Sashe 32
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Taheer baya so yaja da maganar Alhajin amma sai yake ganin kamar ai kyautar tayi yawa sosai Mu'een 'din ma nawa yake da har zaa yi masa irin wannan kyautar amma dole haka ya ha'kura da maganar ganin 'korafin sa bai samu shiga ba, domin Alhajin ba sauraran sa zai yi ba ga dukkan alamu.
Shi haka tsarin sa baya son ayi masa godiya sam koda yayima kyauta baya son yawan godiya shiyasa wa'danda suka san halin sa idan hakan ya faru kawai sai su bishi da addu'o'i cikin ransu.
Shima 'din yafi gane hakan....dan haka shima Taheer sai ya ja bakin sa yayi shiru gami da jinjinawa karamci irin na mutumin tamkar ba 'kabila ba haka yake rayuwar sa.
*****
Alhaji da Mu'een yaji 'kannan mahaifiyar sa na kiran Baban sa da shi ne ya sanya shima ya 'kara Alhaji kan sunan da yake kiran sa da shi wato daga Baba zuwa Alhaji Baba.
Babu kuwa wanda ya hana sa har hakan ya zauna bakin sa abu kadan sai yace Alhaji Baba...Alhaji Baba.
Kwanci tashi rayuwa babu wuya.... har Mu'een ya shekara biyar da haihuwa, yaro kakkykyawa da shi abin so da birgewa.. yayin da yana 'kara girma kywaun sa na 'kara yawai ta.....sai dai kuma har a lokacin ba'a sanya shi makaranta ba haka rayuwar sa ta kasance yau yana gun iyayen sa gobe yana gidan kakan sa, sosai yake samun *gatan kowa* daga cikin su, har da ma Uncle 'din sa dake Azare shima ba'a barshi abaya ba.
Wani zuwa da Ja'afar yayi ne ya kai musu ziyara sai ya dinga masifar me yasa ba'a sanya shi makaranta ba, yanda yake yi 'din idan kun ganshi har zaku zaci cewa ko shine babba, sosai ya nuna musu rashin dacewar hakan, su kansu ma sunsan ba dai-dai suka yi ba kuma bama su da dalilin 'kin sashi a makarantar amma kawai hakan bai zo kansu bane shiyasa, zuwan Ja'afar 'din ne sai ya fargar dasu, musamman da yace idan ba su so shi zai 'dauke sa ya tafi dashi.
Kowa bai so yayi missing yaron dan haka cikin satin suka 'dauri aniyar kaishi makaranta.
Ashe ma basu sani ba Kakan sa ya gama masa komai, shima daya gaji da jiran ganin sun sanya shi yaga shiru shine kawai ya nema masa makarantar da ta dace da kansa batare da ya shawarci kowa daga cikin su ba.
Monday da suke tunanin zasu fara yi masa cuku-cukun makarantar, aranar da sassafe Alhaji ya aiko driver aka 'dauke shi
sai dawo musu yayi da uniform a jikin sa yazama d'an makaranta.
Tun daga ranar Mu'een yaci gaba da zuwa makarantar, wata tsadaddiya da kakan sa ya sanya shi.
Sosai suka ji da'din hakan a lokacin.....Aishatu ce da kanta ta 'kira mahaifin nata tayi masa godiya amma bai ma tankata ba kawai ya kashe wayar.
Bayan ya gama da layin Mu' een sai hankalin sa ya dawo kan processing wa yaran sa tasu makarantar domin suk sun gama secondary school yana so su cigaba.
A Canada ya samar musu dukkan su Umar da Aliyu.. inda suka tafi cikin matu'kar farin ciki suka bar mahaifin nasu da kewa sosai domin gida yayi shiru babu kowa, shima 'din kawai sai ya wuce South Africa inda ya tafi domin gudanar da harkokin *Kasuwancin sa* na can.
Bai dawo ba sai da ya tabbatar su Aliyu zasu dawo hutu kafin nan shima ya dawo, su kam ma ba haka suka so ba domin can suka so zuwa su same shi amma yace kawai su ha'du agida domin shima akwai abinda zai kawo sa.
Ranar da suka dawo Taheer, Mu'een da mahaifiyar sa duk a gidan suka yini sai yamma kafin suka koma gidan su....inda anan Umar ya ce abar musu shi mana su 'dan kara gaisuwa, take Aishatu tace a'a sai dai ya dawo gobe domin basu zo da kayan sa ba, kuma ma kar ya dame su daga sau'kan su gara idan sun 'dan huta sai akawo shi.
Da haka suka yi sallama suka koma gidan su.
Kwatsam tashin farko Taheer ya tsinci kansa a matsayin Assistant Manager na gidan man Oando dake nan cikin garin na Kano.
Wannan abin shi yafi komai yi musu da'di a rayuwar su baya ga haihuwar Mu'een, domin kuwa hakan shine ya kasance silar bun'kasuwan arzi'kin su suma suka zama abin kwatance.
Kunsan abu idan Allah ya dafa maka toh shikenan baka da matsalar komai domin babu wanda ya isa ya sha gaban ka face Allah ya kautar maka da shi.
Mahaifin Aishatu ne yayi masa hanyar hakan batare da sun sani ba dukkan su.....da yake mahaifin nata babban mutun ne mai fada aji....sai dai kuma bayan hakan bai yi wani tsawon rai ba ya koma ga mahallicin sa da dukkan sauran yaran sa biyu da suka zo hutu wato Aliyu da Umar.
Hatsarin mota suka yi akan hanyar su ta zuwa duba wani plot da ya siya zai kaisu ya nuna musu sai hakan bai faru ba, domin kuwa basu kaiga zuwa wurin filin ba ma motar su ta kife da su inda nan take biyu suka rasu, Umar kuwa a asbiti ya 'karasa da kalmar shahada abakin sa.
Wannan mutuwar itace ta kasance babban tashin hankalin su domin Aishatu gaba 'daya kasa nutsuwa tayi.... banda suma babu abinda take yi....shi kansa Taheer yaji mutuwar sosai wanda sai bayan mutuwar ne ma ya samu labarin halaccin da dattijo sirikin nasa yayi masa na canza masa wurin aiki tare da sawa a 'kara masa babban matsayi batare da ya sani ba.
Banda addu'ah babu abinda yake bin sa da shi domin dattijon iyamurin mutum ne mai mutu'kar dattako da halin girma sai fatan Allah yayi wa Alhaji Muhammad Ugoh Chukwu da iyalan sa rahama Ameen .
Hatta Mu'een da yake 'dan shekaru shida ma a lokacin sai da ya fahimci gidan nasu ba dai-dai yake ba, domin shima sosai ya rasa kulawar uwar sa, duk wani kulawar da ta dace ya samu daga gareta to baya samun sa.
Mahaifin sa ne ke 'ko'karin yi masa wa'dan su hidimomin da kansa, ga kuma aikin sa da yake yi, ganin hakan bazai fishshe su bane ya sanya shi nemo wata da zata ringa kulawa da yaron da kuma yi musu abinci.
Hutu ya bawa Aishatu sosai cuz ya san ko shine irin wannan mutuwar ta riske shi dole sai yaji babu da'di balle ita da take matsayin mace mai rauni.
*****
Haka rayuwar su ta cigaba da tafiya ba yabo ba fallasa, har akayi kwana arba'in da rasuwar, kafin hakan kuwa idan kun ga yanda Aishatu ta rame ta lalace abin har zai bawa mutun tsoro, sosai ta zabge ta fita hayyacin ta...ga uban low BP da ya sako ta agaba tun da 'kuruciyar ta...tana nan yau lafiya gobe babu.
Bayan arba'in ne lawyern mahaifin ta yazo da niyyar ya dan'ka mata dukkanin takaddun k'adarorin mahaifin ta harda ma wa'danda bata sani ba....bai wani dame ta ba balle ya d'aga mata hankali domin kyakkyawan nutsuwan ta ma lawyern bai samu ba, Taheer ne ya jagoranci lamarin inda ya kar6a mata wasu yayin da ya dan'ka wasu a hannun lawyern akan ya cigaba da kula mata dasu.
Abubuwa da yawa na mahaifin ta da basu san da shi ba, anan Kano harda ma can South Africa cikin su kuwa babu wanda ya bibiyi lamarin duk kuwa da cewa sun san yana da cibiyar kasuwanci acan, abinda yake gaban su ma ka'dai ya ishe su, domin shi Taheer a yanzu bashi da wani burin da ya wuce yaga matarsa ta warware amma abin ya faskara, tsawon wata uku da rasuwar amma ta kasa ha'kuri da rashin su.
Hatta Mu'een sai da ta koya masa tagumi da rashin son magana, cuz idan yaga tayi shiru tana tunani shima sai yaje gefen ta ya zauna yayi tagumi yana kallon ta, koda taga hakan bata tanka shi, idan kuwa yaga tana hawaye shima kukan yake yi....idan ta ga hakane sai ta rungumo shi zuwa jikin ta su cigaba da kukan tare.
Abin sosai yake ta6a masa zuciya domin ba 'karamin damun sa arai yake yi ba, amma ya rasa yadda zai yi, kullum yana ko'karin ganin ya nuna mata muhimmancin yadda da kaddara matsayin ta na musulma amma a banza kamar bada ita yake ba, ganin kamar yanayin yaron sa na son canza salo irin nata ne ya sanya shi dogon nazari, domin kuwa Mu'een surutaccen yaro ne amma tunda ya fara ganin mahaifiyar sa na yawan kuka shima ya zama shiru-shirun 'karfi da yaji, domin kuwa wani lokacin har mantawa zakayi cewa cikin gidan akwai yaro 'karami...tun farkon rasuwar yayi nacin tambayar su Granny, Uncle Umar da Uncle Aliyu yayi ta rigimar akai sa wurin su kullum amma rashin samun gamsasshiyar amsa daga bakin iyayen nasa ne ya sanya shi yau da gobe ya ha'kura shima duk kuwa da cewar ba wai ya manta dasu bane....tafiyar da ake ce masa sunyi ne ya sanya shi koma cewa " yaushe zasu dawo?".
Hakan ma ba amsa mai kyau yake samu ba amma dai duk da haka baya gajiya da yin tambayar.
Ita Aishatu idan ya tambaye ta sai dai tayi ta masa kuka, a wurin mahaifin sa ka'dai yake samun amsar " baza su dawo ba Mu'een mune zamuje mu tarar da su"
Take sai yace
" To Alhaji Baba mu 'din yaushe zamuje da Ammee na?"
Idan yaron ya fa'di haka sai kawai Taheer yayi murmushi ya shafa kansa yace koda wani lokaci Babana, tafiyar ba'a mata shiri kaji".
Sai ya 'dage kansa da nufin yaji.
Sosai jikin Taheer yake yin sanyi aduk lokacin da sukayi irin haka da Mu'een.
A hankali ma sai Allah ya taimake shi yaron ya rage tambayar sa sai dai kuma shiru-shirun nasa sam baya jin da'din sa.
Hutu ya shirya musu zuwa a Dubai... wai ko zasu d'an nutsu idan sun kauce duk kuwa da cewa ya kasa rabata da zubda hawaye da tunani amma sosai yake iya matu'kar 'ko'karin sa akan hakan.
Shi haka tsarin sa baya son ayi masa godiya sam koda yayima kyauta baya son yawan godiya shiyasa wa'danda suka san halin sa idan hakan ya faru kawai sai su bishi da addu'o'i cikin ransu.
Shima 'din yafi gane hakan....dan haka shima Taheer sai ya ja bakin sa yayi shiru gami da jinjinawa karamci irin na mutumin tamkar ba 'kabila ba haka yake rayuwar sa.
*****
Alhaji da Mu'een yaji 'kannan mahaifiyar sa na kiran Baban sa da shi ne ya sanya shima ya 'kara Alhaji kan sunan da yake kiran sa da shi wato daga Baba zuwa Alhaji Baba.
Babu kuwa wanda ya hana sa har hakan ya zauna bakin sa abu kadan sai yace Alhaji Baba...Alhaji Baba.
Kwanci tashi rayuwa babu wuya.... har Mu'een ya shekara biyar da haihuwa, yaro kakkykyawa da shi abin so da birgewa.. yayin da yana 'kara girma kywaun sa na 'kara yawai ta.....sai dai kuma har a lokacin ba'a sanya shi makaranta ba haka rayuwar sa ta kasance yau yana gun iyayen sa gobe yana gidan kakan sa, sosai yake samun *gatan kowa* daga cikin su, har da ma Uncle 'din sa dake Azare shima ba'a barshi abaya ba.
Wani zuwa da Ja'afar yayi ne ya kai musu ziyara sai ya dinga masifar me yasa ba'a sanya shi makaranta ba, yanda yake yi 'din idan kun ganshi har zaku zaci cewa ko shine babba, sosai ya nuna musu rashin dacewar hakan, su kansu ma sunsan ba dai-dai suka yi ba kuma bama su da dalilin 'kin sashi a makarantar amma kawai hakan bai zo kansu bane shiyasa, zuwan Ja'afar 'din ne sai ya fargar dasu, musamman da yace idan ba su so shi zai 'dauke sa ya tafi dashi.
Kowa bai so yayi missing yaron dan haka cikin satin suka 'dauri aniyar kaishi makaranta.
Ashe ma basu sani ba Kakan sa ya gama masa komai, shima daya gaji da jiran ganin sun sanya shi yaga shiru shine kawai ya nema masa makarantar da ta dace da kansa batare da ya shawarci kowa daga cikin su ba.
Monday da suke tunanin zasu fara yi masa cuku-cukun makarantar, aranar da sassafe Alhaji ya aiko driver aka 'dauke shi
sai dawo musu yayi da uniform a jikin sa yazama d'an makaranta.
Tun daga ranar Mu'een yaci gaba da zuwa makarantar, wata tsadaddiya da kakan sa ya sanya shi.
Sosai suka ji da'din hakan a lokacin.....Aishatu ce da kanta ta 'kira mahaifin nata tayi masa godiya amma bai ma tankata ba kawai ya kashe wayar.
Bayan ya gama da layin Mu' een sai hankalin sa ya dawo kan processing wa yaran sa tasu makarantar domin suk sun gama secondary school yana so su cigaba.
A Canada ya samar musu dukkan su Umar da Aliyu.. inda suka tafi cikin matu'kar farin ciki suka bar mahaifin nasu da kewa sosai domin gida yayi shiru babu kowa, shima 'din kawai sai ya wuce South Africa inda ya tafi domin gudanar da harkokin *Kasuwancin sa* na can.
Bai dawo ba sai da ya tabbatar su Aliyu zasu dawo hutu kafin nan shima ya dawo, su kam ma ba haka suka so ba domin can suka so zuwa su same shi amma yace kawai su ha'du agida domin shima akwai abinda zai kawo sa.
Ranar da suka dawo Taheer, Mu'een da mahaifiyar sa duk a gidan suka yini sai yamma kafin suka koma gidan su....inda anan Umar ya ce abar musu shi mana su 'dan kara gaisuwa, take Aishatu tace a'a sai dai ya dawo gobe domin basu zo da kayan sa ba, kuma ma kar ya dame su daga sau'kan su gara idan sun 'dan huta sai akawo shi.
Da haka suka yi sallama suka koma gidan su.
Kwatsam tashin farko Taheer ya tsinci kansa a matsayin Assistant Manager na gidan man Oando dake nan cikin garin na Kano.
Wannan abin shi yafi komai yi musu da'di a rayuwar su baya ga haihuwar Mu'een, domin kuwa hakan shine ya kasance silar bun'kasuwan arzi'kin su suma suka zama abin kwatance.
Kunsan abu idan Allah ya dafa maka toh shikenan baka da matsalar komai domin babu wanda ya isa ya sha gaban ka face Allah ya kautar maka da shi.
Mahaifin Aishatu ne yayi masa hanyar hakan batare da sun sani ba dukkan su.....da yake mahaifin nata babban mutun ne mai fada aji....sai dai kuma bayan hakan bai yi wani tsawon rai ba ya koma ga mahallicin sa da dukkan sauran yaran sa biyu da suka zo hutu wato Aliyu da Umar.
Hatsarin mota suka yi akan hanyar su ta zuwa duba wani plot da ya siya zai kaisu ya nuna musu sai hakan bai faru ba, domin kuwa basu kaiga zuwa wurin filin ba ma motar su ta kife da su inda nan take biyu suka rasu, Umar kuwa a asbiti ya 'karasa da kalmar shahada abakin sa.
Wannan mutuwar itace ta kasance babban tashin hankalin su domin Aishatu gaba 'daya kasa nutsuwa tayi.... banda suma babu abinda take yi....shi kansa Taheer yaji mutuwar sosai wanda sai bayan mutuwar ne ma ya samu labarin halaccin da dattijo sirikin nasa yayi masa na canza masa wurin aiki tare da sawa a 'kara masa babban matsayi batare da ya sani ba.
Banda addu'ah babu abinda yake bin sa da shi domin dattijon iyamurin mutum ne mai mutu'kar dattako da halin girma sai fatan Allah yayi wa Alhaji Muhammad Ugoh Chukwu da iyalan sa rahama Ameen .
Hatta Mu'een da yake 'dan shekaru shida ma a lokacin sai da ya fahimci gidan nasu ba dai-dai yake ba, domin shima sosai ya rasa kulawar uwar sa, duk wani kulawar da ta dace ya samu daga gareta to baya samun sa.
Mahaifin sa ne ke 'ko'karin yi masa wa'dan su hidimomin da kansa, ga kuma aikin sa da yake yi, ganin hakan bazai fishshe su bane ya sanya shi nemo wata da zata ringa kulawa da yaron da kuma yi musu abinci.
Hutu ya bawa Aishatu sosai cuz ya san ko shine irin wannan mutuwar ta riske shi dole sai yaji babu da'di balle ita da take matsayin mace mai rauni.
*****
Haka rayuwar su ta cigaba da tafiya ba yabo ba fallasa, har akayi kwana arba'in da rasuwar, kafin hakan kuwa idan kun ga yanda Aishatu ta rame ta lalace abin har zai bawa mutun tsoro, sosai ta zabge ta fita hayyacin ta...ga uban low BP da ya sako ta agaba tun da 'kuruciyar ta...tana nan yau lafiya gobe babu.
Bayan arba'in ne lawyern mahaifin ta yazo da niyyar ya dan'ka mata dukkanin takaddun k'adarorin mahaifin ta harda ma wa'danda bata sani ba....bai wani dame ta ba balle ya d'aga mata hankali domin kyakkyawan nutsuwan ta ma lawyern bai samu ba, Taheer ne ya jagoranci lamarin inda ya kar6a mata wasu yayin da ya dan'ka wasu a hannun lawyern akan ya cigaba da kula mata dasu.
Abubuwa da yawa na mahaifin ta da basu san da shi ba, anan Kano harda ma can South Africa cikin su kuwa babu wanda ya bibiyi lamarin duk kuwa da cewa sun san yana da cibiyar kasuwanci acan, abinda yake gaban su ma ka'dai ya ishe su, domin shi Taheer a yanzu bashi da wani burin da ya wuce yaga matarsa ta warware amma abin ya faskara, tsawon wata uku da rasuwar amma ta kasa ha'kuri da rashin su.
Hatta Mu'een sai da ta koya masa tagumi da rashin son magana, cuz idan yaga tayi shiru tana tunani shima sai yaje gefen ta ya zauna yayi tagumi yana kallon ta, koda taga hakan bata tanka shi, idan kuwa yaga tana hawaye shima kukan yake yi....idan ta ga hakane sai ta rungumo shi zuwa jikin ta su cigaba da kukan tare.
Abin sosai yake ta6a masa zuciya domin ba 'karamin damun sa arai yake yi ba, amma ya rasa yadda zai yi, kullum yana ko'karin ganin ya nuna mata muhimmancin yadda da kaddara matsayin ta na musulma amma a banza kamar bada ita yake ba, ganin kamar yanayin yaron sa na son canza salo irin nata ne ya sanya shi dogon nazari, domin kuwa Mu'een surutaccen yaro ne amma tunda ya fara ganin mahaifiyar sa na yawan kuka shima ya zama shiru-shirun 'karfi da yaji, domin kuwa wani lokacin har mantawa zakayi cewa cikin gidan akwai yaro 'karami...tun farkon rasuwar yayi nacin tambayar su Granny, Uncle Umar da Uncle Aliyu yayi ta rigimar akai sa wurin su kullum amma rashin samun gamsasshiyar amsa daga bakin iyayen nasa ne ya sanya shi yau da gobe ya ha'kura shima duk kuwa da cewar ba wai ya manta dasu bane....tafiyar da ake ce masa sunyi ne ya sanya shi koma cewa " yaushe zasu dawo?".
Hakan ma ba amsa mai kyau yake samu ba amma dai duk da haka baya gajiya da yin tambayar.
Ita Aishatu idan ya tambaye ta sai dai tayi ta masa kuka, a wurin mahaifin sa ka'dai yake samun amsar " baza su dawo ba Mu'een mune zamuje mu tarar da su"
Take sai yace
" To Alhaji Baba mu 'din yaushe zamuje da Ammee na?"
Idan yaron ya fa'di haka sai kawai Taheer yayi murmushi ya shafa kansa yace koda wani lokaci Babana, tafiyar ba'a mata shiri kaji".
Sai ya 'dage kansa da nufin yaji.
Sosai jikin Taheer yake yin sanyi aduk lokacin da sukayi irin haka da Mu'een.
A hankali ma sai Allah ya taimake shi yaron ya rage tambayar sa sai dai kuma shiru-shirun nasa sam baya jin da'din sa.
Hutu ya shirya musu zuwa a Dubai... wai ko zasu d'an nutsu idan sun kauce duk kuwa da cewa ya kasa rabata da zubda hawaye da tunani amma sosai yake iya matu'kar 'ko'karin sa akan hakan.