Sashe 68
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har kuwa muka isa layin gidan babu wanda yace da 'dan uwan sa uffan......akan layin gidan muka ha'du da Ma'u bansan me take yi a wurin ba, tana ganin mu kuwa sai naga ta washe ha'kora ta iso gaban mu..." Hudah ina zakuje haka naga kina ta fushi?...da alama ma kiyi kuka".
Tayi maganar tana kallon cikin idanu na.
Kafin nayi magana Saif sai yayi murmushi yana gyara zaman kayan dake hannun sa yace" Rabu da ita matsoraciya, gidan nan zamu fa shine take kuka".
Da murmushi Ma'u tace" Kuka kuma saboda me?"
" Wai tana tsoro"
Washe baki ta sake yi tace " haba da Allah tsoro kuma...muje in rakaku to nima kawai dama gida zan koma yanzu".
Tayi maganar tana kar6an abinda ke hannu na, ni kuwa da wuri na sake mata kamar dama jira nake yi ta kar6a.
Tunani na ko dan bata san waye a gidan bane shiyasa take wani azar6a6i....ashe Ma'u kam ta sani, mantawa ma nayi da cewa ni na gaya mata a gidan yake, dama kullum hanyar da zata 'kara ganin sa take nema shiyasa take yawan shawagi a arean gidan tamkar wata mai gadi, duk da haka kuwa sau d'aya tak ta gansa ranar ma zashi filin ball ne dayake ya fara fita ball.
Tun daga ranar bata 'kara ganin sa ba kusan kwana biyar kenan yanzu, sai yau da in ka lura zaka ga har jikin ta rawa yake yi saboda zata shiga wurin sa.
Ni har Saif duk bamu lura da yanayin ta ba, illah surutun ta da ta cika mu da shi sai ya 'dauke hankalin mu gaba d'aya.
Muna isa 'kofar gidan sai na ja tsaya na basu hanya, duk suka wuce ni, sai na 'kara jan baya ka'dan, Saif ne ya fara shiga da sallamar sa, sai Ma'u a bayan sa, ni kam 'kin shiga nayi nayi tsayuwa ta daga waje...Saif ma bai kulani ba da yake an riga an gama magana tun a gida, Ma'u kuwa hankalin ta ma bai kaina burin ta kawai ta shiga cikin gidan ta ganshi shiyasa bata ko bi ta kaina ba.
Da shigar su sai suka tarar shiru tamkar baya gidan, parlourn ma shiru.
Tsayuwa suka yi suna jiran sa duk da ko sallamar ta su bai amsa ba amma Saif bai damu ba cuz ya san wannan 'daya daga cikin halayyar sa ne, rashin amsa sallama musamman idan ba babba ne yayi ba, ko yanzun ma kuwa yana da ya'kinin yaji su sarai amsawar ce dai kawai ba zai yi ba.
...Ai kuwa hakan akayi, dan batare da ya amsa sallamar ba kawai ya fito daga bedroom 'din jikin sa ko riga babu illah wandon 3quarter a fili zaka ga dukkan baiwar halittar da Allah ya tsara masa na daga cikin sa har zuwa kansa gaba 'daya, Deen ba 'karamin kyakkyawa bane na 'karshe, sosai yayi sa'an fitowa cikin mutanen da ako ina za'a kirashi da kyakkyawa batare da haufi ba, yanda kansa ke cike da yalwattaccen gashi haka ma 'kirjin sa yake..... a hakan kuma ya 'karasa fitowa fuskar sa ba yabo ba fallasa ya 'karaso ya zauna kan kujera.
Ma'u kam tunda idanun ta yayi tozali dashi ai sai ta manta kanta gaba 'daya, ido ta tsura masa tana kallon fuskar sa ji take tamkar tayi ihu saboda farin ciki, haka kawai Allah ya jarabce ta da sonshi, so kuma mai tsanani irib masifaffen nan wanda bai san fulaku ba, tun Nanne na raye suke fama gashi yanzu Nanne ta tafi ta barta kamar wasa abin ya girma cikin zuciyar ta, kullum kwana take tana tashi da lodin soyayyar wanda bai ma san da zamanta cikin garin ba balle ya san matsayin sa a zuciyar ta.
" Yayah na yini?"
Saif yace da shi yana mai ko'karin ajiye kayan hannun sa.
"A'a shigar ciki mana".
Yayi maganar batare da ya amsa gaisuwar Saif ba illah gyarawa da yayi ya kishingi'da kan kujerar.
Saif sai ya kama hanyar shiga ciki kamar yanda aka umarce shi wanda sai lokacin Ma'u da rawar murya tace da shi " Ina..yi...ni?"
Bai amsa ba sai a lokacin kuma ya 'dago tare da kankance idanu yana kallan ta jin sabuwar murya kamar daga sama a tsakar kansa.
Suna ha'da idanu sai ya ha'de gira yayin da Ma'u ta fara rarraba idanu a 'kasa cike da bugun zuciya handle 'din flask 'din dake hannun ta ta kama da duka hannuwan ta biyu.
" Daga ina ke kuma?"
Yace da ita cike da mamaki yana kallon ta.
" Ni....?"
Tace a tsorace still muryan ta na rawa.
Bai amsa ba sai yace " Me kike yi anan nace?"
Yayi maganar a'dan tsawace har Saif dake ciki ma sai da ya jiyo shi.
"..Na..na rako su ne ".
Ta fa'di kamar zata zura da gudu.
Dai-dai fitowar Saif daga cikin bedroom 'din Yah Deen sai ya maida hankalin sa wurin sa...
" Saif nace ka ringa kwaso min mutane anan gidan ne? ko kuma tsabar rainin hankali ne?"
"A'a fa Yayah..Ammi ce ta aiko mu da Hudah ita kuma wai tana tsoro shine Ma'un ta kar6a tace zata rako mu".
Ba sai ya sake tambaya ba cuz ba yau yasan sunan ta hakan ba...a zafafe yace da Saif " Tsoron uban me take ji?"
Shiru sukayi dukkan su...a 'darare Ma'u ta ajiye flask 'din hannun ta ta kama hanyar fita, sai ya dakatar da ita da fa'din " My friend...come back here!"
Tana jin haka jikin ta na rawa ta dawo ta tsaya.
Abin shara ya nuna mata tare da mi'kewa sannan yace" Ki share parlourn ki goge shi and don't waste my time...zan fita ne yanzun".
Yana maganar ne yana tafiya zuwa cikin bedroom 'din nasa.
Ma'u da idanu ta rakashi har ya 'karasa shigewa ciki.
Sam bata zaci haka yake da masifa ba, idan ta ganshi awaje shiru-shirun nan sai ta zaci ko sau'kin hali gare shi har zuciya, baza manta ba da jimawa Huda na 'dan bata labarin sa amma sam bata sawa aka, musamman in 6angaren mugunta ce, gani take tamkar duk rashin jin su Hudah ne ya sanya yake yi musu hakan, bata san cewa haka asalin halin sa yake ba sai yau da ta fara gani...duk da haka Ma'u ko ka'dan bata ji haushi ba sai ma gani da tayi kamar ai dama ta samu tunda har ya sakata aiki a gidan sa kuma da kansa... farin cikin ta sai ya rinjayi raunin ta har hakan ya sanya zuciyar ta cika fal da farin ciki..a hakan tafara aikin tana 'dan murmushi.
( Ni kuwa nace, Babbar Cuta ta kama Ma'u gaskiya).
Shi kam Yah Deen bayi ya shige abinsa ransa ba'ki'kirin, duk zaton sa nice, shiyasa ko lokacin da ya fito bai damu da ya ga inda take tsaye ba saboda yasan dole zan gaida shi ko bai dubi inda nake ba.
Murya ta kawai yake son ji tana masa da'di...bambancin murya ta da ta Nanne kawai shirme ne da nake yi ada amma yanzu ma da sau'ki tunda 'kara girma nake yi ina 'kara wayo ina barin shirmen abaya, yayin da sautin murya ta ke 'kara riki'dewa zuwa na ta sak, Yah Deen ya gama saka rai da yaga Saif tare da wata shiyasa ma bai ko tsaya ya lura da yanayin bambancin halittar mu ba.
Sai a lokacin ma yaga wautar sa da tun farkon shigan sa 'dakin ya kasa gane bani bace tun awajen suturar mu, cuz yasan ji Ammi bata ta6a bari na in saka kayan da suka canza launi ko suka 'dan yage ko kuma kayan da ba'a goge ba, hakan yasa kullum zaka ganni fes dani bana ta6a zama da datti..tun daga 'kafafu idan ka duba zakaga bambanci dan ni 'kafata kullum fes take da haske yayin da 'kafar Ma'u tayi futu-futu da ita da yake ta zama wuri guda ita.
Tsayin mu zai kusan zuwa 'daya da Ma'u duk da kuwa tafini shekaru amma mu 'yan gidan mu muna da tsayi cikin halittar mu shiyasa muka zo kusan 'daya da Ma'u, amma tafini kaurin jiki dan ni haka nake tamkar muciya banda jiki sam sa6anin Ma'u da har ta fara ajiye halittar Allah a 'kirjin ta, ban sani ba ko dan kanta da hijab ne ya sanya bai gane bambamcin halittar mu ba...kuma ma daya ke ni ya saba gani a gidan su, kuma yasan ni jinin Nannen sa ce....sannan kuma ba zai ce ya tsane ni ba saboda wannan ala'kar, amma sau tari idan ya ganni na kan tuna masa da ita har hakan yake sawa yake 'dan yawaita kallo na koda asace ne.
Babban abinda yafi tsaya masa arai game dani kuma shine yanda muryar mu tazo iri 'daya da Nannen sa.
Shiyasa ma wani sa'in bai amsa gaisuwa ta saboda bugun da zuciyar sa keyi na sakamakon jin murya ta da yayi, amma ni sam bansan haka ba zato na ko kuma zallar tsana ce kawai da yake min da mugun halin sa.
Ranar da 'yan Jahilcin suka zo kuma yakanyi abinsa da gangan ne, idan yayi tunanin dama ni mutuwa ta d'auka ta bar masa sahibar sa, hakan sai yasa shi jin haushi na har ma ya'ki amsa gaisuwa ta...ha'ki'ka soyayyar Nanne ta zame masa ne tamkar ciwo a zuciyar sa wanda batada magani, ta kan motsa a duk lokacin da ta ga dama....da kanshi ya san cewa erh lallai Amina ta rasu ba kuma zata dawo ba har abada, da kansa ma yake yi mata adduah kusan kowace sallar sa, amma wannan dun'kulalliyar soyayyar tata ta kasa bajewa cikin zuciyar sa a lokacin, shi kansa bai san me ke 'kara ha66aka masa ita ba balle wani daban.
Saif fita yayi can waje domin ya dubo ni dan kar naji shiru inda ya same ni tsugunne daga waje na buga uban tagumi tamkar wata almajira da ta rasa madafa, ina jin an bu'de 'kofa na zabura na mike a razane.
Saif sai yayi murmushi.." Miye kuma?"
Ya tambaya yana kallo na da murmushi.
Narai-narai da idanu na nace " Ai tsoro ka bani".
Tayi maganar tana kallon cikin idanu na.
Kafin nayi magana Saif sai yayi murmushi yana gyara zaman kayan dake hannun sa yace" Rabu da ita matsoraciya, gidan nan zamu fa shine take kuka".
Da murmushi Ma'u tace" Kuka kuma saboda me?"
" Wai tana tsoro"
Washe baki ta sake yi tace " haba da Allah tsoro kuma...muje in rakaku to nima kawai dama gida zan koma yanzu".
Tayi maganar tana kar6an abinda ke hannu na, ni kuwa da wuri na sake mata kamar dama jira nake yi ta kar6a.
Tunani na ko dan bata san waye a gidan bane shiyasa take wani azar6a6i....ashe Ma'u kam ta sani, mantawa ma nayi da cewa ni na gaya mata a gidan yake, dama kullum hanyar da zata 'kara ganin sa take nema shiyasa take yawan shawagi a arean gidan tamkar wata mai gadi, duk da haka kuwa sau d'aya tak ta gansa ranar ma zashi filin ball ne dayake ya fara fita ball.
Tun daga ranar bata 'kara ganin sa ba kusan kwana biyar kenan yanzu, sai yau da in ka lura zaka ga har jikin ta rawa yake yi saboda zata shiga wurin sa.
Ni har Saif duk bamu lura da yanayin ta ba, illah surutun ta da ta cika mu da shi sai ya 'dauke hankalin mu gaba d'aya.
Muna isa 'kofar gidan sai na ja tsaya na basu hanya, duk suka wuce ni, sai na 'kara jan baya ka'dan, Saif ne ya fara shiga da sallamar sa, sai Ma'u a bayan sa, ni kam 'kin shiga nayi nayi tsayuwa ta daga waje...Saif ma bai kulani ba da yake an riga an gama magana tun a gida, Ma'u kuwa hankalin ta ma bai kaina burin ta kawai ta shiga cikin gidan ta ganshi shiyasa bata ko bi ta kaina ba.
Da shigar su sai suka tarar shiru tamkar baya gidan, parlourn ma shiru.
Tsayuwa suka yi suna jiran sa duk da ko sallamar ta su bai amsa ba amma Saif bai damu ba cuz ya san wannan 'daya daga cikin halayyar sa ne, rashin amsa sallama musamman idan ba babba ne yayi ba, ko yanzun ma kuwa yana da ya'kinin yaji su sarai amsawar ce dai kawai ba zai yi ba.
...Ai kuwa hakan akayi, dan batare da ya amsa sallamar ba kawai ya fito daga bedroom 'din jikin sa ko riga babu illah wandon 3quarter a fili zaka ga dukkan baiwar halittar da Allah ya tsara masa na daga cikin sa har zuwa kansa gaba 'daya, Deen ba 'karamin kyakkyawa bane na 'karshe, sosai yayi sa'an fitowa cikin mutanen da ako ina za'a kirashi da kyakkyawa batare da haufi ba, yanda kansa ke cike da yalwattaccen gashi haka ma 'kirjin sa yake..... a hakan kuma ya 'karasa fitowa fuskar sa ba yabo ba fallasa ya 'karaso ya zauna kan kujera.
Ma'u kam tunda idanun ta yayi tozali dashi ai sai ta manta kanta gaba 'daya, ido ta tsura masa tana kallon fuskar sa ji take tamkar tayi ihu saboda farin ciki, haka kawai Allah ya jarabce ta da sonshi, so kuma mai tsanani irib masifaffen nan wanda bai san fulaku ba, tun Nanne na raye suke fama gashi yanzu Nanne ta tafi ta barta kamar wasa abin ya girma cikin zuciyar ta, kullum kwana take tana tashi da lodin soyayyar wanda bai ma san da zamanta cikin garin ba balle ya san matsayin sa a zuciyar ta.
" Yayah na yini?"
Saif yace da shi yana mai ko'karin ajiye kayan hannun sa.
"A'a shigar ciki mana".
Yayi maganar batare da ya amsa gaisuwar Saif ba illah gyarawa da yayi ya kishingi'da kan kujerar.
Saif sai ya kama hanyar shiga ciki kamar yanda aka umarce shi wanda sai lokacin Ma'u da rawar murya tace da shi " Ina..yi...ni?"
Bai amsa ba sai a lokacin kuma ya 'dago tare da kankance idanu yana kallan ta jin sabuwar murya kamar daga sama a tsakar kansa.
Suna ha'da idanu sai ya ha'de gira yayin da Ma'u ta fara rarraba idanu a 'kasa cike da bugun zuciya handle 'din flask 'din dake hannun ta ta kama da duka hannuwan ta biyu.
" Daga ina ke kuma?"
Yace da ita cike da mamaki yana kallon ta.
" Ni....?"
Tace a tsorace still muryan ta na rawa.
Bai amsa ba sai yace " Me kike yi anan nace?"
Yayi maganar a'dan tsawace har Saif dake ciki ma sai da ya jiyo shi.
"..Na..na rako su ne ".
Ta fa'di kamar zata zura da gudu.
Dai-dai fitowar Saif daga cikin bedroom 'din Yah Deen sai ya maida hankalin sa wurin sa...
" Saif nace ka ringa kwaso min mutane anan gidan ne? ko kuma tsabar rainin hankali ne?"
"A'a fa Yayah..Ammi ce ta aiko mu da Hudah ita kuma wai tana tsoro shine Ma'un ta kar6a tace zata rako mu".
Ba sai ya sake tambaya ba cuz ba yau yasan sunan ta hakan ba...a zafafe yace da Saif " Tsoron uban me take ji?"
Shiru sukayi dukkan su...a 'darare Ma'u ta ajiye flask 'din hannun ta ta kama hanyar fita, sai ya dakatar da ita da fa'din " My friend...come back here!"
Tana jin haka jikin ta na rawa ta dawo ta tsaya.
Abin shara ya nuna mata tare da mi'kewa sannan yace" Ki share parlourn ki goge shi and don't waste my time...zan fita ne yanzun".
Yana maganar ne yana tafiya zuwa cikin bedroom 'din nasa.
Ma'u da idanu ta rakashi har ya 'karasa shigewa ciki.
Sam bata zaci haka yake da masifa ba, idan ta ganshi awaje shiru-shirun nan sai ta zaci ko sau'kin hali gare shi har zuciya, baza manta ba da jimawa Huda na 'dan bata labarin sa amma sam bata sawa aka, musamman in 6angaren mugunta ce, gani take tamkar duk rashin jin su Hudah ne ya sanya yake yi musu hakan, bata san cewa haka asalin halin sa yake ba sai yau da ta fara gani...duk da haka Ma'u ko ka'dan bata ji haushi ba sai ma gani da tayi kamar ai dama ta samu tunda har ya sakata aiki a gidan sa kuma da kansa... farin cikin ta sai ya rinjayi raunin ta har hakan ya sanya zuciyar ta cika fal da farin ciki..a hakan tafara aikin tana 'dan murmushi.
( Ni kuwa nace, Babbar Cuta ta kama Ma'u gaskiya).
Shi kam Yah Deen bayi ya shige abinsa ransa ba'ki'kirin, duk zaton sa nice, shiyasa ko lokacin da ya fito bai damu da ya ga inda take tsaye ba saboda yasan dole zan gaida shi ko bai dubi inda nake ba.
Murya ta kawai yake son ji tana masa da'di...bambancin murya ta da ta Nanne kawai shirme ne da nake yi ada amma yanzu ma da sau'ki tunda 'kara girma nake yi ina 'kara wayo ina barin shirmen abaya, yayin da sautin murya ta ke 'kara riki'dewa zuwa na ta sak, Yah Deen ya gama saka rai da yaga Saif tare da wata shiyasa ma bai ko tsaya ya lura da yanayin bambancin halittar mu ba.
Sai a lokacin ma yaga wautar sa da tun farkon shigan sa 'dakin ya kasa gane bani bace tun awajen suturar mu, cuz yasan ji Ammi bata ta6a bari na in saka kayan da suka canza launi ko suka 'dan yage ko kuma kayan da ba'a goge ba, hakan yasa kullum zaka ganni fes dani bana ta6a zama da datti..tun daga 'kafafu idan ka duba zakaga bambanci dan ni 'kafata kullum fes take da haske yayin da 'kafar Ma'u tayi futu-futu da ita da yake ta zama wuri guda ita.
Tsayin mu zai kusan zuwa 'daya da Ma'u duk da kuwa tafini shekaru amma mu 'yan gidan mu muna da tsayi cikin halittar mu shiyasa muka zo kusan 'daya da Ma'u, amma tafini kaurin jiki dan ni haka nake tamkar muciya banda jiki sam sa6anin Ma'u da har ta fara ajiye halittar Allah a 'kirjin ta, ban sani ba ko dan kanta da hijab ne ya sanya bai gane bambamcin halittar mu ba...kuma ma daya ke ni ya saba gani a gidan su, kuma yasan ni jinin Nannen sa ce....sannan kuma ba zai ce ya tsane ni ba saboda wannan ala'kar, amma sau tari idan ya ganni na kan tuna masa da ita har hakan yake sawa yake 'dan yawaita kallo na koda asace ne.
Babban abinda yafi tsaya masa arai game dani kuma shine yanda muryar mu tazo iri 'daya da Nannen sa.
Shiyasa ma wani sa'in bai amsa gaisuwa ta saboda bugun da zuciyar sa keyi na sakamakon jin murya ta da yayi, amma ni sam bansan haka ba zato na ko kuma zallar tsana ce kawai da yake min da mugun halin sa.
Ranar da 'yan Jahilcin suka zo kuma yakanyi abinsa da gangan ne, idan yayi tunanin dama ni mutuwa ta d'auka ta bar masa sahibar sa, hakan sai yasa shi jin haushi na har ma ya'ki amsa gaisuwa ta...ha'ki'ka soyayyar Nanne ta zame masa ne tamkar ciwo a zuciyar sa wanda batada magani, ta kan motsa a duk lokacin da ta ga dama....da kanshi ya san cewa erh lallai Amina ta rasu ba kuma zata dawo ba har abada, da kansa ma yake yi mata adduah kusan kowace sallar sa, amma wannan dun'kulalliyar soyayyar tata ta kasa bajewa cikin zuciyar sa a lokacin, shi kansa bai san me ke 'kara ha66aka masa ita ba balle wani daban.
Saif fita yayi can waje domin ya dubo ni dan kar naji shiru inda ya same ni tsugunne daga waje na buga uban tagumi tamkar wata almajira da ta rasa madafa, ina jin an bu'de 'kofa na zabura na mike a razane.
Saif sai yayi murmushi.." Miye kuma?"
Ya tambaya yana kallo na da murmushi.
Narai-narai da idanu na nace " Ai tsoro ka bani".