsare da bindiga ya jawo su zuwa makarantar cikin motar da yake kaiwa da 'dauko ta daga scool 'din, bayan an tashi su Husnah tazo ta shiga sai suka 'kara sashi ya ja motar suka yi gaba, Husnah har na gaida su ganin ba'ki har mutun biyu cikin motar duk kuwa da cewa fuskokin su sanye suke da ba'ka'ken face mask, basu amsa gaisuwar tata ba ma dan hakan sai ta kalli drivern ta tambaye shi su wanene...shima 'din bai kulata ba cuz shi ka'dai ya san halin da yake ciki.
Dan haka itama ganin babu mai niyyarf magana cikin su ya sanya ta ja bakin ta tayi shiru, yayin da driver yayi tsuru yana cigaba da driving ji yake kamar yayi ta tsala ihu har aka musu 'dauki amma ina no way...cuz gefen cikin sa bindiga ne hakan yasa ya cigaba da jan motar suka yi nisa suka zo inda babu mutane sosai sannan yaga wata ba'kar mota mai ba'kin tinted glass ta sha gaban su, dole tasa yaja yayi parking.
Yana tsaya yaga sun bu'de sun fita tare da dakawa Husnah tsawar ta fito a firgice ta fita 'dayan ya tisa 'keyar ta zuwa 'dayan motar yayin da 'dayan ya tsaya ya bugawa driver gindin bindiga akan sa dan kar ma yayi tunanin binsu abaya, take kuwa ya kifa kanshi bisa sitiyari ya suma.
Tun daga lokacin da suka sa ta shiga motar Husnah bata 'kara sanin kanta ba bata 'kara sanin komai ba sai tsintan kanta tayi a wani gida da bata san ina ne ba..amma basu ta6a lafiyar ko 'dan yatsan ta ba.
Sai bayan wasu mintina sannan drivet ya dawo hayyacin sa bayan har dan taru akansa ganin kansa da 'dan jini-jini.
A gigice yayi musu takaitaccen bayani sannan ya ja motar yana zubda hawaye ya koma gida ya sanar da iyayen Husnah abinda ya faru...Alhaji Mamman ne ya fara 'dora zargin sa kan Nasiru driver har yaza aka kama shi aka kulle da fa'din wai duk munafurci ne, tun ranar ake gana masa azaba wai adole sai ya amsa cewa shi ya sace Husnah amma ya kasa amsawa saboda yasan ba shi bane...'yan sandan da kansu sai da ya fara basu tausayi suka zuba masa idanu kawai duk ya fita hayyacin sa yayi zuru-zuru da shi amma babu wanda zai iya fahimtar sa sai Allahn sa.
Kuma wai duk akan dukiya da Allah ne ke bada ita..."
Zuciyar sa nawi yake jinta ga numfashin sa take ya sar'ke sa yake fita da 'kyar, banda hawaye babu abinda yake iya yi a wannan halin.
Cikin ransa sa yake jin kamar ya tashi yayi ta jibgan yayan nasa har sai ya illata shi saboda cin amanar da yayi masa, ya nuna masa dukiya tafi masa komai a rayuwar nan ciki kuwa harda zumuncin da Allah ne ya ha'da tsakanin su yayo su daga tsatso 'daya, to laifi ne dan Allah ya fifita 'dan uwanka akan ka? Laifi ne dan Allah ya bawa 'dan uwanka dukiya kai bai baka ka? Shin kasan naka kyautar da ya ajiye maka?
'Kilan duk zafin neman ka ba zai ta6a baka dukiyar ba saboda babu ita cikin 'kaddarorin rayuwar ka ta duniya to meyasa zaka takurawa kanka?
Idan kayi ha'kuri ma kabi Allah kabi manzon sa kayi tawakkali babu mamaki ka dace da samun taka dukiyar acan matabbata tana jiran ka, inda ko wani abu zakayi da shi ba zai ta6a 'karewa ba sannan Allah ba zai ta6a gajiya da baka ba, haka nan kuma ba zai ta6a raba ka da aljannar sa ba..to menene yafi wannan fisabilillahi..?"
( ALLAH KASA MU DACE DA NI'IMAR KA DUNIYA DA LAHIRA)
" Amma wannan wace iriyar rayuwa ce, ashe mutun ba zai iya ri'ke 'kaddarar da Allah ya 'dora masa ba sai ya nuna nasa ikon ta hanyar da be dace da karantarwar musulunci ba, me yasa muke zalunci muke dagewa da cewa sai mun yi arzi'ki ko ta halin 'ka'ka bacin a littafin 'kaddarar mu Allah bai tsara hakan ba?.
Hawaye yake ta zubowa amma bai iya ya furta komai ba yana jin muryar Hajiya Kareema nata 'kiran sunan sa" Alhaji 'karami!..Alhaji 'karami!!.." amma sam ba zai iya amsa mata ba kamar yadda ya kasa motsa koda 'dan yatsan sa ne dake jikin sa.
Har a lokacin kuma bai ji muryar Alhaji Mamman yace komai ba yayin da shi kuma ta 6angaren sa ido kawai yake iya rolling amma haushin ganin wan sa tsaye akan sa sai ya hanashi sake bu'de idanun illah hawaye da yake fitarwa.
Ganin haka ya sanya Hajiya Kareema a rikice ta mi'ke tana fa'din " Alhaji akai shi asbiti mana ga dukkan alamu fa yana jin jiki..."
Shiru bai kulata ba saboda damuwar dake cikin ransa ta isheshi, imaging yanda zakaji idan an kama ka da hannu dumu-dumu bisa cin amana, amanar ma ta jinin ka, 'kanin ka, mabiyin ka da kuka fito ciki 'daya, bayan ko Allah ya san irin 'dawainiyar da yake yi maka amma duk da haka ka ci amanar sa kuma ya kama ka...ya zaka ji please?...kun san ba sau'ki.."
Wannan dalilin ne ya sanya shi komai ya tsaya masa cak ya kasa aiwatar da komai a 'adakin hatta maganar da Hajiya Kareema tayi ma bai ji ta ba hakan yasa bata samu amsa daga gare shi ba.
Ganin hakan ya sanya ta jijjiga shi da 'karfi tana sake maimaita abinda ta fa'di domin tunanin ta ko duk ya ru'de ne saboda ganin 'kanin sa kwance babu lafiya.
Jijjiga shin ke da wuya kuwa take sai ya dawo hayyacin sa, kallo 'daya yai mata sai ya 'dauke idanun sa daga kanta, kowa ma yanzu kunyar sa yake ji gani yake tamkar itama ta san abinda ya aikata.
Baya yayi ya zauna bisa kujera yana sakin numfashi mai mugun numi...batare da ya furta komai agare ta ba.
Da fahimci kamar baya hayyacin sa sai tayi hanzarin barin 'dakin da gudu Hajiya Kareema tayi waje ta 'kira driver mai gadi da masu aikin ta suka cicci6e shi suka kai mota, sannan ta tafi ta zaro mayafin ta suka wuce asbiti da shi while Alhaji Mamman na nan inda yake bai ko motsa ba, kallo 'daya zaka yi masa ka fahimci ba'a hayyacin sa yake ba wanda in baka sani ba dagaske zakayi zaton ko tashin jikin 'kanin nasa ne ya sanya shi hakan...sai dai shi ka'dai ya san girman kunya da takaicin da yake ciki a wancan lokacin.
Sai da ya tabbatar sun bar gidan gaba 'daya kafin ya samu ya sawa ransa 'kwarin gwiwa ya sake 'dauko wayar sa a inda ta fa'di, harha'dawa yayi wannan karan sai da ya 'dan le'ka gudun kar wani ya sake jin sa, duk da kuwa yasan cewa kishiyar Hajiya Kareema bata gari a lokacin amma hakan bai hana shi tunanin itama kar tazo ta jishi ba abinku da marar gaskiya.
'Kira yayi ya bada umarnin akai Husnah 'kofar gidan mahaifin ta a sau'ke ta nan kawai suyi tafiyar su yace daga baya zamu ha'du mu kammala deal 'din.
Hakan kuwa akayi, domin mahaifiyar Husnah na nan zaune tayi tagumi tana jiran isowar 'yar ta da yake tasan mahaifin ta ya fita da ku'din amsar tata(ransom), tare suke zaune da wasu 'yan taya ta jaje 'kalilan daga dangi sai da wasu makwabtan ta mafi kusa.
Kamar daga sama ta fara jiyo tashin kukan Husnah yana tunkaro ta ai kuwa da gudu ta tashi ta fita itama tana kukan ta rungume ta.
Sun 'dauki tsawon lokaci suna a haka tana ta godewa mahallici a fili da zuci...sai da ta 'karashi murnar ta saura na tayata kafin ta tambayi Husnah ina mahaifin nata kuma ya tsaya ganin har a lokacin bai shigo ba kuma bata ga motar sa ba a harabar gidan.
Husnah ce tace itama bata ganshi ba...tace mutanen sune suka kawo ta har gida.
Sauran dake tare da Mummyn Husnah wasu salati suka sanya da mamaki suke fa'din" Har gida suka kawo ki da kasu..tashin hankali?"
Mummyn Husnah kam batayi mamaki ba da jin cewa sun san har gidan su damuwar ta mai gidanta ne kawai.
Amma menene abin da zai sa ta dami kanta dan sun har gidan su, tunda kam har suka iya sace ta a makaranta ai zuwa har gidan mahaifin ta ma ba zai gagare su ba...duk kuwa da tasan cewa yanda suka yi abin ba abu ne mai 'daure kai ba.
Drivern da yake 'dauko Husnah aka tsare da bindiga ya jawo su zuwa makarantar cikin motar da yake kaiwa da 'dauko ta daga scool 'din, bayan an tashi su Husnah tazo ta shiga sai suka 'kara sashi ya ja motar suka yi gaba, Husnah har na gaida su ganin ba'ki har mutun biyu cikin motar duk kuwa da cewa fuskokin su sanye suke da ba'ka'ken face mask, basu amsa gaisuwar tata ba ma dan hakan sai ta kalli drivern ta tambaye shi su wanene...shima 'din bai kulata ba cuz shi ka'dai ya san halin da yake ciki.
Dan haka itama ganin babu mai niyyarf magana cikin su ya sanya ta ja bakin ta tayi shiru, yayin da driver yayi tsuru yana cigaba da driving ji yake kamar yayi ta tsala ihu har aka musu 'dauki amma ina no way...cuz gefen cikin sa bindiga ne hakan yasa ya cigaba da jan motar suka yi nisa suka zo inda babu mutane sosai sannan yaga wata ba'kar mota mai ba'kin tinted glass ta sha gaban su, dole tasa yaja yayi parking.
Yana tsaya yaga sun bu'de sun fita tare da dakawa Husnah tsawar ta fito a firgice ta fita 'dayan ya tisa 'keyar ta zuwa 'dayan motar yayin da 'dayan ya tsaya ya bugawa driver gindin bindiga akan sa dan kar ma yayi tunanin binsu abaya, take kuwa ya kifa kanshi bisa sitiyari ya suma.
Tun daga lokacin da suka sa ta shiga motar Husnah bata 'kara sanin kanta ba bata 'kara sanin komai ba sai tsintan kanta tayi a wani gida da bata san ina ne ba..amma basu ta6a lafiyar ko 'dan yatsan ta ba.
Sai bayan wasu mintina sannan drivet ya dawo hayyacin sa bayan har dan taru akansa ganin kansa da 'dan jini-jini.
A gigice yayi musu takaitaccen bayani sannan ya ja motar yana zubda hawaye ya koma gida ya sanar da iyayen Husnah abinda ya faru...Alhaji Mamman ne ya fara 'dora zargin sa kan Nasiru driver har yaza aka kama shi aka kulle da fa'din wai duk munafurci ne, tun ranar ake gana masa azaba wai adole sai ya amsa cewa shi ya sace Husnah amma ya kasa amsawa saboda yasan ba shi bane...'yan sandan da kansu sai da ya fara basu tausayi suka zuba masa idanu kawai duk ya fita hayyacin sa yayi zuru-zuru da shi amma babu wanda zai iya fahimtar sa sai Allahn sa.