← Book details Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 211

Sashe 34

Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sau'kar sa keda wuya kuwa ya dira gidan a hargitse...inda yana shiga parlourn ya samu Mu'een zaune cikin damuwa, ga ta ita kuma zaune ta kwantar da kant jikin kujera a hakan bacci ya 'dauke ta wanda tashin farko zaka fahimci cewa shima baccin ba'a nutse take yinsa ba, ba itan ba ba yaron ba hatta gidan gaba 'daya idan ka kalla zaka san cewa masu shi na cikin tashin hankali kowa yayi jugum har zaka rasa gane waye cikin su yafi shiga damuwa...domin shi ma yaron ya damu da rashin mahaifin nasa cuz ba haka suka saba ba ya saba ganin sa kullun agida amma yanzu babu shi kuma basa waya dashi ko Landline yaji tana 'kara ya kanje da sauri ya jira zuwan Amminsa a wurin da tunanin ko mahaifin sa ne, in kuwa tazo ta 'dauki 'kiran sai ya bita da idanu gami da zuba kunnuwa ko zaiji muryar mahaifin sa amma baya jin hakan.

Ga yawan kukan Ammin sa dake 'kara 'daga masa hankali shima sau da dama tayata yake yi suyi ta kukan tare shiyasa duk suka fita hayyacin su.

Makaranta kuwa itama babu labarin ta, domin tun ranar da aka kama Baban sa bai sake zuwa ba.

Shiyasa duk suka zama wasu iri dasu gwanin tausayi, kallo 'daya zakayi musu ka fahimci yanayin da suke ciki.

Mu'een na ganin Ja'afar a tsaye ya taso da sanyin jiki ya iso gaban shi, Ja'afar sai ya 'dago shi sama kafin yace wani abu ma Mu'een ya riga shi da fa'din " Uncle kaga Ammina kullum kuka takeyi kuma Alhaji Baba baya nan kullum bana ganin sa agida bansan inda yaje ba inaso in ganshi Uncle".

Kwantar da kan Mu'een yayi kan kafa'dar sa gami da sau'ke ajiyan zuciya, sosai zuciyar sa ta karye da jin furucin yaron.

Da kansa ya shiga ya watsa masa ruwa a extra room dake gidan dan ganin yana bu'katar hakan sannan ya fito da shi yace yaje ya 'dauko kayan sa ya sanya masa sai suje gurin Alhaji Baban.

Mu'een najin haka ya tafi da gudu da yake yana da wayo, da idanu kawai Ammin sa ta raka shi batare da tayi yun'kurin motsawa ba, har yaje ya 'dauko kayan wandon jeans da riga ya sake koma 'dakin " Uncle gashi ka samin da sauri muje wurin Alhaji Baba"
Yayi maganar fuskar sa cike da annurin zaiga Alhaji Baba.

Palour suka dawo bayan ya shirya shi wanda tana ganin su tare sai ta mi'ke tsaye tare da fa'din " Ja'afar please help me....Allah sharri suke yi masa kuma sun'ki saurarata wallahi Taheer bai saci ku'din kowa ba".

Sai yace
" Kunyi magana da shi ne?"
Tace
" ah ah sun hanamu ganin sa ma"

Tambayar Division 'din da yake yayi ta gaya masa sai yace to ta nutsu ta 'dauko masa key su je yanzu ko za'a dace su ganshi"

Da sauri ta wuce ciki ta duba key 'din da rawar jiki domin ita rabon ta da hawa mota tafi 3weeks tun ma kafin faruwar lamarin kuma koda abin ya faru ma idan zasuje Division 'din da aka kulle shin da taxi suke zuwa bata ko sauraran motar gida.

Shine ya jasu har Division 'din, inda aka kai ruwa rana kafin ya samu suka ganshi da dokar mintina biyar cif.

Ganin Tahir sai da ya kusan sanya shi kuka amma wannan dauriyar da ya ara ya yafawa zuciya da fuskar sa tun a gida gaban Mu'een yake so ta 'kara rufa masa asiri, yaso kar ya zubda hawaye amma ganin yanayin da 'dan uwan nasa yake ciki ka'dai ma abin ya ta6ashi sosai domin ba kyan gani, gaba 'daya ya rame yayi ba'ki ya fita a hayyacin sa, rashin 'kibar daya ke da ita ita ta 'kara taimakawa wajen bawa tsufa shiga yanayin halittar sa, gaba 'daya ya zama tamkar wani dattijon mutun ga wani uban handcuff da aka maka mai a hannu.

Mu'een na ganin sa ya fara murna yana fa'din " Alhaji Baba....Alhaji Baba kazo mu tafi gida kullum Ammi kuka take yi bata bacci..."

Kafin ya kai aya sai Taheer ya juya baya dan baya son yaron yaga hawayen da ya sau'ko masa...shi kuwa Mu'een sam ya'ki zama jikin Uncle Ja'afar 'din sai da ya 'kwaci jikin sa yaje ya rungume Alhaji Baban yace " Kaima kana kuka ko Alhaji Baba...Uncle kace yayi shiru mu tafi gida, Alhaji Baba waye ya saka maka wannan abin?"

Yayi tambayar gami da shafo handcuff 'din dake hannun sa......jikin sa Alhaji Baba ya jawo shi sosai ya rungume shi yana 'kara sau'kar da wasu hawayen masu zafi.

Ammi ma dake gefe kukan takeyi yayin da Taheer yayi 'karfin halin ri'ke nasa hawayen bai bari sun sau'ko ba amma kallo 'daya zakayi masa ka fahimci cewa baya cikin mood mai da'di musamman idan kayi duba da yanda idanun wansa suka yi jajir......a hankali Taheer yace " Ja'afar ban san me zance kan lamarin nan ba dan bansan meke shirin faruwa dani ba kwata-kwata, amma dai inada tabbacin kai da Aishatu kunsan cewa ni bazan ta6a iya aikata irin wannan aikin ba har abada ko?"

Kai Ja'afar ya 'dage gami da dafa kafa'dar sa yana shirin magana sai Taheer ya riga da sake fa'din " inaso koda mutuwa nayi sanadin hakan dan Allah kuyi 'ko'karin fahimtar da Muhammad cewa mahaifin sa bashi da laifi kan hakan, ni ban ta6a cin haramun ba, ban saci ku'din kowa ba... 'kaddara ce kawai ta hau kaina kuma na kar6e ta da hannun bibbiyu matsayina na bawan Allah...."

Taran shi Ja'afar yayi da fa'din " ka daina fa'din haka dan Allah Alhaji insha Allahu komai zaizo da sau'ki, mu miye amfanin mu? Zamu kai 'karar duk wanda ya zalince ka wurin mahallici da izinin sa kuma insha Allahu zamuyi nasara".

Bai ce dashi komai ba sai kawai ya 'dago kansa ya kalli Ammi da tun 'dazun take tsaye tana aikin kuka.....suna ha'da idanu sai ta 'daga kanta sama da niyyan tabbatar masa da kalaman Ja'afar 'din wani kukan na sake 'kwace mata.

Saurin cire Mu'een yayi daga jikin sa ganin mai kula dashi dake tsaye gefe dasu na shirin tunkaro su, baya son ayi abinda zaisa Mu'een 'din kuka ko kuma yaji ba da'di tunda bai san meke faruwa ba, dan haka sai yayi saurin mi'kewa tare da fa'din " Mu'inuddeen kuje gida da Uncle ko..nima soon insha Allahu zanzo gidan kaji Babana".

Kafin yaron yayi magana har ya juya 'dan sandan ya rufa masa baya suka yi ciki.

Kuka Mu'een ya sanya yana 'kiran sunan shi sai Ja'afar yayi saurin 'daga shi sama yayi waje dashi, Ammi ma cikin sakakkiyar gwiwa tabiyo su abaya har wajen motar su, da 'kyar Ja'afar ya samu ya lallashe sa yayi shiru da al'kawarin zai kawo shi wurin Alhaji Baban gobe sannan yayi shiru.

Zugum sukayi cikin motar ko'ina shiru babu mai ko motsin kirki illah hannun Ja'afar dake tu'ki har suka je gida. Yana sau'ke su ya sake fita da motar dan neman mafita, domin baya jin zai iya barin 'dan uwan sa ya sake ko kwana 'daya ne cikin wannan halin balle nan da 3weeks da aka ce kafin aje kotu.

Wahala sosai yasha kafin ya samu ganin mutumin da yake tunanin zai taimaka musu shima 'din kuma sai ya so ya nuna akwai wani uzurin a gaban sa amma haka ya nace bai bar inda yake ba da 'kyar ya samu Commisionern ya saurare shi da 'kyar ya amince abada bailing sa bayan ya 'kira wani da bai san ko wanene ba amma yana kyautata zaton ma'aikatar da Taheer 'din ke aiki ya 'kira amma da shara'din daga yau 'din har ranar da za'a shiga kotu kullum zai je ya sa hannu domin a tabbatar da cewa yana kusa, dai-dai da rana 'daya idan ya sa6a lokaci ko rana zasu yi abinda suke ganin dai-dai me agare su.

_Comment_
_Vote_
_Share_

*Salmerh ce* 😍,

[12/22/2019, 3:18 PM] 🌸Salmerh🌸: 💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)

By
*Salmerh MD*

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *18*

Batare da tunanin komai ba Ja'afar ya amince dan kuwa sosai yake da ya'kinin cewa Allah yana tare da su kuma shi zai taimake su, farin cikin sa 'daya kawai shine yau 'dan uwan sa zai kwana cikin gidan sa da iyalan sa .

Kamar yadda suka fa'da 'din kuwa hakan ne ya faru domin kullun yakan je yayi signing kamar yadda suka bu'kata har tsawon sati biyu batare da yayi fashi ba.

Ammi kuwa s
duk iya 'ko'karin da zatayi na ganin cewa ya amince an saida abubuwan data gada daga gurin mahaifin ta tanayi domin a biya bashin sharrin da aka tiwa mai gidan naga amma sam Taheer ya 'ki amincewa bai kuma sanar da ita da dalilin 'Kin amincewar yasa ba.

'Bangaren shi Tahir 'din kuwa har cikin ransa yake jin tamkar idan yayi hakan bai kyauta mata ba duba da yanda wancen Lawyern ya damfare ta ya tafi da dayawa daga cikin dukiyar ta sannan 'dan abinda suka rage kuma yace zai yi haka dasu ai bai kyauta ba....shi aganin sa.

Ammi kuwa rashin amincewar tasa sosai ya bata haushi har ma take jin tamkar da'ace takaddun dukiyar na wajen ta da tuni tayi abinda zatayi sai da ya 'dau duk matakin daya ga daman 'dauka daga baya amma baby abinda zai hanata aiwatar da nufin ta.

Abin na damun ta sosai a duk lokacin da ta tuna cewa mijin ta matsayin mai laifi yake dan har fargaban dare yayi gari ya waye take yi sai take ganin kamar lokacin rabuwan ta da mijin ta ne yake 'kara kusanto ta, dan haka ranar wata talata ta fara bincike sosai cikin 'dakin sa da niyyan duba takaddun dake wurin sa.....domin sunyi magana dashi ko yana da wasu ku'dade cikin account 'dinsa sai yace mata bad
baza su haura 10million ba ku'din ita kuwa bata son rasa shi ta ko wani 6angare.
Chapter 34 · 0% Book details