Sashe 113
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A harabar gida na ci karo da su Alhaji Baba da yaran sa, wato Yah Deen da abokan sa...ban san me suke tattaunawa ba sai dai ga dukkan alamu shigowar su kenan... na tabbatar da hakan ne lokacin da na kusan isa inda suke naji suna faman mi'ka masa gaisuwa inda yake amsa musu da fara'ar sa hannayen sa duk na cikin babbar rigar sa amma kallo 'daya zaka yi masa ka tabbatar ba shi tare da damuwa...fara'a fal a fuksar sa har kana iya hango hasken ha'koran sa afili.
Da gani na sai ya maida hankalinsa wuri na ina gaida shi ya amsa tare da 'karawa da fa'din" Uwata ina zuwa da sssafe haka?"
" Murmushi nayi sannan na 'daga kai na dubi harabar gidan inda duk rana ta mamaye ko'ina..." Ba sassafe bane fa Alhaji Babba kalli fa yanda rana ma tayi".
Na fa'di ina murmushi tare da nuno wurin.. shima Alhaji sai yayi murmushin..sannan ya sake fa'din unguwa zaki ne?"
Nace" Nace a a zanje in gaida Baban mu ne ".
Sai yace
" Ya kamata kam..dan inajin gobe ma zai koma...amma ki bari ba yanzu ba kinji maza ki koma cikin gida".
" To" kawai nace da shi tare da 'daga kaina na kalli su Yah Deen da ke tsatstsatye wanda da shi na fara ha'da idanu sai naga ya ta6e baki tare da kawar da kansa gefe, bansan me nayi masa ba dan haka sai nima 'dauke kaina daga kallon sa zuwa na gefen sa (Anas) shi kuma sai naga yana min murmushi ban damu ba kawai a jimlance nace da su " Ina kwanan ku?"
Mutun biyu zuwa uku ne daga cikin su suka amsa min wanda cikin sun kuwa ina da tabbacin babu Yah Deen a ciki.
Juyawa nayi na fara tafiya zuwa cikin gida yayin da Alhaji Baba ya nufi hanyar fita tare da 'kiran sunan Ishaq da alamun yana so su ke6e da shi, Ishaq sai ya bi bayan sa su Yah Deen kuwa cikin gidan suma suka 'karaso dan gaida su Ammi...in tafe suna bina abaya amma tsakani na da su akwai 'yar tazara ka'dan...ledan hannu na na gyara dan ya fara min nawi hakan yasa na 'dago shi zuwa saman 'kirji na na rungume dalilin hakan yasa mayafin da ke rufe da jiki na ya kame min jiki sosai...bansan da faruwar hakan ba sam illah tsinkayar muryar Yah Deen da naji a tsawace yace" Ke...wani irin hauka ne wannan kuma?"
" Ke" da naji ya furta cikin maganar tasa ne ya sani tsayawa cak sannan na waigo dan ganin shin da wa yake.
Kicin-kicin naga yayi da idanu hakan yasa nayi gefe da nawa idanun ina jiran jin irin haukar da yace nayi...." Gyara mayafin ki".
Ya sake furtawa still suna tunkaro ni...sai a lokacin ma na 'dan fahimci abinda ya faru take sai kuma naji tsananin kunya ta lullu6e ni, tfiya na cigaba da yi ina me gyara mayafin nawa...shi kam haushi sosai ne ya cika shi da be san dalili ba...tunda ya tsinkayi irin kallon da su Imam ke bin baya na da shi yaji tsananin 6acin rai ya shige shi..sai da kuma yayi mata masifar sannan yaga wautar sa, to shishshigin miye kuma nayi?"
Ya tambayi kansa...'yar 'karamar tsaki ya saki a fili da yasa duk 'yan tafaiyar tasa suka kalle shi...dariya m ya bawa Anas sosai dan abinda yayin da yanda yayin tashin farko zaka fassara hakan da tsananin kishi ga wanda yasan asalin tushen kafuwar 'kauna.
Ina shiga parlour sai Anty Zee ta kalle ni da mamaki baki bu'de take min kallon ya haka?
Bance da ita 'kala ba har sai da na iso gefen ta na zauna sannan ta furta" Kin fasa zuwan ne kuma?"
Kai na girgiza mata tare da fa'din" Alhaji Baba ne yace ba yanzu ba".
" Ow woh...sai ki huta abin ki kafin lokacin da ya tsara 'din tayi..."
Bata gama rufe baki ba sai ga sallamar su Yah Deen da tawagar sa...tun ma kafin su 'karasa shigowa na mi'ke tsaye na nufi hanyar 'dakin Ammi da sauri na, ba naso in ha'da idanu da kowa daga cikin su bayan sun gama kalle min baya.
Zazzaunawa suka yi suna gaida Anty Zainab inda take amsawa da fara'ar ta...tana duban Yah Deen tace" Tunda yanzu kayi auren ka sai ka daina firgita mana yarinya kuma ko..kana gani fa yanzu da jin sallamar ku ta tashi ta gudu ciki..."
" Ni ina cin mutane ne Anty da zata guji inda nake?"
" Ni na sani maka ne..ga dai zahiri yanzu...kuma wallahi kabi a hankali in ba haka ba in kayi wasa ita zamu aura maka a ta biyu".
" Ai kuwa da kun kyauta masa Anty".
Cewar Anas yana 'yar dariya.
Anty ma murmushi tayi tana duban sa tace" 'yale shi mana ana masa gata yana min yanga".
Shi kam Yah Deen " Hmm"
kawai yace sannan ya 'kara da fa'din " Ina Ammi take?".
Anty ce ta bashi amsa da fa'din
" Tana ciki yanzu zata fito ma ai".
Nima acan 'daki na sami Ammi inda itama tace dani" ya kika dawo kuma me ya faru?"
Tayi maganar tanacduba na da kulawa da son jin ko wani abin ne ya hana ni tafiya
Sai nace da ita" Inji Alhaji Baba ne wai in bari ba yanzu zani ba".
" Saboda me yasa to?"
Nace
" Nima ban sani ba".
Inda nayi maganar ina cire mayafin da ke kaina.
" Ikon Allah".
Ammi ta fa'di da mamaki harda kama baki.
Ni kam ban damu ba nayi kwanciya ta tare da 'daukan abin da muke buga game ni da su Saif na fara bugawa batare da damuwr komai ba, dan nasan hakan bai ta6a faruwa ba, 'kila akwai dalilin da yasa Alhajin ya fa'di haka a yau 'din.
'Yar hira suke yi sama-sama da su har Ammi ta 'karaso nan duk suka gaida ta sannan suka cigaba da hira.
A can waje kuwa Alhaji Baba duban Ishaq yayi yace" Ya maganar mu?"
" Tana nan Alhaji..babu wanda ya sanar da shi har yanzu".
Murmushi kawai Alhaji Baba ya saki...sannan yace baka gane wancen yarinyar ba ko?"
" Erh gaskiya ban gane ta ba amma ina dai ganin ta agidan nan jifa-jifa".
" Itace Amaryar taku ai, kaga itama har yanzu bata san da maganar auren ba shiyasa na ce ta koma gida kar ra fita."
Take fara'a ta bayyana kan fuskar Ishaq yana murmushi yace" Masha Allah...Ubangiji Allah yayi albarka Alhaji..godiya muke da wannan za6i Allah ya 'kara girma".
" Ameen..Ameen..zan sanar da su da kaina idan naga dacewar lokaci insha Allahu..."
" To Alhaji hakan ma yayi..Allah ya
'kara girma"
Cewar Ishaq..Alhaji Baba kuwa cewa yayi
" Goben zaku koma ko?"
" Erh hakan da muka ce idan Allah yaso".
" Bakomai Ubangiji Allah ya kaimu goben...ka shiga ku gaisa da matan gidan tukunna ".
" To Alhaji".
Ya furta cikin girmamawa tare da juyawa ya koma ciki.
Da isar sa kuwa ya tarar da su kan maganar Fitan da Alhaji ya hanani wanda Ammi ce da kanta ta fara kawo maganar saboda tsananin mamakin da ya cikiu
Sallamar Ishaq ne ya dakatar da maganar da Ammi ke yi cuz ita kam sosai tayi mamaki, batun yau nake fita unguwa ba amma bai ta6a magana ba bai ta6a hanani zuwa ko'ina ba sai yau ka'dai, sannan kuma duk iya tunanin ta takasa hasko musababbabin faruwar hakan.
Ishaq kam da ya san dalilin kawai sai yake ta sakin murmushi, yanzu ne ya fahimci cewa dagaske babu wanda yasan auren dake tsakanin Deeni da yarinyar can, illah su Alhaji Baba...shi dai farin ciki kawai yake taya abokin sa da dacen da yayi...yasan ko shi da kansa aka bawa za6i a irin wancen lokacin ba zai iya za6o irin yarinyar ba, tashin farko ya fahimci natsuwar dake tattare da ita...ha'ki'ka Mu'een yayi dacen samun mace a duniuar nan.
Basu da'de tare da su Ammjn ba suka koma can gidan Yah Deen.
*****
'Bangaren Ma'u kam abin tausayi bata bari taje gida tana kuka ba, kuma sai tayi sa'a lokacin da ta isa gidan matar Baban ta ta shiga ma'kwabta, tana shiga sai ta wuce 'dakin ta ta kwanta tana faman bibiyar lamarin cikin ranta, bata da'de ba bacci yayi gaba da ita saboda maganin da ya bata mai 'karfi ne...ba ita ta shi ba sai kusan maghrib...Allah da ikon sa kuwa duk sai taji ciwon ya ragu...wanka ta sake yi tana ta 'ko'karin daidaita kanta gudun kar a fahimci yanayin da take ciki...matar baban ta sai mita take yi wai tun 'dazu ta tsaya baccin asara bata yi musu ko wanke-wanke ba.
Bata damu ba ita dai burin ta kawai kar a fahimci abinda ya faru tsakanin ta da Deeni kafin ya dawo neman auren ta kamar yadda yayi al'kawari.
Tana yin sallahr la'sar ta dawo ta tattara wanken-wanken ta wanke musu tas ta sake komawa 'dakin ta..tunanin ta kawai shine zuwa yaushe Yah Deen zai zo neman auren ta.
Bata sani ba ashe shi kam ma har ya manta da ita, balle tunanin auren ta...abinda ke gaban sa ma yawa ne da su.
Ammi kuwa rashin ganin an kawo amaryar Yah Deen gida ne ya matu'kar sa ta mamaki, ko da ta tambaye shi dalili sai cewa yayi shima fa bai sani ba..ya dai ji ance ba'a 'daura auren ba an fasa.
Abin sai ya sake 'daure mata kai, ga shi Alhaji bai zauna ba balle ta samu dama ta tambaye shi yana can yana fama da ba'kin sa.
Si taji ta kasa natsuwa da Anty Zainab suka tattauna maganar inda tace abin ya 'daure mata kai sosai itama kuma duk babu wanda yayi musu bayani, da farko ta zaci can Jigawa aka kai amaryar sai daga baya kuma tayi tuananin ba'a kaita can ba tunda ga shi maj auren anan ita zaman me zatayi acana ita ka'dai, amma tunda har anje an 'dauro auren kuma me yasa baza'a kawo amaryar gida ba.
Da daran ranar da yake ba'kin Alhajin duk sun watse anan Ammi ta sami daman ganawa da shi, tambayar sa tayi kan batun amaryar sai taga Alhaji Baba na murmushi yace mata ai tuntuni amaryar na gida.
Da gani na sai ya maida hankalinsa wuri na ina gaida shi ya amsa tare da 'karawa da fa'din" Uwata ina zuwa da sssafe haka?"
" Murmushi nayi sannan na 'daga kai na dubi harabar gidan inda duk rana ta mamaye ko'ina..." Ba sassafe bane fa Alhaji Babba kalli fa yanda rana ma tayi".
Na fa'di ina murmushi tare da nuno wurin.. shima Alhaji sai yayi murmushin..sannan ya sake fa'din unguwa zaki ne?"
Nace" Nace a a zanje in gaida Baban mu ne ".
Sai yace
" Ya kamata kam..dan inajin gobe ma zai koma...amma ki bari ba yanzu ba kinji maza ki koma cikin gida".
" To" kawai nace da shi tare da 'daga kaina na kalli su Yah Deen da ke tsatstsatye wanda da shi na fara ha'da idanu sai naga ya ta6e baki tare da kawar da kansa gefe, bansan me nayi masa ba dan haka sai nima 'dauke kaina daga kallon sa zuwa na gefen sa (Anas) shi kuma sai naga yana min murmushi ban damu ba kawai a jimlance nace da su " Ina kwanan ku?"
Mutun biyu zuwa uku ne daga cikin su suka amsa min wanda cikin sun kuwa ina da tabbacin babu Yah Deen a ciki.
Juyawa nayi na fara tafiya zuwa cikin gida yayin da Alhaji Baba ya nufi hanyar fita tare da 'kiran sunan Ishaq da alamun yana so su ke6e da shi, Ishaq sai ya bi bayan sa su Yah Deen kuwa cikin gidan suma suka 'karaso dan gaida su Ammi...in tafe suna bina abaya amma tsakani na da su akwai 'yar tazara ka'dan...ledan hannu na na gyara dan ya fara min nawi hakan yasa na 'dago shi zuwa saman 'kirji na na rungume dalilin hakan yasa mayafin da ke rufe da jiki na ya kame min jiki sosai...bansan da faruwar hakan ba sam illah tsinkayar muryar Yah Deen da naji a tsawace yace" Ke...wani irin hauka ne wannan kuma?"
" Ke" da naji ya furta cikin maganar tasa ne ya sani tsayawa cak sannan na waigo dan ganin shin da wa yake.
Kicin-kicin naga yayi da idanu hakan yasa nayi gefe da nawa idanun ina jiran jin irin haukar da yace nayi...." Gyara mayafin ki".
Ya sake furtawa still suna tunkaro ni...sai a lokacin ma na 'dan fahimci abinda ya faru take sai kuma naji tsananin kunya ta lullu6e ni, tfiya na cigaba da yi ina me gyara mayafin nawa...shi kam haushi sosai ne ya cika shi da be san dalili ba...tunda ya tsinkayi irin kallon da su Imam ke bin baya na da shi yaji tsananin 6acin rai ya shige shi..sai da kuma yayi mata masifar sannan yaga wautar sa, to shishshigin miye kuma nayi?"
Ya tambayi kansa...'yar 'karamar tsaki ya saki a fili da yasa duk 'yan tafaiyar tasa suka kalle shi...dariya m ya bawa Anas sosai dan abinda yayin da yanda yayin tashin farko zaka fassara hakan da tsananin kishi ga wanda yasan asalin tushen kafuwar 'kauna.
Ina shiga parlour sai Anty Zee ta kalle ni da mamaki baki bu'de take min kallon ya haka?
Bance da ita 'kala ba har sai da na iso gefen ta na zauna sannan ta furta" Kin fasa zuwan ne kuma?"
Kai na girgiza mata tare da fa'din" Alhaji Baba ne yace ba yanzu ba".
" Ow woh...sai ki huta abin ki kafin lokacin da ya tsara 'din tayi..."
Bata gama rufe baki ba sai ga sallamar su Yah Deen da tawagar sa...tun ma kafin su 'karasa shigowa na mi'ke tsaye na nufi hanyar 'dakin Ammi da sauri na, ba naso in ha'da idanu da kowa daga cikin su bayan sun gama kalle min baya.
Zazzaunawa suka yi suna gaida Anty Zainab inda take amsawa da fara'ar ta...tana duban Yah Deen tace" Tunda yanzu kayi auren ka sai ka daina firgita mana yarinya kuma ko..kana gani fa yanzu da jin sallamar ku ta tashi ta gudu ciki..."
" Ni ina cin mutane ne Anty da zata guji inda nake?"
" Ni na sani maka ne..ga dai zahiri yanzu...kuma wallahi kabi a hankali in ba haka ba in kayi wasa ita zamu aura maka a ta biyu".
" Ai kuwa da kun kyauta masa Anty".
Cewar Anas yana 'yar dariya.
Anty ma murmushi tayi tana duban sa tace" 'yale shi mana ana masa gata yana min yanga".
Shi kam Yah Deen " Hmm"
kawai yace sannan ya 'kara da fa'din " Ina Ammi take?".
Anty ce ta bashi amsa da fa'din
" Tana ciki yanzu zata fito ma ai".
Nima acan 'daki na sami Ammi inda itama tace dani" ya kika dawo kuma me ya faru?"
Tayi maganar tanacduba na da kulawa da son jin ko wani abin ne ya hana ni tafiya
Sai nace da ita" Inji Alhaji Baba ne wai in bari ba yanzu zani ba".
" Saboda me yasa to?"
Nace
" Nima ban sani ba".
Inda nayi maganar ina cire mayafin da ke kaina.
" Ikon Allah".
Ammi ta fa'di da mamaki harda kama baki.
Ni kam ban damu ba nayi kwanciya ta tare da 'daukan abin da muke buga game ni da su Saif na fara bugawa batare da damuwr komai ba, dan nasan hakan bai ta6a faruwa ba, 'kila akwai dalilin da yasa Alhajin ya fa'di haka a yau 'din.
'Yar hira suke yi sama-sama da su har Ammi ta 'karaso nan duk suka gaida ta sannan suka cigaba da hira.
A can waje kuwa Alhaji Baba duban Ishaq yayi yace" Ya maganar mu?"
" Tana nan Alhaji..babu wanda ya sanar da shi har yanzu".
Murmushi kawai Alhaji Baba ya saki...sannan yace baka gane wancen yarinyar ba ko?"
" Erh gaskiya ban gane ta ba amma ina dai ganin ta agidan nan jifa-jifa".
" Itace Amaryar taku ai, kaga itama har yanzu bata san da maganar auren ba shiyasa na ce ta koma gida kar ra fita."
Take fara'a ta bayyana kan fuskar Ishaq yana murmushi yace" Masha Allah...Ubangiji Allah yayi albarka Alhaji..godiya muke da wannan za6i Allah ya 'kara girma".
" Ameen..Ameen..zan sanar da su da kaina idan naga dacewar lokaci insha Allahu..."
" To Alhaji hakan ma yayi..Allah ya
'kara girma"
Cewar Ishaq..Alhaji Baba kuwa cewa yayi
" Goben zaku koma ko?"
" Erh hakan da muka ce idan Allah yaso".
" Bakomai Ubangiji Allah ya kaimu goben...ka shiga ku gaisa da matan gidan tukunna ".
" To Alhaji".
Ya furta cikin girmamawa tare da juyawa ya koma ciki.
Da isar sa kuwa ya tarar da su kan maganar Fitan da Alhaji ya hanani wanda Ammi ce da kanta ta fara kawo maganar saboda tsananin mamakin da ya cikiu
Sallamar Ishaq ne ya dakatar da maganar da Ammi ke yi cuz ita kam sosai tayi mamaki, batun yau nake fita unguwa ba amma bai ta6a magana ba bai ta6a hanani zuwa ko'ina ba sai yau ka'dai, sannan kuma duk iya tunanin ta takasa hasko musababbabin faruwar hakan.
Ishaq kam da ya san dalilin kawai sai yake ta sakin murmushi, yanzu ne ya fahimci cewa dagaske babu wanda yasan auren dake tsakanin Deeni da yarinyar can, illah su Alhaji Baba...shi dai farin ciki kawai yake taya abokin sa da dacen da yayi...yasan ko shi da kansa aka bawa za6i a irin wancen lokacin ba zai iya za6o irin yarinyar ba, tashin farko ya fahimci natsuwar dake tattare da ita...ha'ki'ka Mu'een yayi dacen samun mace a duniuar nan.
Basu da'de tare da su Ammjn ba suka koma can gidan Yah Deen.
*****
'Bangaren Ma'u kam abin tausayi bata bari taje gida tana kuka ba, kuma sai tayi sa'a lokacin da ta isa gidan matar Baban ta ta shiga ma'kwabta, tana shiga sai ta wuce 'dakin ta ta kwanta tana faman bibiyar lamarin cikin ranta, bata da'de ba bacci yayi gaba da ita saboda maganin da ya bata mai 'karfi ne...ba ita ta shi ba sai kusan maghrib...Allah da ikon sa kuwa duk sai taji ciwon ya ragu...wanka ta sake yi tana ta 'ko'karin daidaita kanta gudun kar a fahimci yanayin da take ciki...matar baban ta sai mita take yi wai tun 'dazu ta tsaya baccin asara bata yi musu ko wanke-wanke ba.
Bata damu ba ita dai burin ta kawai kar a fahimci abinda ya faru tsakanin ta da Deeni kafin ya dawo neman auren ta kamar yadda yayi al'kawari.
Tana yin sallahr la'sar ta dawo ta tattara wanken-wanken ta wanke musu tas ta sake komawa 'dakin ta..tunanin ta kawai shine zuwa yaushe Yah Deen zai zo neman auren ta.
Bata sani ba ashe shi kam ma har ya manta da ita, balle tunanin auren ta...abinda ke gaban sa ma yawa ne da su.
Ammi kuwa rashin ganin an kawo amaryar Yah Deen gida ne ya matu'kar sa ta mamaki, ko da ta tambaye shi dalili sai cewa yayi shima fa bai sani ba..ya dai ji ance ba'a 'daura auren ba an fasa.
Abin sai ya sake 'daure mata kai, ga shi Alhaji bai zauna ba balle ta samu dama ta tambaye shi yana can yana fama da ba'kin sa.
Si taji ta kasa natsuwa da Anty Zainab suka tattauna maganar inda tace abin ya 'daure mata kai sosai itama kuma duk babu wanda yayi musu bayani, da farko ta zaci can Jigawa aka kai amaryar sai daga baya kuma tayi tuananin ba'a kaita can ba tunda ga shi maj auren anan ita zaman me zatayi acana ita ka'dai, amma tunda har anje an 'dauro auren kuma me yasa baza'a kawo amaryar gida ba.
Da daran ranar da yake ba'kin Alhajin duk sun watse anan Ammi ta sami daman ganawa da shi, tambayar sa tayi kan batun amaryar sai taga Alhaji Baba na murmushi yace mata ai tuntuni amaryar na gida.