Sashe 118
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kaf Mu'een ya san da zuwan Hisham shiyasa ma ya share ta..cuz barazana kawai yai mata dan tana bashi ha'din kai idan ya bu'kaci ganin ta bawai dan yana da niyyar tona ta dagaske ba.
Ko zuwan Hisham daya ga halin da take ciki ma hankalin sa ta shi yayi sosai wanda yayi-yayi ta sanar da shi damuwar ta amma ta'kiya sai dai tace ita garin ne kawai ya ishe ta da kuma zaman ka'daici.
Al'kawari yai mata akan zai sa abincika mata yarinya da zata na taya ta zama da kuma wasu ayyukan...bata 'ki ba ta amince cuz ita kanta zata so hakan ko babu komai zasu zauna suyi hira zata rage mata tunani.
Sati biyu cif da zuwan ta gidan sa amma basu sake ha'duwa da shi ba, har ta 'dan fara sakin ranta kwatsam ranar wata talata sai ta ga text 'din sa cikin wayar ta.
" _Ina jiran ki by 4pm_ ".
Innalillahi ta ringa maimaitawa sannan da rawar jiki ta tura masa " _Ina da lectures_ ".
Sai yacturo mata reply da " _'karya kike yi...ni dai ina jiran ki_ ".
Tun daga gidan tan ta fara share hawaye na ba'kin ciki, haka tana ji tana gani ta shirya ta fita, ni'kab ta sanya ta rufe fuskar ta dashi ita ka'dai tasan ciwon da wannan lamari take yi mata...ganin da auren ta amma Mu'een na so ya lalata mata shi ya na janta izuwa ga mummunar halakar da bazata 6ulle musu ba.
A parlourn sa ta same shi yana kishingi'de kamar ba shi ba...da ganin ta sai ya fara murmushin mugunta...kai ta kawar gefe sannan tace da shi" Kai baka tsoron Allah ko Mu'een?"
Yace " Idan koyawa mutun akeyi sai ki koya min tunda ke 'din na lura gwana ce ta wannan fannin".
Yanda yayi maganar da izza ya sanya ta dole ta sau'kar da muryar ta cuz ta fahimci shi 'din yayi nisa sosai.
Da sanyin murya tace" Nifa indai akan batun yafiya ne wallahi na yafe maka har abada dan Allah ka barni in zauna da mijina lafiya"
Ido ya tsura mata kawai yana kallon ta..wato auren bazata da akayi matan yafiye mata shi da suka da'de suna tare.
Baki ya ta6e yana shafa cikin sa yace" Ni dai yanzu yunwa nake ji..sama min wani abu please ".
Comment
Vote
Share
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
_*Daga marubuciyar Littafin CAPTAIN ABBAS*_
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *57*
Bata ce da shi 'kala ba kamar zatayi kuka ta juya ta nufi kitchen 'din sa dake gidan, sharp-sharp tayi masa jallop na cous-cous da yaji attaruhu sai 'kamshi ke tashi...a hakan ma bata samu vegetables a fridge 'din sa ba shiyasa tayi masa a hakan.
Gaban sa ta kai abincin ta ajiye, har a lokacin kuwa sanye take da hijab 'din ta bata yi gigin cire shi ba.
Tana ajiyewa ya tashi ya mi'ke tsaye da kansa ya 'dauko ruwan gora da cup sannan ya dawo ya zauna ko inda take bai sake kalla ba.
Bata zauna ba haka shima bai ce da ita ta zauna ba, tana tsaye har ya 'kare cin abincin ya kora ruwa...'dayan plate 'din ya 'daga yana rufe guntun abincin da shi yace " Zaki iya tafiya".
Wani sanyin da'di da Husnah ta ji ya sau'ko mata har sai da yasa ta saki ajiyan numfashi a fili.
Da sauri ta nufi hanyar fita dan ma kar yace ya fasa shiyasa bata wani 6ata lokaci ba...sai hamdala take da abun ya tsaya iya girki duk da hakan 'din ma tasan ba dai-dai bane amma ya zatayi...abin is complicated to her bata san hanyar 6ullewa ba tako ina ba sau'ki.
Haka ta cigaba da rayuwa a kullun Allah take mi'kawa kukan ta akan ya yi mata katanga da sharrin Mu'een...duk da tana tsananin son shi har yanzun amma darajar auren ta yafiye mata komai.
Cikin sa'a bai kuma neman ta ba har aka 'kara cin wasu kwanaki, wanda zuwa lokacin har an kawo mata yarinya mai tayata zaman 'yar matashiya mai suna Dija, yarinyar nada nutsuwa kuma tana 'debe mata kewa sosai, ga ta da aiki bata san jiki, ga girmama ta da take yi tamkar 'kanwar ta..hakan ne yasa hankalin ta ya kwanta yanzu sosai.
*****
A can Shuwarin kuwa Ammi sosai take bani kulawa, tana jana a jiki da maganganu inda har take shan cikina cikin dubara dan taji ko ina kula wasu samari awaje, ban ma san manufar ta ba amma da yake ba kowa 'din nake kulawa ba shiyasa ban 6oye mata ba.
Sosai yanzu ta ri'ke min wuta da shiga kitchen kula da tsafta ta duk da dama can ina da ita amma yanzu Ammi komai na sake yimin gyara take yi akan sa ni kam duk ban ta6a kawo komai cikin raina ba.
Ko jiya ma da nace zanje in dubo Ma'u dan bata lafiya Ammi hana ni zuwa tayi tace in bari ba yanzu ba bata son in cika yawo sosai...tace kawai inyi mata addu'ah.
*****
'Bangaren Ma'u kuwa tun cikar sati uku da ha'duwar su da Yah Deen abubuwa suka fara canza mata, ga damuwar yaudaran da yayi mata ga kuma wasu 'yan canze-canze da take jin jikin ta ciki.
Sai tana jin 'kananun zazza6i da ke tashi mata lokaci zuwa lokaci.
Babu wanda ya damu da zazza6in nata dayake ba kwantar da ita yayi ba amma kafin sati biyu sai abin ya 'karu ta fara jin bakin ta na tara yawu akai-akai ga kasala da ke yawan damun ta.
Matar Baban ta ce ta fara mitar hakan dan ko 'dan wanke-wanke da take yi mata ma yanzu da 'kyar take yin sa.
Ga wankin kayan ta nan ma duk ta tara su amma takasa wankewa.
Ko a school mun fara jarabawa amma banda Ma'u cuz ko taje makarantar bata iya yin komai shiyasa ma ta daina zuwa.
Wata biyu ba sati 'daya kenan yanzu da ha'duwar su da Yah Deen, abin nata kuwa sai abinda yayi gaba, mahaifin ta da jansa ya 'dauke ta ya kai ta Chemist dan aduba ta tunda jikin nata ya'ki da'di da tunanin typhoid ke damun ta da yake yaga sai 'karewa take yi wuri guda.
Mai Chemist kam ko daya ganta da yanayin ta kawai sai ya bata su paracetamol sannan ya 'debi jini da fitsarin ta yace za'a kai gwaji a cikin Azare.
Ku'din da duk za'a bu'kata ya gaya wa mahaifin ta take kuwa Malam Barau ya ciro ya biya sannan suka koma gida da sunan jibi zai dawo ya kar6i result 'din test 'din nata.
Ranar ne ya kasance ranar 'kunci da damuwar ga mahaifin Ma'u dan tashin farko likita ya fito fili ya bayyana wa MALAM BARAU cewa 'yar sa Asma'u na 'dauke da juna na tsawon wata biyu.
Kusan mutuwar tsaye Malam Barau yayi saboda tashin hankali, gashi ko da yaje gida da labarin ma step mothern Ma'u bata kwantar masa da hankali ba sai ma masifar da ta haushi da shi wai maganin su kenan ai tunda yace sai tayi makarantar boko ai sakamakon su kenan.
Ma'u kuwa kamar ranta zai fita haka taji...wai ita ce ke 'dauke da ciki ajikin ta..tayi kuka fili da zuci.
Duk ta rame tayi fayau da ita..saboda ko abinci ma ba iya ci take yi ba da taci yake dawowa.
Duk abin nan dake faruwa Ammi bata bar ni naje dubo Ma'u ba...har ma zuwa yanzun na gaji da tambayar na ha'kura.
Mahaifin Ma'u bai iya yayi magana da Ma'u ba saboda takaici, matar sa ce ma cikin 'kananun maganganunta har ta tuna masa batun sanin mamallakin cikin wanda shima sai a lokacin hakan yazo ransa.
Tun ranar da ya shigo da result na test 'din abinda kawai ya iya ce da Ma'u shine" Baki kyauta min ba Ma'u".
Cikin tsananin rashin walwala ya fa'di mata hakan tare da wulla mata takardar gwajin har yau bai 'kara ce da ita komai ba, ita kam ma nawin ahalin gidan ya hanata sakat bata ko iya fitowa ta zauna tare da su..ga shi shirun da mahaifin ta yayi matan sai ya 'kara tada mata hankali, abubuwan duk sun taru sun yi mata yawa.
Sai yanzun ne Malan Barau ya iya tashi ya shiga har cikin 'dakin da Ma'u take inda ya same ta du'kun'kune cikin hijabi kamar mai bacci...jin motsin shigowar shi ne ya sa ta yun'kura ta tashi ta zauna amma sam ta kasa ha'da idanu da shi.. yana daga tsaye ta gaishe shi kanta 'kasa inda ya amsa mata babu yabo ba fallasa shima 'din ji yake kamar ya zubar da hawaye idan ya ganta, Ma'u banda hawaye babu abinda ke motsi a jikin ta su ka'dai ke gudu wani na bin wani.
" Ban ta6a tunanin zaki bani kunya ba Ma'u, nayi 'ko'kari sosai wurin ganin na bawa rayuwar ki kariya bansani ba ashe shirme na nake yi..."
Cikin kuka tayi saurin taran sa da fa'din" Baba dan Allah kayi ha'kuri ka yafe min wallahi ba hali na bane..."
Yanda tayi maganar da yanda take kuka ya sashi juyawa kawai ya bar 'dakin saboda tausayin ta da ya sake tsarga masa a zuci, abin ma da ya kawo shi bai iya ya tambaye ta ba.
Yana fita Innar su ta tare shi da fa'din" Waye mamallakin cikin ta gaya maka?"
" Bansani ba nima".
Ya bata amsa atakaice.
Ko zuwan Hisham daya ga halin da take ciki ma hankalin sa ta shi yayi sosai wanda yayi-yayi ta sanar da shi damuwar ta amma ta'kiya sai dai tace ita garin ne kawai ya ishe ta da kuma zaman ka'daici.
Al'kawari yai mata akan zai sa abincika mata yarinya da zata na taya ta zama da kuma wasu ayyukan...bata 'ki ba ta amince cuz ita kanta zata so hakan ko babu komai zasu zauna suyi hira zata rage mata tunani.
Sati biyu cif da zuwan ta gidan sa amma basu sake ha'duwa da shi ba, har ta 'dan fara sakin ranta kwatsam ranar wata talata sai ta ga text 'din sa cikin wayar ta.
" _Ina jiran ki by 4pm_ ".
Innalillahi ta ringa maimaitawa sannan da rawar jiki ta tura masa " _Ina da lectures_ ".
Sai yacturo mata reply da " _'karya kike yi...ni dai ina jiran ki_ ".
Tun daga gidan tan ta fara share hawaye na ba'kin ciki, haka tana ji tana gani ta shirya ta fita, ni'kab ta sanya ta rufe fuskar ta dashi ita ka'dai tasan ciwon da wannan lamari take yi mata...ganin da auren ta amma Mu'een na so ya lalata mata shi ya na janta izuwa ga mummunar halakar da bazata 6ulle musu ba.
A parlourn sa ta same shi yana kishingi'de kamar ba shi ba...da ganin ta sai ya fara murmushin mugunta...kai ta kawar gefe sannan tace da shi" Kai baka tsoron Allah ko Mu'een?"
Yace " Idan koyawa mutun akeyi sai ki koya min tunda ke 'din na lura gwana ce ta wannan fannin".
Yanda yayi maganar da izza ya sanya ta dole ta sau'kar da muryar ta cuz ta fahimci shi 'din yayi nisa sosai.
Da sanyin murya tace" Nifa indai akan batun yafiya ne wallahi na yafe maka har abada dan Allah ka barni in zauna da mijina lafiya"
Ido ya tsura mata kawai yana kallon ta..wato auren bazata da akayi matan yafiye mata shi da suka da'de suna tare.
Baki ya ta6e yana shafa cikin sa yace" Ni dai yanzu yunwa nake ji..sama min wani abu please ".
Comment
Vote
Share
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
_*Daga marubuciyar Littafin CAPTAIN ABBAS*_
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *57*
Bata ce da shi 'kala ba kamar zatayi kuka ta juya ta nufi kitchen 'din sa dake gidan, sharp-sharp tayi masa jallop na cous-cous da yaji attaruhu sai 'kamshi ke tashi...a hakan ma bata samu vegetables a fridge 'din sa ba shiyasa tayi masa a hakan.
Gaban sa ta kai abincin ta ajiye, har a lokacin kuwa sanye take da hijab 'din ta bata yi gigin cire shi ba.
Tana ajiyewa ya tashi ya mi'ke tsaye da kansa ya 'dauko ruwan gora da cup sannan ya dawo ya zauna ko inda take bai sake kalla ba.
Bata zauna ba haka shima bai ce da ita ta zauna ba, tana tsaye har ya 'kare cin abincin ya kora ruwa...'dayan plate 'din ya 'daga yana rufe guntun abincin da shi yace " Zaki iya tafiya".
Wani sanyin da'di da Husnah ta ji ya sau'ko mata har sai da yasa ta saki ajiyan numfashi a fili.
Da sauri ta nufi hanyar fita dan ma kar yace ya fasa shiyasa bata wani 6ata lokaci ba...sai hamdala take da abun ya tsaya iya girki duk da hakan 'din ma tasan ba dai-dai bane amma ya zatayi...abin is complicated to her bata san hanyar 6ullewa ba tako ina ba sau'ki.
Haka ta cigaba da rayuwa a kullun Allah take mi'kawa kukan ta akan ya yi mata katanga da sharrin Mu'een...duk da tana tsananin son shi har yanzun amma darajar auren ta yafiye mata komai.
Cikin sa'a bai kuma neman ta ba har aka 'kara cin wasu kwanaki, wanda zuwa lokacin har an kawo mata yarinya mai tayata zaman 'yar matashiya mai suna Dija, yarinyar nada nutsuwa kuma tana 'debe mata kewa sosai, ga ta da aiki bata san jiki, ga girmama ta da take yi tamkar 'kanwar ta..hakan ne yasa hankalin ta ya kwanta yanzu sosai.
*****
A can Shuwarin kuwa Ammi sosai take bani kulawa, tana jana a jiki da maganganu inda har take shan cikina cikin dubara dan taji ko ina kula wasu samari awaje, ban ma san manufar ta ba amma da yake ba kowa 'din nake kulawa ba shiyasa ban 6oye mata ba.
Sosai yanzu ta ri'ke min wuta da shiga kitchen kula da tsafta ta duk da dama can ina da ita amma yanzu Ammi komai na sake yimin gyara take yi akan sa ni kam duk ban ta6a kawo komai cikin raina ba.
Ko jiya ma da nace zanje in dubo Ma'u dan bata lafiya Ammi hana ni zuwa tayi tace in bari ba yanzu ba bata son in cika yawo sosai...tace kawai inyi mata addu'ah.
*****
'Bangaren Ma'u kuwa tun cikar sati uku da ha'duwar su da Yah Deen abubuwa suka fara canza mata, ga damuwar yaudaran da yayi mata ga kuma wasu 'yan canze-canze da take jin jikin ta ciki.
Sai tana jin 'kananun zazza6i da ke tashi mata lokaci zuwa lokaci.
Babu wanda ya damu da zazza6in nata dayake ba kwantar da ita yayi ba amma kafin sati biyu sai abin ya 'karu ta fara jin bakin ta na tara yawu akai-akai ga kasala da ke yawan damun ta.
Matar Baban ta ce ta fara mitar hakan dan ko 'dan wanke-wanke da take yi mata ma yanzu da 'kyar take yin sa.
Ga wankin kayan ta nan ma duk ta tara su amma takasa wankewa.
Ko a school mun fara jarabawa amma banda Ma'u cuz ko taje makarantar bata iya yin komai shiyasa ma ta daina zuwa.
Wata biyu ba sati 'daya kenan yanzu da ha'duwar su da Yah Deen, abin nata kuwa sai abinda yayi gaba, mahaifin ta da jansa ya 'dauke ta ya kai ta Chemist dan aduba ta tunda jikin nata ya'ki da'di da tunanin typhoid ke damun ta da yake yaga sai 'karewa take yi wuri guda.
Mai Chemist kam ko daya ganta da yanayin ta kawai sai ya bata su paracetamol sannan ya 'debi jini da fitsarin ta yace za'a kai gwaji a cikin Azare.
Ku'din da duk za'a bu'kata ya gaya wa mahaifin ta take kuwa Malam Barau ya ciro ya biya sannan suka koma gida da sunan jibi zai dawo ya kar6i result 'din test 'din nata.
Ranar ne ya kasance ranar 'kunci da damuwar ga mahaifin Ma'u dan tashin farko likita ya fito fili ya bayyana wa MALAM BARAU cewa 'yar sa Asma'u na 'dauke da juna na tsawon wata biyu.
Kusan mutuwar tsaye Malam Barau yayi saboda tashin hankali, gashi ko da yaje gida da labarin ma step mothern Ma'u bata kwantar masa da hankali ba sai ma masifar da ta haushi da shi wai maganin su kenan ai tunda yace sai tayi makarantar boko ai sakamakon su kenan.
Ma'u kuwa kamar ranta zai fita haka taji...wai ita ce ke 'dauke da ciki ajikin ta..tayi kuka fili da zuci.
Duk ta rame tayi fayau da ita..saboda ko abinci ma ba iya ci take yi ba da taci yake dawowa.
Duk abin nan dake faruwa Ammi bata bar ni naje dubo Ma'u ba...har ma zuwa yanzun na gaji da tambayar na ha'kura.
Mahaifin Ma'u bai iya yayi magana da Ma'u ba saboda takaici, matar sa ce ma cikin 'kananun maganganunta har ta tuna masa batun sanin mamallakin cikin wanda shima sai a lokacin hakan yazo ransa.
Tun ranar da ya shigo da result na test 'din abinda kawai ya iya ce da Ma'u shine" Baki kyauta min ba Ma'u".
Cikin tsananin rashin walwala ya fa'di mata hakan tare da wulla mata takardar gwajin har yau bai 'kara ce da ita komai ba, ita kam ma nawin ahalin gidan ya hanata sakat bata ko iya fitowa ta zauna tare da su..ga shi shirun da mahaifin ta yayi matan sai ya 'kara tada mata hankali, abubuwan duk sun taru sun yi mata yawa.
Sai yanzun ne Malan Barau ya iya tashi ya shiga har cikin 'dakin da Ma'u take inda ya same ta du'kun'kune cikin hijabi kamar mai bacci...jin motsin shigowar shi ne ya sa ta yun'kura ta tashi ta zauna amma sam ta kasa ha'da idanu da shi.. yana daga tsaye ta gaishe shi kanta 'kasa inda ya amsa mata babu yabo ba fallasa shima 'din ji yake kamar ya zubar da hawaye idan ya ganta, Ma'u banda hawaye babu abinda ke motsi a jikin ta su ka'dai ke gudu wani na bin wani.
" Ban ta6a tunanin zaki bani kunya ba Ma'u, nayi 'ko'kari sosai wurin ganin na bawa rayuwar ki kariya bansani ba ashe shirme na nake yi..."
Cikin kuka tayi saurin taran sa da fa'din" Baba dan Allah kayi ha'kuri ka yafe min wallahi ba hali na bane..."
Yanda tayi maganar da yanda take kuka ya sashi juyawa kawai ya bar 'dakin saboda tausayin ta da ya sake tsarga masa a zuci, abin ma da ya kawo shi bai iya ya tambaye ta ba.
Yana fita Innar su ta tare shi da fa'din" Waye mamallakin cikin ta gaya maka?"
" Bansani ba nima".
Ya bata amsa atakaice.