Sashe 51
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
" Yanzu zan shirya insha Allahu"
yace tare da juyawa ya shige cikin gida.
Kallon Alhaji Baba nayi bayan shigewar tasa a hankali nace " Alhaji Baba wannan ma 'dan ka ne?"
Cike da kulawa yace dani
" D'ana ne Hudah...baki ta6a ganin sa ba ko?"
" ah ah jiya na ganshi a parlour".
Alhaji Baba sai yayi murmushi yace " to shima yayan ki ne kinji shine babban 'dana...kina ce masa Yayah".
Tunzuro baki na nayi gaba tare da fa'din " ni dai ba Yayah na bane...shida ma har marina yayi jiya dan nayi karo dashi kuma yanzu ma ai dana gaida shi k'in amsawa yayi...kuma bazan sake gaida shi ba ma".
Da mamaki Alhaji yake kallo na yace
" Mari kuma? Deen 'din ne ya mareki?"
Kaina na daga sami gami da fa'din
" Ehh amma Ammi tace zata rama min"!
Na karasa maganar harda jin da'di na.
Murmushi yayi dan yasan Ammi ta fa'di hakane kawai dan ta lalla6ani....
Kafin ya sake yin wata magana sai na riga shi da fa'din " Alhaji Baba Deen 'din ma sunan shi ne? Naji Ammi ba haka tace jiya ba, kuma naji ka ce mishi Muhammad duka sunan na shi ne shi ka'dai?"
Ta'kaitacciyar dariya yayi tare da fa'din
" Sunan sun masa yawa ko Hudah?"
Sai na 'dage kaina sama alamar " ehh"
Alhaji ma sai yace
" Kuma ai duk sunayen shi ne, Muhammad Mu'inuddeen sunan sa....zaki iya ce masa Mu'een sannan Deen duk wanda zaki iya ki fa'di.....gaya min wanne yafi miki sau'kin fa'da ?"
Ya 'karashe da tambaya ta...a hankali na bu'di baki na na furta
" *Deen* !"
Alhaji baba sai yayi murmushi yace dani " yayi to duk 'daya....daga yau kuma shima yayan ki ne idan bakya yi masa rashin ji bazai na dukan ki ba kinji?".
"Uhmn"
Nace da Alhajin gami da mi'kewa " na tafi " na sake fa'di batare da jiran jin komai daga bakin sa ba kawai nayi gaba abina.
Cikin gida kuwa yau ma Mu'een kunun sa ya sha son ransa harda waina ya hada yaci har guda biyu, cikin ransa yake yabawa da da'din wainar da duk zaton sa Ammin ce keyin kunu da wainar dan sam bai san cewa da safen ake kawo shi ba.
Kofi ya 'daya ya kur6i kunun a hankali bayan ya ha'diye sai ya kalli Ammi yace " Alhaji Baba fa bai shigo yayi break 'din ba kuma naji yana fa'din zamu fita yanzu?"
" Azumi yake yi"
Ammi ta bashi amsa a takaice.
Sai ya jinjina kansa tare da fa'din " ai na manta ma ashe yau thursday...duk da'din kunun ki ne kuma fa ya sani mantuwar Ammi".
Ya karashe maganar yana murmushi.
" Da'din kunun masu kunu dai...."
Ammi tace da shi.
Deen bai wani sa maganar aka ba kuma balle ya fahimci me take nufi...da yake ma tana gama waccan maganar sai ta sake fa'din " ba surutu ba ka hanzar ta dai kasame shi tun da yana can yana jiran ka"
Wannan maganar ne ya 'dauke masa hankali harya gama breakfast 'din ya tashi da hamdala bayan ya goge bakin sa....bai tuna maganar Ammi ta farkon ba.
*Kuyi ha'kuri fa kun jini shiru jiya...alhini ne ya hana ni posting* *wlh.....amma yanzu Alhmdllh...zamu cigaba da iznin Allah.*
🤔AMMA READERS ME YASA BA KWA SHARING NE❓.......any ways🤷♀👇🏼
~A CIGABA DA GASHI....~ 🤞🏻
_Comment, Vote and share please_ 👌🏻
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *27*
Da yamman ranar kuwa babu islamiya da yake ranar Alhamis ne kuma bama zuwa, ranar ma ni da Nanne muka kai marka'den shinkafar wainar Ummahn mu...da kuma gya'da dayake yau d'in harda gya'da ta gyara shiyasa muka tafi mu biyu, dama ranar da duk za'ayi markaden gya'da ne muke tafiya mu biyu idan kuwa marka'da'd'iyar gya'dar Ummah bata kare ba ni ka'dai ke zuwa in marka'do mata shinkafa.
A hanyar mu ta dawowa muna tafiya muna 'yar hira, wani sa'in kuma fa'da mukeyi da ita dan ni nawi ya dame ni sosai yayin da ita kuma take faman jan 'kafa tafiyar ta kamar dan dole take yin sa.
Burina tayi sauri mu wuce gida ita kuma ta'ki a hankali take tafiyar ta kamar yanda ta saba.
Cikin shirin zuwa ball yazo ya gifta mu ban sani ba ko bai gane ni amma ni kam sau 'daya na kalle shi amma sai na gane shi.
Sai da ya wuce ne sannan Nanne tace da ni " tab amma wannan yana da kyau gaskiya".
" Waye wai wancan ?"
Na tambaye ta gami da nuna shi da bakina cuz da duk biyun hannaye na ri'ke roban dake kaina.
Nanne sai tace " ehh mana koke baki ganshi ba "
Juyawa nayi na cigaba da tafiyata sannan nace
" Na ganshi mana... 'dan gidan Alhaji Baba ne, mugunta ce dashi ingaya miki sosai".
Baki kawai Nanne ta ta6e bata 'kara magana ba, daga nan kuwa muka cigaba da tafiyar mu.
Na kanyi gaba in barta dan yanayin tafiyar mu ba 'daya bane da ita sam...ban sani bama ashe Nanne kam hankalin ta duk ya koma kan Yah Deen ne, tafiya take tana waigen sa lokaci-lokaci....ni kuwa dake gaban ta bansan hakan ba sam....bazata kawai naji karan fa'duwan abu...waigowata kawai sai naga ashe marka'den dake kan Nanne ne ya kife gaba d'aya sanadin tuntu6e da tayi.....ido na zaro na kalli marka'den sannan na kalle ta...." ta6'di Nanne marka'den wainar kika zubar?"
Sai tace dani " ai tunt6e nayi ban kula ba".
" To ki 'dauko robar mutafi gida...."
Hannu ta kai ta dago robar sai muka ga ashe itama ta face yayin da marfin ta yake nan garau jefe a gefe guda.
" ko zamu 'dan kwasa ka'dan?"
Nanne ta fa'da tana kallona" Sai nace kamamin mu sau'ke to sai in tayaki".
" ka'dan muka kwasa muka bari dan gaba d'aya ya lalace a wurin ba zai 'kara amfani ba.
Koda muka je gida kuwa Ummah bata ce komai ba jin cewa Nanne ce ta zubar kawai sai ta kar6i wanda muka kwasa 'din ta ha'da da ruwa da dama ta baiwa ragunan Baban mu suka shanye abinsu.....wannan dalilin ne ya sanya washegari bata yi waina ba harma da kunun baki d'aya.....sanadin kallon Deen da Nanne keyi wanda a lkacin ita kanta ma bazata iya shaidar ya san da zaman ta a duniya ba ko a'a duk da kuwa ha'duwar su da shi ta biyu kenan inda yau.
*****
Tsananin yanda Deen ya saka Nanne cikin zuciyar sa ya sanya kafin sati har ya nemi duk wasu bayanan da ya kamata ya sani game da ita, cikakken sunan ta da sunan mahaifin ta harma da gidan su duk ya sani amma bai ta6a zuwa ba.
Da yake da wayo yake yin tambayar ba a fili yake fitowa ya bayyana manufar sa ba...misali ranar da zai fara yin tambayar aranar wani friend 'din sa yazo wurin sa ne sai da ya daidaici 'karfe biyu tayi sai ya jashi suka fito wajen gida suka zauna kamar da gaske, daka yanzun 'karfi da yaji yake tilastawa kansa zaman waje kawai dan ya ganta yaji sanyi cikin ransa..wani sa'in ma idan ya fito sallar azahar baya ta6a komawa gida koda kuwa 'karfe nawa zai kai a wurin to bazai ta6a shigewa ba sai yaga giftawar ta...(ni kuwa nace...aiki ya kama gwari).
Suna zaune a wurin muka zo muka wuce bamu ma kula da su ba....
Ashe Deen kam hankalin sa na kanmu sai ya koma ya kishingi'da ya wani lumshe idanu bazaka ta6a yin zaton yana ganin abu a hakan ba.
Shi 'dayan abokin Deen da bai san meke faruwa bane da wucewar mu sai ya girgiza kansa yace " Allah sarki...wallahi yarinyar nan na matu'kar bani tausayi...gata haka zaka ganta kamar lafiyayya amma wallahi kar kaso kaga wurin jinyarta, hankalin kowa sai ya tashi a dangin ta, gata da masifar shiga rai".
Ya 'karashe maganar da sanyin murya.
Mu'een na jin haka sai ya gyara zaman sa da kyau da mamaki yace da shi " wace kake magana akai wai?"
Juyawa yayi ya kallomu dan shi baya ya juya mana Yah Deen ka'dai ne ke facing da hanyar da muka bi.
" Nannen Malam Mamman nake magana akai...gasu can yanzun nan suka gifta mu 'yar doguwa mai hasken....ai kai bazaka sansu ba saboda ba'a garin kake zama ba shiyasa...
Yah Deen taran shi yayi da fa'din " to wani irin suna ne kuma Nanne?"
Hannu wancan 'din ya 'dago yace kai dakata " cikakken sunan ta Amina Nannen kawai sunan gida ne".
Komawa yayi ya kishingi'da yana kallon abokin na sa kamar mai nazarin wani abu a hankali sai yace to me ke damun ta har haka da kace tana baka tausayi?"
" Ai kai de ka bari...wallahi sickler ce da ita abin tausayi yarinyar ni ai badan hakan ba wallahi sai na nemi auren ta yarinyar akwai natsuwa tun tana 'yar 'karamar ta".
Idanun sa ya miyar ya limshe su a hankali cikin ransa yace " gara hakan ai, kaga ni sai na nemi auren ta in kula da ita....."
A fili kuwa " Allah yata lafiya" kawai ya furta daga nan bai 'kara fa'din komai ba.
A ranar ne Mu'een yasan haka game da Nannen mu....to ko ranar da yaga gidan mu ma sanadin wani da suke ha'duwa a filin ball ne ya sa mu ganin gidan da yamma bayan sun tashi daga ball 'din sai hanya ta biyo da su ta wurin anan yaga Nannen mu ta fito daga ma'kwabta ta shiga gida.
Shi 'dayan bai ma kula da ita ba Yah Deen ne ka'dai ya lura da hakan.
Basarwa yayi sai da ta shige gidan kafin ya tambaye shi wai wannan gidan...gidan waye ne?"
" Gidan Malam Mamman ne...me ya faru?"
Abokin ya 'karasa da tambaya, Mu'een sai yace " bakomai".
yace tare da juyawa ya shige cikin gida.
Kallon Alhaji Baba nayi bayan shigewar tasa a hankali nace " Alhaji Baba wannan ma 'dan ka ne?"
Cike da kulawa yace dani
" D'ana ne Hudah...baki ta6a ganin sa ba ko?"
" ah ah jiya na ganshi a parlour".
Alhaji Baba sai yayi murmushi yace " to shima yayan ki ne kinji shine babban 'dana...kina ce masa Yayah".
Tunzuro baki na nayi gaba tare da fa'din " ni dai ba Yayah na bane...shida ma har marina yayi jiya dan nayi karo dashi kuma yanzu ma ai dana gaida shi k'in amsawa yayi...kuma bazan sake gaida shi ba ma".
Da mamaki Alhaji yake kallo na yace
" Mari kuma? Deen 'din ne ya mareki?"
Kaina na daga sami gami da fa'din
" Ehh amma Ammi tace zata rama min"!
Na karasa maganar harda jin da'di na.
Murmushi yayi dan yasan Ammi ta fa'di hakane kawai dan ta lalla6ani....
Kafin ya sake yin wata magana sai na riga shi da fa'din " Alhaji Baba Deen 'din ma sunan shi ne? Naji Ammi ba haka tace jiya ba, kuma naji ka ce mishi Muhammad duka sunan na shi ne shi ka'dai?"
Ta'kaitacciyar dariya yayi tare da fa'din
" Sunan sun masa yawa ko Hudah?"
Sai na 'dage kaina sama alamar " ehh"
Alhaji ma sai yace
" Kuma ai duk sunayen shi ne, Muhammad Mu'inuddeen sunan sa....zaki iya ce masa Mu'een sannan Deen duk wanda zaki iya ki fa'di.....gaya min wanne yafi miki sau'kin fa'da ?"
Ya 'karashe da tambaya ta...a hankali na bu'di baki na na furta
" *Deen* !"
Alhaji baba sai yayi murmushi yace dani " yayi to duk 'daya....daga yau kuma shima yayan ki ne idan bakya yi masa rashin ji bazai na dukan ki ba kinji?".
"Uhmn"
Nace da Alhajin gami da mi'kewa " na tafi " na sake fa'di batare da jiran jin komai daga bakin sa ba kawai nayi gaba abina.
Cikin gida kuwa yau ma Mu'een kunun sa ya sha son ransa harda waina ya hada yaci har guda biyu, cikin ransa yake yabawa da da'din wainar da duk zaton sa Ammin ce keyin kunu da wainar dan sam bai san cewa da safen ake kawo shi ba.
Kofi ya 'daya ya kur6i kunun a hankali bayan ya ha'diye sai ya kalli Ammi yace " Alhaji Baba fa bai shigo yayi break 'din ba kuma naji yana fa'din zamu fita yanzu?"
" Azumi yake yi"
Ammi ta bashi amsa a takaice.
Sai ya jinjina kansa tare da fa'din " ai na manta ma ashe yau thursday...duk da'din kunun ki ne kuma fa ya sani mantuwar Ammi".
Ya karashe maganar yana murmushi.
" Da'din kunun masu kunu dai...."
Ammi tace da shi.
Deen bai wani sa maganar aka ba kuma balle ya fahimci me take nufi...da yake ma tana gama waccan maganar sai ta sake fa'din " ba surutu ba ka hanzar ta dai kasame shi tun da yana can yana jiran ka"
Wannan maganar ne ya 'dauke masa hankali harya gama breakfast 'din ya tashi da hamdala bayan ya goge bakin sa....bai tuna maganar Ammi ta farkon ba.
*Kuyi ha'kuri fa kun jini shiru jiya...alhini ne ya hana ni posting* *wlh.....amma yanzu Alhmdllh...zamu cigaba da iznin Allah.*
🤔AMMA READERS ME YASA BA KWA SHARING NE❓.......any ways🤷♀👇🏼
~A CIGABA DA GASHI....~ 🤞🏻
_Comment, Vote and share please_ 👌🏻
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *27*
Da yamman ranar kuwa babu islamiya da yake ranar Alhamis ne kuma bama zuwa, ranar ma ni da Nanne muka kai marka'den shinkafar wainar Ummahn mu...da kuma gya'da dayake yau d'in harda gya'da ta gyara shiyasa muka tafi mu biyu, dama ranar da duk za'ayi markaden gya'da ne muke tafiya mu biyu idan kuwa marka'da'd'iyar gya'dar Ummah bata kare ba ni ka'dai ke zuwa in marka'do mata shinkafa.
A hanyar mu ta dawowa muna tafiya muna 'yar hira, wani sa'in kuma fa'da mukeyi da ita dan ni nawi ya dame ni sosai yayin da ita kuma take faman jan 'kafa tafiyar ta kamar dan dole take yin sa.
Burina tayi sauri mu wuce gida ita kuma ta'ki a hankali take tafiyar ta kamar yanda ta saba.
Cikin shirin zuwa ball yazo ya gifta mu ban sani ba ko bai gane ni amma ni kam sau 'daya na kalle shi amma sai na gane shi.
Sai da ya wuce ne sannan Nanne tace da ni " tab amma wannan yana da kyau gaskiya".
" Waye wai wancan ?"
Na tambaye ta gami da nuna shi da bakina cuz da duk biyun hannaye na ri'ke roban dake kaina.
Nanne sai tace " ehh mana koke baki ganshi ba "
Juyawa nayi na cigaba da tafiyata sannan nace
" Na ganshi mana... 'dan gidan Alhaji Baba ne, mugunta ce dashi ingaya miki sosai".
Baki kawai Nanne ta ta6e bata 'kara magana ba, daga nan kuwa muka cigaba da tafiyar mu.
Na kanyi gaba in barta dan yanayin tafiyar mu ba 'daya bane da ita sam...ban sani bama ashe Nanne kam hankalin ta duk ya koma kan Yah Deen ne, tafiya take tana waigen sa lokaci-lokaci....ni kuwa dake gaban ta bansan hakan ba sam....bazata kawai naji karan fa'duwan abu...waigowata kawai sai naga ashe marka'den dake kan Nanne ne ya kife gaba d'aya sanadin tuntu6e da tayi.....ido na zaro na kalli marka'den sannan na kalle ta...." ta6'di Nanne marka'den wainar kika zubar?"
Sai tace dani " ai tunt6e nayi ban kula ba".
" To ki 'dauko robar mutafi gida...."
Hannu ta kai ta dago robar sai muka ga ashe itama ta face yayin da marfin ta yake nan garau jefe a gefe guda.
" ko zamu 'dan kwasa ka'dan?"
Nanne ta fa'da tana kallona" Sai nace kamamin mu sau'ke to sai in tayaki".
" ka'dan muka kwasa muka bari dan gaba d'aya ya lalace a wurin ba zai 'kara amfani ba.
Koda muka je gida kuwa Ummah bata ce komai ba jin cewa Nanne ce ta zubar kawai sai ta kar6i wanda muka kwasa 'din ta ha'da da ruwa da dama ta baiwa ragunan Baban mu suka shanye abinsu.....wannan dalilin ne ya sanya washegari bata yi waina ba harma da kunun baki d'aya.....sanadin kallon Deen da Nanne keyi wanda a lkacin ita kanta ma bazata iya shaidar ya san da zaman ta a duniya ba ko a'a duk da kuwa ha'duwar su da shi ta biyu kenan inda yau.
*****
Tsananin yanda Deen ya saka Nanne cikin zuciyar sa ya sanya kafin sati har ya nemi duk wasu bayanan da ya kamata ya sani game da ita, cikakken sunan ta da sunan mahaifin ta harma da gidan su duk ya sani amma bai ta6a zuwa ba.
Da yake da wayo yake yin tambayar ba a fili yake fitowa ya bayyana manufar sa ba...misali ranar da zai fara yin tambayar aranar wani friend 'din sa yazo wurin sa ne sai da ya daidaici 'karfe biyu tayi sai ya jashi suka fito wajen gida suka zauna kamar da gaske, daka yanzun 'karfi da yaji yake tilastawa kansa zaman waje kawai dan ya ganta yaji sanyi cikin ransa..wani sa'in ma idan ya fito sallar azahar baya ta6a komawa gida koda kuwa 'karfe nawa zai kai a wurin to bazai ta6a shigewa ba sai yaga giftawar ta...(ni kuwa nace...aiki ya kama gwari).
Suna zaune a wurin muka zo muka wuce bamu ma kula da su ba....
Ashe Deen kam hankalin sa na kanmu sai ya koma ya kishingi'da ya wani lumshe idanu bazaka ta6a yin zaton yana ganin abu a hakan ba.
Shi 'dayan abokin Deen da bai san meke faruwa bane da wucewar mu sai ya girgiza kansa yace " Allah sarki...wallahi yarinyar nan na matu'kar bani tausayi...gata haka zaka ganta kamar lafiyayya amma wallahi kar kaso kaga wurin jinyarta, hankalin kowa sai ya tashi a dangin ta, gata da masifar shiga rai".
Ya 'karashe maganar da sanyin murya.
Mu'een na jin haka sai ya gyara zaman sa da kyau da mamaki yace da shi " wace kake magana akai wai?"
Juyawa yayi ya kallomu dan shi baya ya juya mana Yah Deen ka'dai ne ke facing da hanyar da muka bi.
" Nannen Malam Mamman nake magana akai...gasu can yanzun nan suka gifta mu 'yar doguwa mai hasken....ai kai bazaka sansu ba saboda ba'a garin kake zama ba shiyasa...
Yah Deen taran shi yayi da fa'din " to wani irin suna ne kuma Nanne?"
Hannu wancan 'din ya 'dago yace kai dakata " cikakken sunan ta Amina Nannen kawai sunan gida ne".
Komawa yayi ya kishingi'da yana kallon abokin na sa kamar mai nazarin wani abu a hankali sai yace to me ke damun ta har haka da kace tana baka tausayi?"
" Ai kai de ka bari...wallahi sickler ce da ita abin tausayi yarinyar ni ai badan hakan ba wallahi sai na nemi auren ta yarinyar akwai natsuwa tun tana 'yar 'karamar ta".
Idanun sa ya miyar ya limshe su a hankali cikin ransa yace " gara hakan ai, kaga ni sai na nemi auren ta in kula da ita....."
A fili kuwa " Allah yata lafiya" kawai ya furta daga nan bai 'kara fa'din komai ba.
A ranar ne Mu'een yasan haka game da Nannen mu....to ko ranar da yaga gidan mu ma sanadin wani da suke ha'duwa a filin ball ne ya sa mu ganin gidan da yamma bayan sun tashi daga ball 'din sai hanya ta biyo da su ta wurin anan yaga Nannen mu ta fito daga ma'kwabta ta shiga gida.
Shi 'dayan bai ma kula da ita ba Yah Deen ne ka'dai ya lura da hakan.
Basarwa yayi sai da ta shige gidan kafin ya tambaye shi wai wannan gidan...gidan waye ne?"
" Gidan Malam Mamman ne...me ya faru?"
Abokin ya 'karasa da tambaya, Mu'een sai yace " bakomai".