Sashe 77
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ko da naje gida kuwa Ammi fa'da sosai ta fara yimin inda tace na da'de daga raka ta kuma sai inje in zauna, ni banga ita bata da'de agidan mun ba shine ni zan bita har gidan su, kenan ta fini wayo tunda jana tazo yi tace ai da tasan zan da'de da ba zama ta barni in bita ba..daga 'karshe sai tace idan ina yawo irin haka zata saka Mu'een ya zane ni".
Ammi ta fa'di haka ne saboda ta san ina tsoron sa wai ko idan naji hakan zan kiyaye gaba...bata san cewa tsoron nawa ya zarce misali ba...dan kuwa tunda naji tace zai zane ni nayi narai-narai da idanu ina kallon ta nace " Dan Allah Ammi kiyi ha'kuri..bamu gama sharar bane da wuri fa shiyasa muka da'de..ni dai kar kice masa ya zane ni".
Na 'karasa maganar hawaye na sa'k'ko min.
Da mamaki Ammi tace " Shara kuma ta me kuma a ina?"
Comment
Vote
Share
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
🤞🏻
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *39*
" Ai shine ya sani sharar"!
Wannan karan ina share hawaye na nayi maganar.
" Waye?".
Ammi ta sake tambaya ta tana mai bada dukkan hankalin ta gare ni.
" Yah Deen 'din ?"
Na bata amsa hawaye na na sake gangarowa.
Salati Ammi ke zubawa da jin abinda na fa'di, tana tafa hannuwa tace "
Hudah dagaske shine ya saki shara?"
Da kai na bata amsa alamar " Erh"
Wannan karan Ammi baki ta ri'ke cike da mamaki tace" Allah Buwayi...Ina gidan nan ya akayi har yazo ya aikata hakan batare da na sani ba?".
Ina tura baki nace
" Ai ya da'de da fa'da min kuma yace kar ingaya miki in ba haka kashe ni zaiyi".
Dariya ma maganar tawa ta bata amma yanda Yah Deen ya ninke ta abaibai ya yaudaretan sai ya sa ta jin 6acin rai sosai, " Wato barazana yayi miki da kisa"
Ta fa'di a fili"..hmm lalle!... shiyasa ya daina neman atura masa kowa...munafiki ashe ya san munafurcin da ya 'kulla...zaizo ya same ni ai"
Ni kuwa ina daga tsaye sai goge idanu nake yi kamar zan cire su, a lokacin tsoro biyu ne suka ha'du min, ga na kar Ammi ta sashi ya zane ni ga kuma tunowa da nayi cewa ya hana ni sanar da ita wanda hakan ya sanya hawayen nawa kasa tsayuwa.
Zama tayi ta gyara tare da janyo hannu na zuwa gaban ta kusa da ita, kafin ta furya komai na 'dago jajayen idanu na sauke au kan fuskar ta nace " Ammi kar ki ce masa na gaya miki dan Allah cewa yayi kashe ni zai yi"
Na 'karasa cikin kuka.
...Cikin lallami da kwantar da murya tace
" Haba uwata ina nan din kike tunanin zai kashe min ke kuma in barshi, 'kyale ni da shi zai zo ya same ni ne...kinji?"
Kaina na 'dage alamar Erh naji.
" Yanzu gaya min me ya faru duk karki 6oye min kinji ".
....Daki-daki na hau bawa Ammi duk amsar tambayar da ta min.
Takaici ne sosai ya kama Ammi jin yanda tsawon lokaci yake wasa da hankalin ta kamar 'kwallo...ya muzanta ta ya nuna mata bata isa ba, sannan ya girgiza mata igiyar al'kawarin da ta 'dauka kafin ta kar6o Noorul Hudah da wani irin fuska yake so iyayen na su dube ta ?"
Ran Ammi sosai ya 6aci da shi.
Abinda kawai ta iya 'karfin halin furta min a fili shine" Rabu da shi zai zo ya same ni"!
Ni kam take sai na marairaice fuska tuno irin kashedin da ya zayyana min gashi na warware wa Ammi komai, cikin kuka da marairaita nace " Ammi dan Allah kar kice na gaya miki Allah kashe ni zai yi".
Dai-dai nan Zaidu ya shigo 'dakin yana ta6e baki jin abinda nake fa'dawa Ammi, shi haka yake sam bai damu da damuwar kowa ba har ma sai nake ganin gara kowa ma akaina, domin iya tsawon zama na a gidan bai mun sha'ku da shi ya fara yi min kallon 'yar uwa ba yayin da ni nake jin su tamkar 6angaren jiki na.
Daga can hanyar corridor Saif dake biyo bayan Zaidu yake fa'din " ...Wai Zaid anya kuwa ka tuna siyan wannan...."
Cak maganar tasa ta yanke sakamakon ganin yanda nake rusa kuka...Ammi ya kalla sai yaga itama hankalin ta na kaina.
Take akalar tambayar tasa ta canza daga kan Saif zuwa Ammi inda ya karasa shigowa parlourn da sassarfa yake tambayar.." Lafiya Ammi me ya same ta?"
Ammi bata tanka shi ba kawai ta cigaba da duba na...shi kuma Saif ya 'karaso ya zauna daga gefen Ammi yana min duba a tsanake da son karantar yanayin da nake ciki.
Ammi kuwa 'dan takaitaccen murmushin takaici ta saki gami da kamo hannu na tana share min hawaye tace " Ki kwantar da hankalin ki, ba na gaya miki ba, ai be isa ya kashe ki ba matu'kar ina nan kar ki damu kinji?"
Sai na 'dage kaina sama.
" Yauwa...sannan daga yau ki daina 6oye min abu kinji..koma miye ya faru kar ki 6oye min bana son irin haka ni...ko me ya miki ki zo ki sanar dani, zanyi maganin sa, yanzu wannan da kin gaya min tuntuni ai da hakan ba zai faru ba, da ba zan ta6a bari ya ringa bautar da ke ba balle har su lattin zuwa makaranta, munafukin kuma ya sani amma ya basar...zai zo ya same ni ne...ni ina nan na saki baki ina tunanin ramar girma ce ta kamaki ashe ba haka bane..wani abin ne daban...hmm yaron nan na wasa da ni Allah".
Daga yanda Ammi ke furta maganar ma zaka san cewa ranta a tsananin 6ace yake hakan yasa da mamaki Saif ya 'kara jefa mata tambayar" Ammi wai meke faruwa ne na kasa ganewa".
Sai yanzun Ammi ta 'daga idanu ta kalle shi sai tace da shi " me ke faru kuwa Saif a gidan banda matsalar Yayan ku, fisabilillahi nawa yarinyan take da zai maida abokiyar hamayyar sa? ace tsawon lokaci ina gidan nan ban sani ba ashe kullum sai taje tayi masa bauta acan gidan ko makaranta bata zuwa a lokacin da ya dace, kuma abin haushi ma wai sai yayi mata barazanar kisa idan ta sanar da kowa...ji min hauka fa? Bansan me Mu'een ya 'dauki kansa ba gaskiya".
Ta 'karashe maganar da yaren su tare da watsa hannu.
Ajiyar zuciya Saif ya sau'ke tare da fa'din" Haba!..ai nima wallahi sai da na zargi wani abu tuntuni, Allah Ammi da Hudah fa ba haka take ba, amma kwanan nan naga duk ta canza bata fiye son shiga mutane ba, kuma fa ko makaranta idan nace zan rakata hanya 'kin yadda take yi...ko'ina zata bata son araka ta sam, ashe dan kar aga inda zata je ne shiyasa".
Tsaki Ammi taja tana kallon Saif cikin ido tace" See you, tun farko me yasa baka gaya min hakan ba to?"
Yana shirin sake yin magana ta Ammi ta kwa6e shi da fa'din" Shut up please ya ishe ni..ai kaima harda laifin ka Saif...wancan wawan kan ma nasan koda ya sani he won't tell saboda mugun hali".
Ta 'karashe tmaganar tana nuna Zaidu.
Da haushin ance mai wawa yace " Nima fa Ammi bansani ba".
" Kai ka sani ai.. useless kawai".
Ta fa'di cike da takaici.
Saif kam cikin kwantar da murya yace" Ammi sorry ni dai bansan haka bane Allah da kinsan bazan 6oye miki ba".
Shiru Ammi tayi bata sake tanka shi ba.
Ni kam kuka na na cigaba da yi bayan na kwantar da kaina bisa cinyar Ammi..ban 'kara fa'din komai ba cikin haka har bacci yayi gaba dani.
Ta shi na daga baccin kuwa sai na tashi da zazza6i mai zafi saboda tsoron abinda zai biyo baya tsakanin ni da shi, cuz koka'dan ban yadda cewa Ammi zata iya hana shi ta6a lafiya ta ba.
*****
Tun a ranar ba'a kwana ba Imrana yaje gidan su Ma'u da sunan zance ita kuwa ta 'kara jaddada masa wanda take so da yake tana tare da yarin ta itama shi yasa sam bata damu da bayyana sirrin dake cikin ranta ba, domin dududu shekarun ta sha biyar ne a lokacin.
Mahaifin ta ma daya ga Imrana tare da 'yar sa ai sai hankalin sa ya tashi sosai, ba zato ba tsammani kawai washe gari yasa ta shirya ya tura ta can wurin dangin mahaifiyar ta a Lanzai ko ita kanta Ma'un kuwa bata san dalilin tafiyar tata ba balle wani daban...dan a cewar sa sam be yaba da tarbiyar Imrana ba.
Ana gobe su Saif zasu tafi zazza6i na yayi tsanani sosai....hankalin Ammi kuwa ba 'karamin tashi yayi ba.
Ko lokacin da su Saif zasu wuce ma kuka na dingayi Ammi duk sai ta 'kara rikicewa har suka tafi basu samu natsuwar Ammi ba.
Bayan tafiyar su ne suka sake 'kiran ta awaya lokacin ina bacci.....sai a sannan hankalin su ya kwanta da suka ji tayi musu Addu'ah cikin natsuwa...anan Saif ya sake tambayar ta jiki na ta ce da shi " Alhamdulillahi da sau'ki".
Jin hakan ne ya 'kara kwantar da hankalin Saif har ya saki ransa a makaranta.
Kwana uku ina kwance ban zuwa ko'ina, Alhaji Baba da kansa ya 'kira likita ya dubani ya bani magunguna da Allura, ni kaina wannan karan ban san me yasa banji tsoro ba akayi min har guda biyu, sai dai magungunan kam ban iya na sha ba illah kuka da nake tayi wanda ganin haka yasa Alhaji Baba yace abarni kawai.
'Bangaren Yah Deen kuwa sai da ya kwana biyar cif bai sa ni a idanun sa ba, koma ba dan sharar da nake yi masa ba atleast idan ya ganni ya kanji natsuwa har cikin zuciyar sa, amma sai gashi yanzu ko gidan yazo baya gani na haka ban zuwa can gidan nashi, shine ranar ya ku'duri aniyar tambayar Ammi dalilin daina gani na da yayi.
Ammi ta fa'di haka ne saboda ta san ina tsoron sa wai ko idan naji hakan zan kiyaye gaba...bata san cewa tsoron nawa ya zarce misali ba...dan kuwa tunda naji tace zai zane ni nayi narai-narai da idanu ina kallon ta nace " Dan Allah Ammi kiyi ha'kuri..bamu gama sharar bane da wuri fa shiyasa muka da'de..ni dai kar kice masa ya zane ni".
Na 'karasa maganar hawaye na sa'k'ko min.
Da mamaki Ammi tace " Shara kuma ta me kuma a ina?"
Comment
Vote
Share
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
🤞🏻
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *39*
" Ai shine ya sani sharar"!
Wannan karan ina share hawaye na nayi maganar.
" Waye?".
Ammi ta sake tambaya ta tana mai bada dukkan hankalin ta gare ni.
" Yah Deen 'din ?"
Na bata amsa hawaye na na sake gangarowa.
Salati Ammi ke zubawa da jin abinda na fa'di, tana tafa hannuwa tace "
Hudah dagaske shine ya saki shara?"
Da kai na bata amsa alamar " Erh"
Wannan karan Ammi baki ta ri'ke cike da mamaki tace" Allah Buwayi...Ina gidan nan ya akayi har yazo ya aikata hakan batare da na sani ba?".
Ina tura baki nace
" Ai ya da'de da fa'da min kuma yace kar ingaya miki in ba haka kashe ni zaiyi".
Dariya ma maganar tawa ta bata amma yanda Yah Deen ya ninke ta abaibai ya yaudaretan sai ya sa ta jin 6acin rai sosai, " Wato barazana yayi miki da kisa"
Ta fa'di a fili"..hmm lalle!... shiyasa ya daina neman atura masa kowa...munafiki ashe ya san munafurcin da ya 'kulla...zaizo ya same ni ai"
Ni kuwa ina daga tsaye sai goge idanu nake yi kamar zan cire su, a lokacin tsoro biyu ne suka ha'du min, ga na kar Ammi ta sashi ya zane ni ga kuma tunowa da nayi cewa ya hana ni sanar da ita wanda hakan ya sanya hawayen nawa kasa tsayuwa.
Zama tayi ta gyara tare da janyo hannu na zuwa gaban ta kusa da ita, kafin ta furya komai na 'dago jajayen idanu na sauke au kan fuskar ta nace " Ammi kar ki ce masa na gaya miki dan Allah cewa yayi kashe ni zai yi"
Na 'karasa cikin kuka.
...Cikin lallami da kwantar da murya tace
" Haba uwata ina nan din kike tunanin zai kashe min ke kuma in barshi, 'kyale ni da shi zai zo ya same ni ne...kinji?"
Kaina na 'dage alamar Erh naji.
" Yanzu gaya min me ya faru duk karki 6oye min kinji ".
....Daki-daki na hau bawa Ammi duk amsar tambayar da ta min.
Takaici ne sosai ya kama Ammi jin yanda tsawon lokaci yake wasa da hankalin ta kamar 'kwallo...ya muzanta ta ya nuna mata bata isa ba, sannan ya girgiza mata igiyar al'kawarin da ta 'dauka kafin ta kar6o Noorul Hudah da wani irin fuska yake so iyayen na su dube ta ?"
Ran Ammi sosai ya 6aci da shi.
Abinda kawai ta iya 'karfin halin furta min a fili shine" Rabu da shi zai zo ya same ni"!
Ni kam take sai na marairaice fuska tuno irin kashedin da ya zayyana min gashi na warware wa Ammi komai, cikin kuka da marairaita nace " Ammi dan Allah kar kice na gaya miki Allah kashe ni zai yi".
Dai-dai nan Zaidu ya shigo 'dakin yana ta6e baki jin abinda nake fa'dawa Ammi, shi haka yake sam bai damu da damuwar kowa ba har ma sai nake ganin gara kowa ma akaina, domin iya tsawon zama na a gidan bai mun sha'ku da shi ya fara yi min kallon 'yar uwa ba yayin da ni nake jin su tamkar 6angaren jiki na.
Daga can hanyar corridor Saif dake biyo bayan Zaidu yake fa'din " ...Wai Zaid anya kuwa ka tuna siyan wannan...."
Cak maganar tasa ta yanke sakamakon ganin yanda nake rusa kuka...Ammi ya kalla sai yaga itama hankalin ta na kaina.
Take akalar tambayar tasa ta canza daga kan Saif zuwa Ammi inda ya karasa shigowa parlourn da sassarfa yake tambayar.." Lafiya Ammi me ya same ta?"
Ammi bata tanka shi ba kawai ta cigaba da duba na...shi kuma Saif ya 'karaso ya zauna daga gefen Ammi yana min duba a tsanake da son karantar yanayin da nake ciki.
Ammi kuwa 'dan takaitaccen murmushin takaici ta saki gami da kamo hannu na tana share min hawaye tace " Ki kwantar da hankalin ki, ba na gaya miki ba, ai be isa ya kashe ki ba matu'kar ina nan kar ki damu kinji?"
Sai na 'dage kaina sama.
" Yauwa...sannan daga yau ki daina 6oye min abu kinji..koma miye ya faru kar ki 6oye min bana son irin haka ni...ko me ya miki ki zo ki sanar dani, zanyi maganin sa, yanzu wannan da kin gaya min tuntuni ai da hakan ba zai faru ba, da ba zan ta6a bari ya ringa bautar da ke ba balle har su lattin zuwa makaranta, munafukin kuma ya sani amma ya basar...zai zo ya same ni ne...ni ina nan na saki baki ina tunanin ramar girma ce ta kamaki ashe ba haka bane..wani abin ne daban...hmm yaron nan na wasa da ni Allah".
Daga yanda Ammi ke furta maganar ma zaka san cewa ranta a tsananin 6ace yake hakan yasa da mamaki Saif ya 'kara jefa mata tambayar" Ammi wai meke faruwa ne na kasa ganewa".
Sai yanzun Ammi ta 'daga idanu ta kalle shi sai tace da shi " me ke faru kuwa Saif a gidan banda matsalar Yayan ku, fisabilillahi nawa yarinyan take da zai maida abokiyar hamayyar sa? ace tsawon lokaci ina gidan nan ban sani ba ashe kullum sai taje tayi masa bauta acan gidan ko makaranta bata zuwa a lokacin da ya dace, kuma abin haushi ma wai sai yayi mata barazanar kisa idan ta sanar da kowa...ji min hauka fa? Bansan me Mu'een ya 'dauki kansa ba gaskiya".
Ta 'karashe maganar da yaren su tare da watsa hannu.
Ajiyar zuciya Saif ya sau'ke tare da fa'din" Haba!..ai nima wallahi sai da na zargi wani abu tuntuni, Allah Ammi da Hudah fa ba haka take ba, amma kwanan nan naga duk ta canza bata fiye son shiga mutane ba, kuma fa ko makaranta idan nace zan rakata hanya 'kin yadda take yi...ko'ina zata bata son araka ta sam, ashe dan kar aga inda zata je ne shiyasa".
Tsaki Ammi taja tana kallon Saif cikin ido tace" See you, tun farko me yasa baka gaya min hakan ba to?"
Yana shirin sake yin magana ta Ammi ta kwa6e shi da fa'din" Shut up please ya ishe ni..ai kaima harda laifin ka Saif...wancan wawan kan ma nasan koda ya sani he won't tell saboda mugun hali".
Ta 'karashe tmaganar tana nuna Zaidu.
Da haushin ance mai wawa yace " Nima fa Ammi bansani ba".
" Kai ka sani ai.. useless kawai".
Ta fa'di cike da takaici.
Saif kam cikin kwantar da murya yace" Ammi sorry ni dai bansan haka bane Allah da kinsan bazan 6oye miki ba".
Shiru Ammi tayi bata sake tanka shi ba.
Ni kam kuka na na cigaba da yi bayan na kwantar da kaina bisa cinyar Ammi..ban 'kara fa'din komai ba cikin haka har bacci yayi gaba dani.
Ta shi na daga baccin kuwa sai na tashi da zazza6i mai zafi saboda tsoron abinda zai biyo baya tsakanin ni da shi, cuz koka'dan ban yadda cewa Ammi zata iya hana shi ta6a lafiya ta ba.
*****
Tun a ranar ba'a kwana ba Imrana yaje gidan su Ma'u da sunan zance ita kuwa ta 'kara jaddada masa wanda take so da yake tana tare da yarin ta itama shi yasa sam bata damu da bayyana sirrin dake cikin ranta ba, domin dududu shekarun ta sha biyar ne a lokacin.
Mahaifin ta ma daya ga Imrana tare da 'yar sa ai sai hankalin sa ya tashi sosai, ba zato ba tsammani kawai washe gari yasa ta shirya ya tura ta can wurin dangin mahaifiyar ta a Lanzai ko ita kanta Ma'un kuwa bata san dalilin tafiyar tata ba balle wani daban...dan a cewar sa sam be yaba da tarbiyar Imrana ba.
Ana gobe su Saif zasu tafi zazza6i na yayi tsanani sosai....hankalin Ammi kuwa ba 'karamin tashi yayi ba.
Ko lokacin da su Saif zasu wuce ma kuka na dingayi Ammi duk sai ta 'kara rikicewa har suka tafi basu samu natsuwar Ammi ba.
Bayan tafiyar su ne suka sake 'kiran ta awaya lokacin ina bacci.....sai a sannan hankalin su ya kwanta da suka ji tayi musu Addu'ah cikin natsuwa...anan Saif ya sake tambayar ta jiki na ta ce da shi " Alhamdulillahi da sau'ki".
Jin hakan ne ya 'kara kwantar da hankalin Saif har ya saki ransa a makaranta.
Kwana uku ina kwance ban zuwa ko'ina, Alhaji Baba da kansa ya 'kira likita ya dubani ya bani magunguna da Allura, ni kaina wannan karan ban san me yasa banji tsoro ba akayi min har guda biyu, sai dai magungunan kam ban iya na sha ba illah kuka da nake tayi wanda ganin haka yasa Alhaji Baba yace abarni kawai.
'Bangaren Yah Deen kuwa sai da ya kwana biyar cif bai sa ni a idanun sa ba, koma ba dan sharar da nake yi masa ba atleast idan ya ganni ya kanji natsuwa har cikin zuciyar sa, amma sai gashi yanzu ko gidan yazo baya gani na haka ban zuwa can gidan nashi, shine ranar ya ku'duri aniyar tambayar Ammi dalilin daina gani na da yayi.