← Book details Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 209 OF 211

Sashe 209

Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

" Lafiya ta qalau Ammi..kawai fa wasa nake yi mata".
" Baka da hankali!.."
" Thank u Madame"
Ya bata amsa yana murmushi.
Tace
" Idan ka sake rikita min yarinya Allah ni da kai Mu'een zaka zo ka same ni ne"
Yana 'yar dariya yace
" Sorry Ammi..yarinyar taki ne bata ji shiyasa"
" Haka ma kace ko to wallahi ka yadda ta sake 'kira na kan hakan ka gani..kasan hali naai ba sai na sake gaya ma ba, this time around idan na dawo da ita gaba na har abada tsakanin ka da ita sai dai hange..ai kasan wace ni".
" Ai kuwa da mutuwa zan yi Ammi...itace bugun numfashi na fa..".
" Ka gwada ka gani kana wasa da ni ne..."
Dariya sosai yayi sannan yace
" Kiyi ha'kuri Ammi insha Allahu baza'a sake ba...daga yau na daina".

Noor dake parlour jin muryar sa yana waya garau ya sanya ta tahowa da sauri dan ta ganewa idanun ta shin kunnuwan ta 'karya suke yi mata ko kuwa dagske shi 'dinne har da dariya.
Zaune ta hange shi kunnan sa ma'kale da waya yana dariya.

Mutuwar tsaye tayi tana duban sa da tsananin mamaki take cigaba da sauraran surutun da yake yi.

Mutum da ko hannun sa ma baya iya 'dagawa shine kuma yanzu take gani zaune har yake wannan uban surutun?

Comment
Vote
Share

*Salmerh ce* 😍

💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)

By
*Salmerh MD*

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

_*Daga marubuciyar Littafin CAPTAIN ABBAS*_

*Last Page* 💯

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *94*

Mamaki 'karara ya bayyana kan fuskar ta, sai ta rasa shin kuka zata yi ne ko kuma dariya...yana cire wayan daga kunnan sa suka ha'da idanu da ita.

Murmushi kawai yayi gami da cire duvet daga saman jikin sa ya tashi ya nufi bayi tsab kamar bashi babu wani dafe 'kirji da ri'ke bango bai ko sake kallon inda take ba ma.

Tana ganin ya shige bathroom da kansa taji wani 'kululun takaici ya kamata ashe dama lafiyar sa 'kalau shine yake ta wahal da ita.

Komawa tayi jikin window ta dafe 'karfen windown tana hawaye..babu tunanin da bai zo ranta ba, sam ta rasa dalilin da yasa yayi mata hakan.

Fitowar sa daga bayin sai yaga bata inda take tsaye..bai tsaya ba sai ya bi bayan ta inda ya hango ta jikin window tana kuka mayafin dake kanta ya 'dan zamo yana iya hango tsefaffen gashin kanta dake nan 'daure cikin ribbom guda.

A hankali.ya tako zuwa inda take ya matso daf da ita da kansa yasan be kyauta mata ba dan wahala sosai ya bata ya ringa yi mata wasa da hankali.

.. ..kusa da kanta ya kawo fuskar sa yana sha'kan 'kamshin da kanta ke fitar wa...a hankli ya maida idanun sa ya lumshe tare da matsawa jikin ta sosai.

Tana jin motsin sa kusa da ita kawai sai ta juya gami da sar'ke hannun ta a wuyan sa bai wani 6ata lokaci ba ya ha'de musu baki ya fara kissing 'din ta irin wanda ta manta a rayuwar ta cewa ana yin irin sa...lumshe idanu tayi tana kar6an sa'kon nasa gami da jin zuciyar ta wasai musamman da yake yanzu ta fahimci cewa mijin ta lafiya 'kalau yake babu abinda ke damun sa.

Tsawon lokaci kafin ya rabu da ita wanda kamar jira take kuma sai tayi saurin juya masa baya tana fuskantar windown.

Murmushi mai 'kayatarwa yayi gami da kai hannun sa gefen wuyan yana yi mata tafiyar tsutsa yace" What kuma?...bayan kin gama cinye min baki shine kuma zaki juya min baya?"
Ya 'karasa maganar da sau'kar da kansa saman wuyan ta.
Kafa'da ta no'ke tana lumshe idanu amma bata ce da shi komai ba.

Abubuwan
da taji yana fa'dawa Ammi cikin waya sune suke dawowa 'kwa'kwalwar ta...murmushi tayi tana jin 'kaunar mijin ta na ratsa mata zuciya.

Ganin baza ta juyo ba ya sanya shi cire hannun sa daga jikin ta ya 'dan matsa baya ka'dan yana murmushi...'kirjin sa ya dafe gami da fa'din" Wash..!"
Ai da sauri ta waigo tana zare idanu har ta ma manta da cewa ciwon 'karya yake yi.

Da ganin ta juyo 'din sai ya tuntsire dariya yana nuna ta...kicin-kicin tayi da fuska tamkar zatayi kuka.." Ba gashi kin juyo ba yanzu ai na gano maganin masu taurin kai cikin sau'ki".

Shagwa6e fuska tayi ta taho da sauri zata gifta gefen sa ta wuce sai yayi saurin kamo hannun ta fa'da jikin sa ya rungume ta.

Dukkan su ajiyan zuciya suka sau'ke mai cike da ma'anoni da dama.

*****
Cikin lokaci 'kan'kani suka daidaita zaman auren su har ma sun fara shirye-shiryen komawa gida inda Deen yace da zarar sun koma zasu wuce Umrah dan cika burin Jasmine 'din su kamar yadda yayi al'kawari.

Yanayin 'kaunar da yake nuna mata ita kanta yanzu tasan ba irin na baya bane...sannan ko ita kanta ma bata yadda ta sake yin wani sakaci kamar yadda ta aikata abaya ba.

Sosai ta ri'ke mijin ta hannu bibbiyu ta jashi a jiki.
Sam yanzu bata kuskuren hana shi hakkin sa dake kanta dan ta fahimci ko abubuwan da suka ta faruwa abaya ma ciki harda laifukan ta.

Darasin rayuwa kala-kala yanzu ta koya.
Wani sa'in har ji take kamar yanzu ne suka yi sabon aure da shi domin sai yanzun ne suka yi sha'kuwar da ya kamata ace sun yi ta tun a baya amma sai suka kasa fahimtar junan su wancan lokacin.

Ko lokacin da suka koma gida ma ba 'karamin farin ciki Ammi tayi da ganin su ba, jikin Deen ya 'dan koma sai dai har yanzun ba kamar baya can da yake rayuwar sa cikin farin ciki ba.

Sai dai da yake har yanzun bai daina kar6ar magunguna ba ya sanya basu wani damu ba domin sun san with time komai zai daidaita ne, balle ma sun san yanzu ya riga ya samu abinda yake so in ba wani ikon Allah kam tafiya mai nisa ciwon zai yi.
Yana zuwa kuma ana sake duba shi a duk lokacin da bu'katar hakan ta taso...sannan baya sa6a dokar shan maganin sa bisa 'ka'ida yake shan su, da ya 'dan kuskure lokaci ma Noor zata tunatar da shi.

Ummah kanta ji tayi kamar ta goya su saboda farin ciki sai dai kunya bai barta ta bayyana hakan a fili ba...Albarka ta ringa sa musu tana yi musu fatan Alkhairi cikin rayuwar su da samun zuri'a 'dayyiba.

Satin su biyu da dawowa suka wuce Umrah...Yah Deen da ya gansa gaban ka'abah sosai jikin sa yayi sanyi...Noor kuwa kasa jurewa tayi sai da ta zubda hawaye, bata ta6a manta kalaman Jasmine da kuma burin ta na son zuwa Makkah da Madinah taga 'dakin Allah ba, yau gashi Allah ya nufe su da zuwa amma babu ita.

Addu'ah sosai suka yi kafin su dawo...ko a Madinah sai da suka 6ata lokaci sosai dan kusan satin su uku kafin suka juyo gida.

Ginin da ake yi na gidan mai 'din Ammi ma ba'a jima da kammala shi ba... *T. Manga and sons* aka sanya wa gidan man.

...Ishaq Alhaji Baba ya 'dora matsayin manager na gidan mai 'din dama a kullum burin sa bai wuce yaga yayi wa Ishaq wani abin da zai taimaki rayuwar sa ba domin yanda Ishaq ke son zuri'ar sa ka'dai ya sa yake birge shi balle tuni ya koma yi masa kallon 'da kamar su Muhammad, har cikin zuciyar sa yake jin sa.

Sosai Ishaq ya nuna tsantsan farin cikin sa da wannan karramawa da Alhaji yayi masa dama aikin da yake yi ba wani ku'din kirki ake biyan sa ba 40k ne duk 'karshen wata ake bashi, sai ga shi tashin farko matsayin manager ya fito inda za'a biya shi maku'dan ku'dade...amfanin zama da mutane masu karamci kenan.

Hatta Sani da ke can jihar Plateau Alhaji Baba sai da ya nemo shi shima ya bashi aiki agidan man, cikin sa'a kuwa albarkar Allah tuni ta sau'ka akan sa...sosai suke samun 'karuwa abin ba'a cewa komai.

Saif ma anan yake aiki sai dai bai kai Ishaq matsayi ba Sani kuwa dama dake be yi wani karatun kirki ba a matsa mai kawai ya tsaya...Zaidu kuwa na can wurin Uncle Ja'afar shima a shekarar nan yayi retire daga aikin sa sai dai babu ranar dawowa gida, dan kuwa acan ya samawa Zaidu aiki shima a wani bankin daban mai suna Gt ba wanda yayi nasa aikin ba.

Tuni anyi bikin Ishaq ya tare da amaryar sa anan Azare, nuna mata matsayin da gidan Alhaji Taheer Manga ke da shi a wurin sa yayi koda wasa baya nuna mata wani bambamcin da zai sa taji ta raina wani daga cikin familyn, matsayin iyaye ya basu ita ma kuma kan hakan ya 'dora ta.

Imrana kam na can tun da 'yan drugs suka tafi da shi ba'a sake jin 'duriyar sa ba...ashe wai sai da 'kwayoyi yake yi da manyan abubuwan maye shiyasa har yanzun ba'a sake shi ba.

Mu'een duk ya manta da shi sai ranar yana wucewa ya hango wasu 'yan shaye-shaye shine Imrana ya fa'do ransa da yake ya jima da sanin cewa inda Imrana yafi kauri kenan amma duk da hakan yake abota da shi da kansa ya sha bashi ku'da'de yana zuwa yana sayen kayan mayen sa da shi, tun lokacin da suka zo gidan sa ne shikenan yaji ya fita ransa bai kuma neman sa ko shiga harkar sa ba.

Sake kallon su yayi sai ya girgiza kansa, yara 'kanana ne amma duk sun lalata rayuwar su da shaye-shaye.
Cikin zuciyar sa ya furta Allah ya sauwa'ka ya shirya mu baki 'daya...Allah ya baku baki amma 'karfi da yaji kun maida shi salansa kuna ta 'karawa duniya hazo...manyan ku ma basu ci nasara ba balle ku... *_Allah Ubangiji ka raba mu da aikin dana sani da mu da Zuri'ar mu da ma Al'ummar Musulmai baki 'daya_ .*
Chapter 209 · 0% Book details