Sashe 80
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Allah sarki Mahaifin Ma'u kuwa ganin kamar ya warware matsalar Imrana ne ya sanya shi bayan wasu watanni kamar uku ya dawo da 'yar sa Ma'u gaban sa ya cigaba da kulawa da abin sa da fatan Allah ya bata miji nagari ya aurar da ita ya huta wa ransa.
Comment
Vote
Share
*Salmerh ce*😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
🤞🏻
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *40*
Lokaci sun 'dan ja sosai, dan kusan watanni shida kenan da ganin da na yiwa Yah Deen da budurwar sa na farko, ko hutun can ma kuwa daya zo na 'kara ganin su, marasa kunya a 'kofar gida ganin dan unguwar babu mutane sosai ya sanya ko kunyar Allah basu jiba suke kissing juna ga dukkan alamu ta fito zata tafi ne.
Ni kuwa yanzu har na saba da bi ta gidan da yake matu'kar yana gari idan zani gidan Ummah ta sai nabi ta can dan kawai inga ko wannan farar motar tazo...bansan me yasa na damu da zuwan motar ba duk kuwa da cewa idan na ganin na kanji haushi sosai har cikin raina, sau tari kuwa ina ganin motar, sai dai bansan me suke aikata wa ba a cikin gidan tunda ba gani nayi da idanu na ba amma koma de miye ina da tabbacin ba abin alkhairi bane.
Ko Ammi ma yanzu kwata-kwata ta daina aika na wurin sa, idan yana son abu sai dai shi da kansa yazo ko kuma ya aiko yaro amma Ammi bata tura ni sam...musamman ma da ta fahimci irin tsoron sa da nake yi sosai.
*****
Yau 'din ma kuwa gidan Ummah ta zani gaida Addah ta Maryam da tazo tun jiya, ni ka 'dai nake tafiya ta cikin hankali kaina 'kasa, sai dai maimakon in 'dauki hanyar gidan Ummah direct a a sai na yanka na kama hanyar da zata sada ni da gidan Yah Deen.
Tun daga nesa na fara hango motar take sai naji wani iri cikin raina, sai dai duk da naga motar ban dakatar da tafiyar da nake yi ba inda nake sake tunkarar gidan ban kuma san me ke ingiza ni ba kawai dai nasan bai wuci tsabar gulma ba, cak na tsaya ganin ta fito ita ka'dai ta shiga motar ta taja tayi gaba har ta 'karasa wucewa ban ga ya fito ba ga dukkan alamu dai ranar bai yi mata rakiya ba.
Juyawa nayi da sauri na kama hanya 'kafafu na har na sar'kewa saboda yanda jiki na ke rawa da ganin Husnan.
Husnah kam yanzu hat ta saba da zuwa wajen sa ma ko ganin wahalar hakan batayi balle rashin dacewar sa, ko da shi bai 'kira ta saboda bu'katar sa ba ita da kanta ma bata iya sati batare da ta zo inda yake ba hakan yasa jama'ah da dama suka farga da zirga-zirgan da take yawan yi a garin musamnan da kowa ua san cewa gidan da take zuwa 'din gidan 'dan Alhaji Baba ne kuma shi ka'dai ke zama a gidan.
Sannan zuwan Husnah yana farawa ne da zarar ya dawo hutu gida, idan akace baya nan kuwa ba'a ta6a ganin ta tazo, wannan dalilin ya sanya jama'ah zargin wannan ala'kar tasu tare da dasa tunani a zu'katan jama'ah.
Haka na isa gida wata iri da ni sam na rasa walwala ta, su'kuku na yini ranar gaba 'daya, abin na ci na arai amma ban iya na sanar da kowa ba...koda su Addah ta suka tisani gaba da tambayar abinda ke damu na sai cewa nayi kaina ke ciwo, ai kuwa take aka nemo min magani na sha dan dole ba dan raina ya so ba.
Ana saura sati biyu zai koma school ranar da sassafe Alhaji Baba ya 'kira shi a waya inda yace yazo ya same shi....
Yanayin da yaji muryar Alhaji Baba yayi maganar ya sanya bai 6ata lokaci ba ya iso gidan dan cika umarnin Alhajin.
Bayan sun gaisa cikin sakin fuska sai Alhaji Baba ya tambaye shi cewa " Abinda yaji gaskiya ne ko kuwa, ance wata yarinya na yawan zuwa wancen gidan da kake, wacece ita?" Numfashi Alhaji Baba ya sau'ke tare da cigaba da fa'din " Ni da kaina naga tana shiga gidan rannan ko ba ita bace ke zuwa da farar mota?"
Ya 'karashe maganar yana kallon fuskar Yah Deen domin karantar yanayin sa.
Yah Deen kam zuciyar da 'karfi ta tsinke saboda ka'duwa, cike da firgici ya 'daga idanu ya kalli Alhaji sai kuma ya sake sunkuyar da kansa 'kasa nan take, baya fatan ace Alhaji Baba da kansa ya gansa da Husnah da idanun sa, in hakan ne kuwa ya shiga uku da tarin abin kunya ai.
Hakan da yayi ka'dai sai ya tabbatar wa Alhaji Baba cewa ba zargi ake wa Mu'een ba komai da yaji gaskiya ne....duk da fahimtar hakan da yayi amma sai ya 'kara tambayar sa saboda tabbatar wa duk da ya san da wuya ne Yah Deen 'din ya iya bu'dan baki ya sanar da shi gaskiyar lamari amma ua zama dole ya bincika saboda gano wace iriyar rayuwa yake yi da har mutane ke masa habaicin wai _ko 'dan Alhaji yayi aure ne bamu sani mun sanya albarka ba_ .
Cikin dakiya Yah Deen ya bu'di baki batare da ya iya kallon Alhaji Baba ba yace " Ni...Alhaji...Babu kowa da ke zuwa wuri na".
Wanda ya fa'di hakan ne bayan Alhaji Baba ya maimaita tambayar da yayi masa da farko.
Murmushin takaici Alhaji Baba yayi...yayin da Yah Deen ya ayyana irin yanda zai ci ubana a cikin ransa, tunanin sa gaba 'daya kaina ya tafi dan shi a tunanin sa ni ka'dai nasan ala'kar sa da Husnah sai kuma Imrana, shi kuwa ya san ba zai ta6a zuwa ya sanar da Alhaji wannan zancen ba.
Cikin natsuwa Alhaji Baba yayi masa fa'da ta yadda zai gane abinda yake yi 'din ba dai-dai yake aikatawa ba....inda ya 'karasa da fa'din idan aure yake son yi shi bashi da matsala zai iya yi masa jagora a kowani lokaci ko yau ko gobe sati ko wata a shirye yake kuma zai 'dau nauyin fahimtar da Uncle Ja'afar ma ba abin damuwa bane...Yace ya sanar da shi ko 'yar gidan waye shi zai je ya nema masa auren ta yafi akan a zarge ka da abinda bashi bane ko da baka aikata ba da ciwo balle ma babu mai yadda da kai tunda yarinyar ba muharramar ka bace ita.
Kansa 'kasa yace " Babu komai tsakani na da ita Alhaji ba wani batun aure.."
" Toh me yasa take zuwa gurin ka?"
"...Course mate 'dina ce..abu take zuwa kar6a".
Baya Alhaji Baba ya koma ya jinginu...sam baya son 'dan sa ya fa'da irin wannan rayuwar da jama'ah ke zargin sa da shi ko a mafarki baya son ace shike aikatawa.
Amma saboda baya son ya ja maganar sosai dan ransa 'kara yaci yake yi...ya sanya shi ta'kaita batun da fa'din " Naji...amma Muhammad ka sani.. matu'kar ka kuskura na 'kara ji ko ganin abu makamancin hakan ya faru wallahi duk matakin dana ga dama shi zan 'dauka akan ka sam bazan lamunci rashin 'da'a ba, kana jina ko?"
Da " Erh " ya amsa yana mai jin da'din rashin tsananta bincike da Alhaji bai yi ba.
Yana cikin tunanin hakan yaji Alhaji Baba na fa'din " Tashi ka bani wuri...Allah ubangiji ya shirye ka bisa tafarkin tsira".
Da 'dan hanzari ya bar gaban Alhaji Baba ya nufi wurin Ammi...
Yana shiga parlourn ni kuma sai gani na fito cikin shirin zuwa makaranta ina 'ko'karin dai-dai ta zaman jaka ta ya shigo hankalin Ammi ma duk na kaina.
Muna ha'da ido da shi sai ya wani banka min harara cike da 6acin rai, take sai nayi 'kasa da idanu na bansan me na aikata ba kuma yau 'din da aka tare ni da mugun kallo.
'Karaso wa yayi ya zauna a kujera dake facing Ammi...sai lokacin kuma Ammi ma ta ganshi...kafin tayi magana sai nace da ita " Ammi na tafi".
" Adawo lafiya mama na"
Ta bani amsa amma hankalin ta na kansa.
Sum-sum nayi ficewa ta da yake tun lokacin da ya shigo gidan mun ha'du kuma na gaishe shi a lokacin kuma banga yayi min mugun hali ba, Ammi ce dai basu ha'du ba kawai ya shiga wurin Alhaji.
Ita kam ma sam bata san da cewa yana gidan tun 'dazu ba, bata kuma san da wannan batun ba haka bata san me suka tattauna da Alhaji Baba ba ta dai gansa wani iri sai faman kau da kai yake kamar munafuki, yana gaida ta ko abinci bai tsaya ya ci ba kawai yace da ita ya tafi.
Ammi da idanu ta raka shi har ya 'karasa fita, bata damu ba cuz ta sha ba'kin halin nasa ne yau ya motsa.
Ko da ya koma gida bai iya ya sanar da Husnah cewa kar ta sake zuwa ba kamar yadda aka garga'de shi, ita kuwa yanzu sosai ta jarabtu da shi dan yana yi mata natan, ta kan yawaita shirga wa mahaifiyar ta 'karya n zata guri kaza idan ta fito sai ta nufo wurin Mu'een, sau da dama ma baya sanin zata zo sai dai kawai kwatsam ya ganta ba kuma yace mata me yasa kawai sai su shiga sha'anin su.
Shai'danin bai ta6a complaint akan hakan ba da yake shima 'din baya wuce tayi musamman idan akan Husnah ne.
Haka ranar ya wuni wani iri da shi..bai fita ko'ina ba ko neman abinci bai je yayi ba, Imrana ne ya nemo musu 'dan abin tabawa dangin drinks shima 'din ba wani na kirki ya sha ba ya bari, ko da Husna ta 'kira shi a waya kuwa sama-sama ya amsa ta, wanda jn sa wani iri ya sanya ta tambayar ko lafiya ...baka jin da'di ne? sai yace mata "Erh"
A takaice.
Take ta rikice ta fara yi mai sannu a jere...bai amsa ko 'daya ba kawai ya yanke 'kiran yama kashe wayar tasa gaba 'daya.
Comment
Vote
Share
*Salmerh ce*😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
🤞🏻
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *40*
Lokaci sun 'dan ja sosai, dan kusan watanni shida kenan da ganin da na yiwa Yah Deen da budurwar sa na farko, ko hutun can ma kuwa daya zo na 'kara ganin su, marasa kunya a 'kofar gida ganin dan unguwar babu mutane sosai ya sanya ko kunyar Allah basu jiba suke kissing juna ga dukkan alamu ta fito zata tafi ne.
Ni kuwa yanzu har na saba da bi ta gidan da yake matu'kar yana gari idan zani gidan Ummah ta sai nabi ta can dan kawai inga ko wannan farar motar tazo...bansan me yasa na damu da zuwan motar ba duk kuwa da cewa idan na ganin na kanji haushi sosai har cikin raina, sau tari kuwa ina ganin motar, sai dai bansan me suke aikata wa ba a cikin gidan tunda ba gani nayi da idanu na ba amma koma de miye ina da tabbacin ba abin alkhairi bane.
Ko Ammi ma yanzu kwata-kwata ta daina aika na wurin sa, idan yana son abu sai dai shi da kansa yazo ko kuma ya aiko yaro amma Ammi bata tura ni sam...musamman ma da ta fahimci irin tsoron sa da nake yi sosai.
*****
Yau 'din ma kuwa gidan Ummah ta zani gaida Addah ta Maryam da tazo tun jiya, ni ka 'dai nake tafiya ta cikin hankali kaina 'kasa, sai dai maimakon in 'dauki hanyar gidan Ummah direct a a sai na yanka na kama hanyar da zata sada ni da gidan Yah Deen.
Tun daga nesa na fara hango motar take sai naji wani iri cikin raina, sai dai duk da naga motar ban dakatar da tafiyar da nake yi ba inda nake sake tunkarar gidan ban kuma san me ke ingiza ni ba kawai dai nasan bai wuci tsabar gulma ba, cak na tsaya ganin ta fito ita ka'dai ta shiga motar ta taja tayi gaba har ta 'karasa wucewa ban ga ya fito ba ga dukkan alamu dai ranar bai yi mata rakiya ba.
Juyawa nayi da sauri na kama hanya 'kafafu na har na sar'kewa saboda yanda jiki na ke rawa da ganin Husnan.
Husnah kam yanzu hat ta saba da zuwa wajen sa ma ko ganin wahalar hakan batayi balle rashin dacewar sa, ko da shi bai 'kira ta saboda bu'katar sa ba ita da kanta ma bata iya sati batare da ta zo inda yake ba hakan yasa jama'ah da dama suka farga da zirga-zirgan da take yawan yi a garin musamnan da kowa ua san cewa gidan da take zuwa 'din gidan 'dan Alhaji Baba ne kuma shi ka'dai ke zama a gidan.
Sannan zuwan Husnah yana farawa ne da zarar ya dawo hutu gida, idan akace baya nan kuwa ba'a ta6a ganin ta tazo, wannan dalilin ya sanya jama'ah zargin wannan ala'kar tasu tare da dasa tunani a zu'katan jama'ah.
Haka na isa gida wata iri da ni sam na rasa walwala ta, su'kuku na yini ranar gaba 'daya, abin na ci na arai amma ban iya na sanar da kowa ba...koda su Addah ta suka tisani gaba da tambayar abinda ke damu na sai cewa nayi kaina ke ciwo, ai kuwa take aka nemo min magani na sha dan dole ba dan raina ya so ba.
Ana saura sati biyu zai koma school ranar da sassafe Alhaji Baba ya 'kira shi a waya inda yace yazo ya same shi....
Yanayin da yaji muryar Alhaji Baba yayi maganar ya sanya bai 6ata lokaci ba ya iso gidan dan cika umarnin Alhajin.
Bayan sun gaisa cikin sakin fuska sai Alhaji Baba ya tambaye shi cewa " Abinda yaji gaskiya ne ko kuwa, ance wata yarinya na yawan zuwa wancen gidan da kake, wacece ita?" Numfashi Alhaji Baba ya sau'ke tare da cigaba da fa'din " Ni da kaina naga tana shiga gidan rannan ko ba ita bace ke zuwa da farar mota?"
Ya 'karashe maganar yana kallon fuskar Yah Deen domin karantar yanayin sa.
Yah Deen kam zuciyar da 'karfi ta tsinke saboda ka'duwa, cike da firgici ya 'daga idanu ya kalli Alhaji sai kuma ya sake sunkuyar da kansa 'kasa nan take, baya fatan ace Alhaji Baba da kansa ya gansa da Husnah da idanun sa, in hakan ne kuwa ya shiga uku da tarin abin kunya ai.
Hakan da yayi ka'dai sai ya tabbatar wa Alhaji Baba cewa ba zargi ake wa Mu'een ba komai da yaji gaskiya ne....duk da fahimtar hakan da yayi amma sai ya 'kara tambayar sa saboda tabbatar wa duk da ya san da wuya ne Yah Deen 'din ya iya bu'dan baki ya sanar da shi gaskiyar lamari amma ua zama dole ya bincika saboda gano wace iriyar rayuwa yake yi da har mutane ke masa habaicin wai _ko 'dan Alhaji yayi aure ne bamu sani mun sanya albarka ba_ .
Cikin dakiya Yah Deen ya bu'di baki batare da ya iya kallon Alhaji Baba ba yace " Ni...Alhaji...Babu kowa da ke zuwa wuri na".
Wanda ya fa'di hakan ne bayan Alhaji Baba ya maimaita tambayar da yayi masa da farko.
Murmushin takaici Alhaji Baba yayi...yayin da Yah Deen ya ayyana irin yanda zai ci ubana a cikin ransa, tunanin sa gaba 'daya kaina ya tafi dan shi a tunanin sa ni ka'dai nasan ala'kar sa da Husnah sai kuma Imrana, shi kuwa ya san ba zai ta6a zuwa ya sanar da Alhaji wannan zancen ba.
Cikin natsuwa Alhaji Baba yayi masa fa'da ta yadda zai gane abinda yake yi 'din ba dai-dai yake aikatawa ba....inda ya 'karasa da fa'din idan aure yake son yi shi bashi da matsala zai iya yi masa jagora a kowani lokaci ko yau ko gobe sati ko wata a shirye yake kuma zai 'dau nauyin fahimtar da Uncle Ja'afar ma ba abin damuwa bane...Yace ya sanar da shi ko 'yar gidan waye shi zai je ya nema masa auren ta yafi akan a zarge ka da abinda bashi bane ko da baka aikata ba da ciwo balle ma babu mai yadda da kai tunda yarinyar ba muharramar ka bace ita.
Kansa 'kasa yace " Babu komai tsakani na da ita Alhaji ba wani batun aure.."
" Toh me yasa take zuwa gurin ka?"
"...Course mate 'dina ce..abu take zuwa kar6a".
Baya Alhaji Baba ya koma ya jinginu...sam baya son 'dan sa ya fa'da irin wannan rayuwar da jama'ah ke zargin sa da shi ko a mafarki baya son ace shike aikatawa.
Amma saboda baya son ya ja maganar sosai dan ransa 'kara yaci yake yi...ya sanya shi ta'kaita batun da fa'din " Naji...amma Muhammad ka sani.. matu'kar ka kuskura na 'kara ji ko ganin abu makamancin hakan ya faru wallahi duk matakin dana ga dama shi zan 'dauka akan ka sam bazan lamunci rashin 'da'a ba, kana jina ko?"
Da " Erh " ya amsa yana mai jin da'din rashin tsananta bincike da Alhaji bai yi ba.
Yana cikin tunanin hakan yaji Alhaji Baba na fa'din " Tashi ka bani wuri...Allah ubangiji ya shirye ka bisa tafarkin tsira".
Da 'dan hanzari ya bar gaban Alhaji Baba ya nufi wurin Ammi...
Yana shiga parlourn ni kuma sai gani na fito cikin shirin zuwa makaranta ina 'ko'karin dai-dai ta zaman jaka ta ya shigo hankalin Ammi ma duk na kaina.
Muna ha'da ido da shi sai ya wani banka min harara cike da 6acin rai, take sai nayi 'kasa da idanu na bansan me na aikata ba kuma yau 'din da aka tare ni da mugun kallo.
'Karaso wa yayi ya zauna a kujera dake facing Ammi...sai lokacin kuma Ammi ma ta ganshi...kafin tayi magana sai nace da ita " Ammi na tafi".
" Adawo lafiya mama na"
Ta bani amsa amma hankalin ta na kansa.
Sum-sum nayi ficewa ta da yake tun lokacin da ya shigo gidan mun ha'du kuma na gaishe shi a lokacin kuma banga yayi min mugun hali ba, Ammi ce dai basu ha'du ba kawai ya shiga wurin Alhaji.
Ita kam ma sam bata san da cewa yana gidan tun 'dazu ba, bata kuma san da wannan batun ba haka bata san me suka tattauna da Alhaji Baba ba ta dai gansa wani iri sai faman kau da kai yake kamar munafuki, yana gaida ta ko abinci bai tsaya ya ci ba kawai yace da ita ya tafi.
Ammi da idanu ta raka shi har ya 'karasa fita, bata damu ba cuz ta sha ba'kin halin nasa ne yau ya motsa.
Ko da ya koma gida bai iya ya sanar da Husnah cewa kar ta sake zuwa ba kamar yadda aka garga'de shi, ita kuwa yanzu sosai ta jarabtu da shi dan yana yi mata natan, ta kan yawaita shirga wa mahaifiyar ta 'karya n zata guri kaza idan ta fito sai ta nufo wurin Mu'een, sau da dama ma baya sanin zata zo sai dai kawai kwatsam ya ganta ba kuma yace mata me yasa kawai sai su shiga sha'anin su.
Shai'danin bai ta6a complaint akan hakan ba da yake shima 'din baya wuce tayi musamman idan akan Husnah ne.
Haka ranar ya wuni wani iri da shi..bai fita ko'ina ba ko neman abinci bai je yayi ba, Imrana ne ya nemo musu 'dan abin tabawa dangin drinks shima 'din ba wani na kirki ya sha ba ya bari, ko da Husna ta 'kira shi a waya kuwa sama-sama ya amsa ta, wanda jn sa wani iri ya sanya ta tambayar ko lafiya ...baka jin da'di ne? sai yace mata "Erh"
A takaice.
Take ta rikice ta fara yi mai sannu a jere...bai amsa ko 'daya ba kawai ya yanke 'kiran yama kashe wayar tasa gaba 'daya.