← Book details Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 79 OF 211

Sashe 79

Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ni kam baiwar Allah, idanu na 'kur akan connection 'din da yayi da hannu na nawa hannun 'dumi ne da shi yayin da nashi yake sanyi 'kalau, ji nake kamar in wafci hannu na in zura da gidu amma tsoro bazai barni ba, ban kuma san manufar hakan da ya yayi ba sam.

Idan kinga hannu na a cikin nasan abin tausayi, duk yadda nake fallin nafi su Addah Saudah Hasken fata compared to him ba'ka na dawo, idan ina tare da Yah Deen sai dai a 'kira ni da mai choculate skin, hasken sa tas ne shi irin na Ammi ya 'debo, dan shima sosai yafi su Saif hasken fata.

'Dan motsi nayi da hannu na dake cikin nashi sai yayi saurin sake min hannun tare da mi'kewa tsaye bai sake fa'din komai ba har ya juya ya kusa fita daga 'dakin sannan yace " Allah ya sauwa'ka".
Inda yayi maganar ciki-ciki tamkar dole aka sa shi furtawa.

Nima ban ko amsa shi ba kawai na bishi da idanu har bar 'dakin ya maida 'kofar ya rufe.

Da ganin haka kuma sai na maida idanu na kan hannu na da ya ri'ke 'din ina mai jin wani farin ciki na ratsani na ganin bai kashe nin ba, da yake dama fargaba ceke 'kara narkar da ni shiyasa da na ga bai kula ba kawai sai naji wani sanyin da'di har zuciya ta..zakiyi mamaki Hafsat kamar wanda ciwon ya cire min take naji ni garau illah rashin 'karfin jiki.

Kafin washegari kuwa har na warware abina kamar bani ba, Ammi kanta sai da tayi mamaki.

Haka kuwa na cigaba da rayuwa ta cikin kwanciyar hankali..ba na tare da damuwa yanzu dan zuwa ko'ina illah makaranta da Islamiya...ga shi Ma'u ma bata nan balantana ta dame ni...sabuwar rayuwa na fara mai cike da 'yan cin kai da walwala.

〰〰〰
_*Bayan sati biyu.....*_
Zaune muke ni da Ammi tana tsife min kaina sai wayar ta tayi ringing...tana gefe na wayar game na keyi da na gaji na ajiye ta gefe na.
Baki na ta6e da ganin suna mai 'kiran nata, bai jima da barin gidan ba kuma miye na 'kiran waya na fa'di cikin zuciya ta tare mi'ka mata wayar.

" Wa alaikissalam..."
Naji Ammi tace cikin kulawa.
" Ammi akwai wasu kaya na da na bawa Zaidu ya wanke min bai kawo ba tuntuni...na manta kuma 'dazu ban tambaya ba, please ki bayar akawo min".
Daga 'dayan 6angaren aka fadi hakan cikin natsuwa.
Ammi sai tace" Bani da 'dan aike ai ka sani ko?"
Dariya kawai yayi sannan ya yanke 'kiran.

Ammi sai da ta gama min tsifan tana mitar mantuwar karya me yasa da ya tuna bai dawo ya duba ba.

Kusan shu'dewar mintina a'kalla arba'in har mun kammala tsifan ta kame min da ribbom dan nace kitson sai da yamma zanje idan na huta da yake ranar bani da Islamiya.

Muna zaune wayar Ammi ta sake yin 'kara sai ta'ki 'dagawa, sau biyu aka kuma 'kira duk bata 'daga ba, sai da na ukun ya tsinke kafin ta ja tsaki gami da fa'din inyi ha'kuri in kai masa kayan in dawo kafin lokacin zuwa kitson yayi, da taga na canza fuska sai kuma fa'din kar in damu duk abinda ya min idan na dawo in gaya mata tana dai-dai da shi.

Haka de na tashi na wuce na nemo hijab 'dina wani sky blue na sanya ajiki na kafin in fito ma har Ammi ta fito da kayan ta shirya su cikin jakar da kawo su tun ranar da ya bawa Zaidu wankin, haka na 'kar6a na tafi badan raina naso ba na kama hanyar gidan sa ina tafe ina 'ku'k'uni cikin raina, fuska ta ka'dai zaka kalla kasan cewa raina be so aiken ba.

Yah Deen na zaune a parlourn sa yana murmushi shi ka'dai, ba na komai ba sai ni sabon halayyar da Ammi ke yi masa musamman saboda ni, shi har mamakin ta yake yi wasu lokutan yadda ta fifita ni akan kowa, ai ya san babu wanda za'a turo sai ni ne shiyasa Ammi taki 'daga wayar sa...A fili ya saki ajiyar zuciya tare da fa'din" Ko cinye ta zanyi oho".
Yana cikin zancen zuci bazata kawai sai yaji tsayawar mota daga waje, cak ya tsaida hankalin sa tare da sauraren wanda zai shigo, ga mamakin sa kawai sai yaga Husnah ta shigo da fara'ar ta ba tare da tunanin komai ba kawai ta fa'da jikin sa ta rungume shi.

Ko da nazo nayi mamaki da naga mota daga waje amma ban wani damu ba nayi shigewa ta ciki da tunanin 'kila abokansa ne suka zo, duk da nasan ba amsa sallama yake ba amma hakan bai hanani yi ba har sau biyu, sai dai jin ba'a amsa ya sa kawai na cusa kaina cikin parlourn na shiga.

Cak na tsaya daga ba'kin 'kofar ban ko 'karasa sakin labilen dake hannu na ba sakamakon karo da nayi da mugun gani.

Yah Deen da wata mace kan doguwar kujera yana lalumar jikin ta.

Duk basu lura da shigowa ta, 'dan hasken da ya bayyana sakamakon rashin sake labilen da banyi ba ne ya fargar da su inda a tare suka waigo suka dube ni.

Yana gani na sai yayi saurin sakin ta ya dai-dai ta natsuwar sa gami da mi'kewa tsaye, kicin-kicin yayi da fuska sannan yana duba na yace a masifance yace"..Baki iya sallama ba ne ke?"
Ya tambaye ni cikin dakiya yana tunkaro inda nake.
Kaina 'kasa nace " ai nayi ba'a amsa ba..."
"...Shiyasa bazamu ta6a yin shiri da ke ba har abada da shegen sanyin tsiya, da kin yi da 'karfi ai da zanji ki".

Kaina na kara sau'karwa ina fa'din " Allah nayi sallama baku ji ba bane".

Tsaki yaja ni kuwa abin hannu na nayi saurin ajiye sai na fara matsawa baya da niyyar tafiya kafin yace zai ta6a lafiya ta.
Yah Deen sai ya daka min tsawa...cak na tsaya na fara rawar jiki.
Sai da ya iso gaba na ya tsaya sannan ya 'dan rage sautin muryar sa yace " Saura inji a wani wuri kinsan hali na ai, da wu'ka zan yanka ki".

Ni kam ma ina ruwa na, har cikin raina ni banga abin bada labari anan ba....sai dai sosai abin ya tsaye min araina na kasa mantawa da shi...wannan karan kashedin sa bai wani tsorata ni ba saboda nasan ba ma fa'dan zanyi ba balle har ta kai shi ga yanka ni.

Haka na juya na koma gida amma duk kotsi na abin na raina, sosai kuwa nayi jarumtar 6oyewa Ammi halin da nake ciki koda ta tambaye ni abinda ya min ma da 'karfin gwiwa ta nace mata ba abinda ya min yau kam.
" Kar fa ki 6oye min..idan na bincika naji wani abu kinsan harda ke zan zane ko?"
" Allah Ammi ba komai".
Na bata amsa da 'kwarin gwiwa ta.

'Bangaren sa kuwa tun fita ta ya kasa ta6uka komai, gaba 'daya 'kunci ya cika zuciyar sa ya cunkushe, duk wani yanayin jinda'din da yake jin sa mintina 'kalilan da suka gaba ta dun sun dakushe, zaune kawai yayi kan 1seater ya sar'ke hannun sa cikin juna ransa a matu'kar 6ace..damuwar sa ni...what if naje na sanar da Ammi abinda naga yana aikatawa.

Husnah kam bata damu ba duk da tayi zaton sister din sa ce ni, amma duk da hakan ganin nawa bai sa taji ta ha'kura da abinda ya kawo ta ba, sai dai duk yadda taso Yah Deen ya kwantar da hankalin sa su farantawa juna abin ya faskara, daga 'karshe ma da masifa suka rabu ya kora ta.

Hankalin sa yazo ya 'dan kwanta ne ganin har anyi kwanaki uku bai ga wani canji daga iyayen sa ba, wanda hakan ne yasa shi fahimtar ban sanar da su ba, tun daga lokacin ya sami natsuwa sai dai bai gushe ba a kullum yana sake Addu'ar Allah ya mantar da ni yasa kar na sake tunawa balle har inyi gigin bada labari.

Ni kuwa 6angare na ko 'kaunar sake jin muryar sa bana yi yanzu balle ganin sa...haka har ranar komawar sa tayi tun ganin sa da nayi da Husnah har zuwa ranar tafiyar tasa ban 'kara sashi cikin idanu na ba...ko ranar ma ina school ya tafi bamu ha'du dashi ba.

Tafiyar sa kuwa yafi komai yi min da'di a rayuwa ta, daga ranar da na san ya tafi shikenan na saki jiki na amma a kullum abinda na gani 'din nan baya barin kaina na kasa cire shi araina sam.

Bayan tafiyar tasa ne Imrana ya je gurin Mahaifin Ma'u da gaske wai shi son ta yake yi kuma da aure, amma mahaifin Ma'u sai yace da shi ya riga yayi mata miji tuntuni dan haka yayi ha'kuri, duk da lokacin babu wanda aka bawa auren Ma'u, amma dole a shekarun san nan badan yaso ba dan dole ya zame masa ya shirga 'karya, badan komai ba sai dan kawai ya tseratar da mutuncin 'yar sa ga fa'dawa lalataccen hannu...cuz yasan fa'dar hakan kawai shine katangar da zai iya ginawa tsakanin Imrana da Ma'u.

Ashe Imrana yaji haushin wannan maganar sosai, dan haka cikin ransa ya ku'duri aniyar 6atawa mahaifin Ma'u rai fiye da yanda yayi masa akan Ma'u, kafin yazo ai sai da ya bincika ya tabbatar ba wani a'kasa da zai kawo kasa tsaiko, ko Deeni da tace tana so bai damu bane dan yasan Deeni ba zai so irin ta ba dan shi 'dan gayu ne na 'karshe...amma bakomai " Zanyi maganin ka 'dan tsoho". 'Karshen abinda Imrana ya 'kudurta cikin ransa kenan kafin ya bar wurin mahaifin Ma'u.

Da wannan damar Imrana yayi amfani tun kafin Yah Deen ya dawo ya dinga shigar masa da Ma'u, shi da kansa ya dinga bayyana masa irin soyayyar da take yi masa tare da yawaita siffanta masa ita ya ringa 'kawata masa halittar ta, tun Yah Deen baya damuwa har yazo ya fara ri'ke zancen ta cikin ransa, bawai dan yana son ta ba a'a kawai dan yawan zancen ta da Imrana ke yawaita yi masa.
Chapter 79 · 0% Book details