Sashe 114
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
" Kamar yaya?"
Ammi ta sake tambaya cike da mamaki tana duban sa
Sai yace " Kamar yadda kika sani".
" Nifa na kasa ganewa Mu'een ce min yayi wai an fasa auren yanzu kuma ga ka kana cemin wai amaryar na gida".
" Yana saka jallabiya yace mata" To be frank Aisha..auren Muhammad bai yiyu da wancen yarinyar ba dan wan mahaifinta yaci amanar mu..muna zaune a wurin ya 'daure auren 'yar sa da wani daban bacin ya san shi muke zaman jira...sai daga baya ne ma Ja'afar ke sanar dani ashe wai shi wanda ya 'daurawa auren 'dan sa ne na cikin sa..kinga an nuna mana bambanci a zahiri.
...ran kowa da muke tare sai da ya 6aci a wurin hakan yasa Mahaifin Hudah yace tunda muka zo har Azare da niyyar aure to baza'a fasa ba...yace s 'daura auren kawai da Hudah ya bashi ita...na so in nuna 'kin amincewa amma yace matu'kar na nuna bana do to azahiri na nuna masa 'kyama matsayin sa na talaka...dole naja baki na nayi shiru na wakilci amarya Ja'afar kuma ya kar6awa Mu'een gudun maganar da zai biyo baya, yanzu dai Hudah 'yar ki da kike tsananin so marsayin mata take a wurin 'dan ki Muhammad..."
Ya 'karashe yana 'yar dariya.
Ammi kam rasa abinda zata ce da shi tayi saboda farin ciki..ita kanta ta fahimci jin da'din Alhaji Baba kan wannan auren...to inaga ita da ta jima da son ganin faruwar hakan duk da bata furta ba amma ya da'de cikin zuciyar ta.
Maganar Alhaji Baba ne ya katse mata tunanin ta inda yace" Sai dai bazan bashi Hudah ba har sai na tabbatar da cewa halin sa mai kyau ne , zargin da nake yi masa abaya idan ya kasance ba gaskiya ba ne sannan zan bashi Hudah matsayin mata dan bana so ya lalatawa yarin farin cikin ta da gur6ataccen tunani..matu'kar na tabbatar da zargi na akan sa wallahi da kaina zan sa ya rabu da ita in aura mata wani daban..dan haka a yanzu ko sanin cewa itace matar sa bana so yayi harda itama...ke de kawai ki 'kara kulawa da rayuwar ta ki tabbatar babu wanda ke shiga rayuwar ta tunda yanzu da aure akanta, batun zuwa gida kuma gobe da safe zan sa akaita ta gaida mahaifin nata 'kila ma a goben...zai koma".
Ammi kam ji tayi kamar ta taka rawa saboda tsananin farin ciki...ba ta iya ri'ke maganar ba sai da ta sanar da Anty Zee a daren ranar..ga mamakin ta kuwa sai taga farin cikin da Anty Zainab ta shiga har yaso ya zarta nata ma.
Sam hakan bai sa Ammi mamaki ba cuz tasan irin 'kaunar da Anty Zainab ke wa Mu'een, in sha'kuwa ce kuwa ko ita da ta haife shi baza ta ce tafi ta sha'kuwa da shi ba saboda a gaban ta ya tashi..so fiye da haka ma idan ta gani daga Anty Zainab bazai sa ta mamaki ba.
Itama Anty Zainab Uncle Ja'afar ta 'kira a waya tace dashi gaskiya bai kyauta mata ba da har ya 6oye mata wannan maganar.
Sai yace" Tunda yanzu kinji ai shikenan".
Ita ka'dai tasan me take ji cikin ranta...Alhamdulillah kawai take ta maimaitawa, cuz tafi kowa 'kaunar ganin Mu'een 'din ya samu mata irin Hudah sai gashi Allah ya cika mara burin ta cikin sau'ki, badan Ammi ta gaya mata abinda Alhaji Baba yace game da batun ba da gobe sai ta ha'da sabuwar gagarumar walima na farin ciki dan ta nuna godiyar ta ga mahalicci.
Washe gari sunday..kamar yadda Alhaji yayi al'kawari kuwa hakan ne ya faru..cuz wani yaron sa ya sa ya kaini gidan mu dan gaida mahaifi na, anan na tarar da shi ma yana kan shirin tafiya, ban fahimci komai ba duk kuwa da cewa naga anata nan nan dani sannan Baban mu yayi min doguwar nasiha cikin natsuwa kan ha'kuri tamkar wanda ganawar mu da shi kenan ta 'karshe har yasa jiki na yayi sanyi.
Ko da wasa babu wanda yace min an 'daura min aure duk kuwa da cewa duk sun sani, ban sani ba ashe duk Alhaji Baba ya ro'ki da kar a fa'di min har sai yaga abinda hali yayi.
Abu 'daya na fahimta kawai canji daga wurin ahali na, yanda ake bani wani daraja da kaffa-kaffa dani abin ya 'daure min kai sosai, sai dai ban kawo batun aure ba sam ko a tunani na, na dai yi tunanin girman da na 'kara ne ya sa ake min hakan dan haka naji Anty Zainab ta fa'di lokacin da zan taho.
Turare wannan hanani amfani tayi da asalin nawa ta bani wasu marasa 'kamshi sosai wai ai na girma yanzu so in dinga kula da komai na rayuwa ta.
ko da nace zanje gidan su Binta ma Ummah ta hanani tayi, ko gidan Anty saudahn mu banje ba Ummah ta ta ri'ke ni a gida tace wai in bari sai wani lokacin kawai.
Ban fi 3hrs ba a gidan aka dawo 'dauka ta...haka na shiga mota ina tuttura baki na gaba da mitar ni banganewa wannan sabuwar tsarin ba duk an bi an takura ni.
Da isata gida kuwa na tari Ammi da mitan Ummah ta bata barni naje ko'ina ba, ko gidan Addah ta banje ba da gidan su Binta...kafin in kai 'karshen magana ta kuwa sai ga hawaye ya gangaro min.
Ammi rasa abinda zata ce da ni tayi kawai sai ta jawo jikin ta ta hau lallashi na, cikin hakan dmtake ce dani kar in da mu wataran ai zanje...nace" Ammi kinga ma fa Ma'u tace min zata zo bikin Yah Deen kuma bata zo ba bansan me yasa ba kuma ban je na duba ta ba duk Ummah ta ta hana ni".
" Rabu da ita ai zata zo may be bata samu daman zuwa bane kawai".
Anty Zee na ganin yanda nake yiwa Ammi kuka sai ta janyo ni ta ringa bani misalai tana jan hankali na da da'da'dan kalamai take fa'din duk mace mai aji ai bata yawan yawo komin ta bisa tsari take yin sa ba wai ta ringa shige-shige ko'ina kamar akuyar da babu 'dauri ba.
Ni dai kawai jin ta nayi ba wai dan na fahimci me take nufi ba.
Ranar kuwa gida ya watse kaf kowa ya koma inda ya fito, ko abokan Yah Deen ma ranar duk suka koma dan daga gida da suka gaida su Alhaji sai suka wuce bayan ya sallame su, aka bar shi shi ka'dai sai Imrana kamar da can.
Yah Deen ranar bai je ko'ina ba dan haushin an hana shi tafiya bacin ba komai yake yi a gidan ba, haka ya yini a wuri 'daya illah Imrana da ke faman shiga yana fita...cikin kwanciyar hankali abin sa.
Uncle J ma da sassafen ranar ya koma Taraba Anty Zee kuwa ba yanzu ba sai daga baya zata koma dan sai ta 'dan kwana biyu a Azare ma tukunna kafin ta tafi, gida ya zama shiru babu da'di..lalle jama'ah rahama.
Haka inaji ina gani aka takurani da zaman gida, illah makaranta da nake zuwa...kuma ko makarantar ma ban ganin Ma'u, gashi su Ammi sun hanani yawo balle inje gidan su in dubo ta...
Sai da aka yi kwana biyar da bikin Yah Deem kafin Ma'u tafara fitowa makaranta...nan na isheta da tambayar me yasa bata zo bikin Yah Deen ba?"
Tace min" bikin da aka ce an fasa 'din?"
Nace" Erh amma ai de mutane sun taru kowa yazo nayi ta duba ki bangan ki ba...".
Tace" Banda lafiya ne shiyasa banzo ba".
Sai nace
" To waye yace miki an fasa kuma ?"
" Imrana".
Ta bani amsa a takaice.
Sai nace
" Ayyah ai naso in zo gidan na ku amma an hanani yawo yanzu shiyasa banzo ba".
Shiru tayi bata sake kulani ba.
One thing da na fahimta game da Ma'u yanzu sam bata son yawan surutu sosai sai dai ban san dalili ba dan haka nima sai nayi shiru ko mun ha'du a makaranta ko Islamiya hirar mu ka'dan ce da ita da yake ma ba kullum take zuwa ba sai jifa-jifa...amma duk ta natsu ta daina rawar kai yanzu (ban sani ba ashe Yah Deen ne ya koya mata hankali).
_Comment_
_Vote_
_Share_
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
_*Daga marubuciyar Littafin CAPTAIN ABBAS*_
_Nagode sosai masoya Allah ya bar min ku..._
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *55*
Hisham yazo gida kamar yadda mahaifiyar sa ta bu'kata sunyi magana kuma ya fahimce ta, musamman ma da yaji cewar an riga da an aura masa Husnah, jin hakan ya matu'kar faranta ransa har ma ya kasa 6oye farin cikin sa, bakomai bane kuma yasa hakan face tsananin soyayyar da yake yi mata, shiyasa ma ko guda daga cikin sharu'd'dan da mahaifiyar sa ta gindaya masa akan Husnahn bai yi jayayya da shi ba.
Zuciyar sa 'daya ya 'daukan mata al'kawarin kulawa da Husnah da kuma sau'ke duk wani hakkin ta da ya rataya akan sa, ya kuma yi al'kawarin bata kariya iya iyawar sa, duk da Hajiya Kareema bata fito fili ta bayyana masa asalin meke tafiya ba amma tayi 'ko'karin ganin ta nuna masa daraja da muhimmancin da Husnan ke da shi a wurin sa...wanda bayaga aure akwai kyakykyawar dangantaka tsakani wanda shi kansa ya sani.
Ko da ya isa ga mahaifin sa ma ba wani ba'kon al'amari yaji daga bakin sa ba wanda zai rikita shi, bambancin kawai shine shi bai yi masa maganar ta fuskar fahimta ba, ya dai ce da shi yayi masa aure da Husnah and kuma yana fatan zai masa biyayya bisa hakan.
Hisham bai wani damu ba dan ya riga ya san wace Husnah, kuma sun riga sun gama magana da mahaifiyar sa kafin nan so hankalin sa kwance ya bar gaban mahaifin sa da 6oyayyen farin cikin sa a zuci.
Ammi ta sake tambaya cike da mamaki tana duban sa
Sai yace " Kamar yadda kika sani".
" Nifa na kasa ganewa Mu'een ce min yayi wai an fasa auren yanzu kuma ga ka kana cemin wai amaryar na gida".
" Yana saka jallabiya yace mata" To be frank Aisha..auren Muhammad bai yiyu da wancen yarinyar ba dan wan mahaifinta yaci amanar mu..muna zaune a wurin ya 'daure auren 'yar sa da wani daban bacin ya san shi muke zaman jira...sai daga baya ne ma Ja'afar ke sanar dani ashe wai shi wanda ya 'daurawa auren 'dan sa ne na cikin sa..kinga an nuna mana bambanci a zahiri.
...ran kowa da muke tare sai da ya 6aci a wurin hakan yasa Mahaifin Hudah yace tunda muka zo har Azare da niyyar aure to baza'a fasa ba...yace s 'daura auren kawai da Hudah ya bashi ita...na so in nuna 'kin amincewa amma yace matu'kar na nuna bana do to azahiri na nuna masa 'kyama matsayin sa na talaka...dole naja baki na nayi shiru na wakilci amarya Ja'afar kuma ya kar6awa Mu'een gudun maganar da zai biyo baya, yanzu dai Hudah 'yar ki da kike tsananin so marsayin mata take a wurin 'dan ki Muhammad..."
Ya 'karashe yana 'yar dariya.
Ammi kam rasa abinda zata ce da shi tayi saboda farin ciki..ita kanta ta fahimci jin da'din Alhaji Baba kan wannan auren...to inaga ita da ta jima da son ganin faruwar hakan duk da bata furta ba amma ya da'de cikin zuciyar ta.
Maganar Alhaji Baba ne ya katse mata tunanin ta inda yace" Sai dai bazan bashi Hudah ba har sai na tabbatar da cewa halin sa mai kyau ne , zargin da nake yi masa abaya idan ya kasance ba gaskiya ba ne sannan zan bashi Hudah matsayin mata dan bana so ya lalatawa yarin farin cikin ta da gur6ataccen tunani..matu'kar na tabbatar da zargi na akan sa wallahi da kaina zan sa ya rabu da ita in aura mata wani daban..dan haka a yanzu ko sanin cewa itace matar sa bana so yayi harda itama...ke de kawai ki 'kara kulawa da rayuwar ta ki tabbatar babu wanda ke shiga rayuwar ta tunda yanzu da aure akanta, batun zuwa gida kuma gobe da safe zan sa akaita ta gaida mahaifin nata 'kila ma a goben...zai koma".
Ammi kam ji tayi kamar ta taka rawa saboda tsananin farin ciki...ba ta iya ri'ke maganar ba sai da ta sanar da Anty Zee a daren ranar..ga mamakin ta kuwa sai taga farin cikin da Anty Zainab ta shiga har yaso ya zarta nata ma.
Sam hakan bai sa Ammi mamaki ba cuz tasan irin 'kaunar da Anty Zainab ke wa Mu'een, in sha'kuwa ce kuwa ko ita da ta haife shi baza ta ce tafi ta sha'kuwa da shi ba saboda a gaban ta ya tashi..so fiye da haka ma idan ta gani daga Anty Zainab bazai sa ta mamaki ba.
Itama Anty Zainab Uncle Ja'afar ta 'kira a waya tace dashi gaskiya bai kyauta mata ba da har ya 6oye mata wannan maganar.
Sai yace" Tunda yanzu kinji ai shikenan".
Ita ka'dai tasan me take ji cikin ranta...Alhamdulillah kawai take ta maimaitawa, cuz tafi kowa 'kaunar ganin Mu'een 'din ya samu mata irin Hudah sai gashi Allah ya cika mara burin ta cikin sau'ki, badan Ammi ta gaya mata abinda Alhaji Baba yace game da batun ba da gobe sai ta ha'da sabuwar gagarumar walima na farin ciki dan ta nuna godiyar ta ga mahalicci.
Washe gari sunday..kamar yadda Alhaji yayi al'kawari kuwa hakan ne ya faru..cuz wani yaron sa ya sa ya kaini gidan mu dan gaida mahaifi na, anan na tarar da shi ma yana kan shirin tafiya, ban fahimci komai ba duk kuwa da cewa naga anata nan nan dani sannan Baban mu yayi min doguwar nasiha cikin natsuwa kan ha'kuri tamkar wanda ganawar mu da shi kenan ta 'karshe har yasa jiki na yayi sanyi.
Ko da wasa babu wanda yace min an 'daura min aure duk kuwa da cewa duk sun sani, ban sani ba ashe duk Alhaji Baba ya ro'ki da kar a fa'di min har sai yaga abinda hali yayi.
Abu 'daya na fahimta kawai canji daga wurin ahali na, yanda ake bani wani daraja da kaffa-kaffa dani abin ya 'daure min kai sosai, sai dai ban kawo batun aure ba sam ko a tunani na, na dai yi tunanin girman da na 'kara ne ya sa ake min hakan dan haka naji Anty Zainab ta fa'di lokacin da zan taho.
Turare wannan hanani amfani tayi da asalin nawa ta bani wasu marasa 'kamshi sosai wai ai na girma yanzu so in dinga kula da komai na rayuwa ta.
ko da nace zanje gidan su Binta ma Ummah ta hanani tayi, ko gidan Anty saudahn mu banje ba Ummah ta ta ri'ke ni a gida tace wai in bari sai wani lokacin kawai.
Ban fi 3hrs ba a gidan aka dawo 'dauka ta...haka na shiga mota ina tuttura baki na gaba da mitar ni banganewa wannan sabuwar tsarin ba duk an bi an takura ni.
Da isata gida kuwa na tari Ammi da mitan Ummah ta bata barni naje ko'ina ba, ko gidan Addah ta banje ba da gidan su Binta...kafin in kai 'karshen magana ta kuwa sai ga hawaye ya gangaro min.
Ammi rasa abinda zata ce da ni tayi kawai sai ta jawo jikin ta ta hau lallashi na, cikin hakan dmtake ce dani kar in da mu wataran ai zanje...nace" Ammi kinga ma fa Ma'u tace min zata zo bikin Yah Deen kuma bata zo ba bansan me yasa ba kuma ban je na duba ta ba duk Ummah ta ta hana ni".
" Rabu da ita ai zata zo may be bata samu daman zuwa bane kawai".
Anty Zee na ganin yanda nake yiwa Ammi kuka sai ta janyo ni ta ringa bani misalai tana jan hankali na da da'da'dan kalamai take fa'din duk mace mai aji ai bata yawan yawo komin ta bisa tsari take yin sa ba wai ta ringa shige-shige ko'ina kamar akuyar da babu 'dauri ba.
Ni dai kawai jin ta nayi ba wai dan na fahimci me take nufi ba.
Ranar kuwa gida ya watse kaf kowa ya koma inda ya fito, ko abokan Yah Deen ma ranar duk suka koma dan daga gida da suka gaida su Alhaji sai suka wuce bayan ya sallame su, aka bar shi shi ka'dai sai Imrana kamar da can.
Yah Deen ranar bai je ko'ina ba dan haushin an hana shi tafiya bacin ba komai yake yi a gidan ba, haka ya yini a wuri 'daya illah Imrana da ke faman shiga yana fita...cikin kwanciyar hankali abin sa.
Uncle J ma da sassafen ranar ya koma Taraba Anty Zee kuwa ba yanzu ba sai daga baya zata koma dan sai ta 'dan kwana biyu a Azare ma tukunna kafin ta tafi, gida ya zama shiru babu da'di..lalle jama'ah rahama.
Haka inaji ina gani aka takurani da zaman gida, illah makaranta da nake zuwa...kuma ko makarantar ma ban ganin Ma'u, gashi su Ammi sun hanani yawo balle inje gidan su in dubo ta...
Sai da aka yi kwana biyar da bikin Yah Deem kafin Ma'u tafara fitowa makaranta...nan na isheta da tambayar me yasa bata zo bikin Yah Deen ba?"
Tace min" bikin da aka ce an fasa 'din?"
Nace" Erh amma ai de mutane sun taru kowa yazo nayi ta duba ki bangan ki ba...".
Tace" Banda lafiya ne shiyasa banzo ba".
Sai nace
" To waye yace miki an fasa kuma ?"
" Imrana".
Ta bani amsa a takaice.
Sai nace
" Ayyah ai naso in zo gidan na ku amma an hanani yawo yanzu shiyasa banzo ba".
Shiru tayi bata sake kulani ba.
One thing da na fahimta game da Ma'u yanzu sam bata son yawan surutu sosai sai dai ban san dalili ba dan haka nima sai nayi shiru ko mun ha'du a makaranta ko Islamiya hirar mu ka'dan ce da ita da yake ma ba kullum take zuwa ba sai jifa-jifa...amma duk ta natsu ta daina rawar kai yanzu (ban sani ba ashe Yah Deen ne ya koya mata hankali).
_Comment_
_Vote_
_Share_
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
_*Daga marubuciyar Littafin CAPTAIN ABBAS*_
_Nagode sosai masoya Allah ya bar min ku..._
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *55*
Hisham yazo gida kamar yadda mahaifiyar sa ta bu'kata sunyi magana kuma ya fahimce ta, musamman ma da yaji cewar an riga da an aura masa Husnah, jin hakan ya matu'kar faranta ransa har ma ya kasa 6oye farin cikin sa, bakomai bane kuma yasa hakan face tsananin soyayyar da yake yi mata, shiyasa ma ko guda daga cikin sharu'd'dan da mahaifiyar sa ta gindaya masa akan Husnahn bai yi jayayya da shi ba.
Zuciyar sa 'daya ya 'daukan mata al'kawarin kulawa da Husnah da kuma sau'ke duk wani hakkin ta da ya rataya akan sa, ya kuma yi al'kawarin bata kariya iya iyawar sa, duk da Hajiya Kareema bata fito fili ta bayyana masa asalin meke tafiya ba amma tayi 'ko'karin ganin ta nuna masa daraja da muhimmancin da Husnan ke da shi a wurin sa...wanda bayaga aure akwai kyakykyawar dangantaka tsakani wanda shi kansa ya sani.
Ko da ya isa ga mahaifin sa ma ba wani ba'kon al'amari yaji daga bakin sa ba wanda zai rikita shi, bambancin kawai shine shi bai yi masa maganar ta fuskar fahimta ba, ya dai ce da shi yayi masa aure da Husnah and kuma yana fatan zai masa biyayya bisa hakan.
Hisham bai wani damu ba dan ya riga ya san wace Husnah, kuma sun riga sun gama magana da mahaifiyar sa kafin nan so hankalin sa kwance ya bar gaban mahaifin sa da 6oyayyen farin cikin sa a zuci.