← Book details Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 69 OF 211

Sashe 69

Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

" Yi ha'kuri to".
Ya fa'di tare da matsowa kusa da ni sannan ya sake fa'din" Allah ya taimake ki yarinya".
Yayi maganar yana kallo idanu na.
   Ban amsa shi ba sai kawai nace da shi" ina Ma'u?"
" An saka ta shara".
Ya bani amsa yana 'dan dariya.

" Maganin ta ai".
Nima na fa'da harda mugunta ta.
Au haka ma zakice ke da ta tazo taimakon ki...ai badan ita ba da ke za'a saka sharar".
Sai nace" Ba wani nan ai dama Ammi tace kar in shiga ciki".
"  Naji to, muje ki taya ta"
Cewar Saif yana bani hanya.
Kafa'da na no'ke tare da 'kara matsawa baya.
Dariya ma bashi, sai da yayi dariyar kafin yace " Allaj kin fiya tsoro, nima fa an min masifar nan amma kin gani a jikina ne...mazgewa akeyi in ba haka ba bazaki daina tsoron nan ba".

" Ni dai ba ruwa na, ka 'kirata mu tafi ko kuma muyi tafiyar mu idan ta gama sai ta wuce itama".

" Rufa min asiri ni kam in ba so kike ya 6a66alani ba...bari in dubo ta".
Yana gama fa'din hakan ya juya ya shige ciki.

Lokacin da ya shiga sai ya samu ma har ta gama sharan tana kwashewa.

Sannu yayi mata sannan ya wuce ya ha'do abubuwan da za'ayi mopping 'din dasu.
      Ga mamakin  Saif fuskar Ma'u cike take da murmushi, sa6anin yanda ya zaci zata ji haushin ta rako su kuma an saka ta aiki.

Bai damu ba ya wuce ya fara goge 'dakin, sai tayi saurin tasowa ganin abinda yake shirin yi tace.." Me zakayi?"
" Wai da zan tayaki ne"
" Banso..nace ka taya ni ne?" tayi maganar tana kar6a daga hannun sa.
Saif baki ya ta6e yaja gefe ya tsaya yana binta da kallon mamaki.

Comment
Vote
Share

*Salmerh ce*😍

💕 *NOORUL* 💕
      (Haske nah)

By
*Salmerh MD*

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

*Dedicated to Hassan ATk & 80k...Allah ya bar Zumunci ya biya bu'katu...( Amin thumma Amin)* 😍

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *35*

Haka tayi abinta ita ka'dai har ta kammala goge tiles 'din tas,.

" Sannu".
Saif yayi mata sannan ya shiga ciki dan sanar da shi zasu wuce sai kuma ya tarar yana bayi ne a lokacin.

Saif kam hakan ma yafi masa, dan bai son wata sabuwar mitar kuma da yake baya rasa na yi shi. { a fa'dar Saif kenan}… 
  Dalilin ma kenan da ya sanya batare da 6ata wani lokaci ba ya fito yace da Ma'u wai yace ya gode za su iya tafiya.

Ma'u kam ba haka taso ba dan taso ta 'kara ganin fuskar sa ma ko da kuwa ace wata masifar zai kuma yi mata… amma ganin bata samu hakan ba sai kawai ta basar suka fito daga gidan inda suka suka same ni tsaye tsuru-tsuru duk na gaji da jiran su, sosai na 'kosa su fito muyi gaba.

     Ai kuwa ina ganin sun fito sai na saki hamdala a zuciya ta a fili kuwa ajiyan zuciya na sau'ke har ina lumshe idanu.
"...Kamo ta nan".
Naji muryar Saif ya fa'di da 'dan 'karfi.

A firgice nayi baya da niyyar kwasa da gudu kawai sai naji sun kwashe da dariya atare suna nuno ni, baki na tura ina 'dan kalle-kalle dan harga Allah ni tsorata nayi.
" Y'ar gidan Ammi matsoraciya".
Cewar Saif bayan ya gama dariyar tasa.

" Ni dai kam kuzo mu tafi".
Nayi maganar tare da juyawa na fara tafiya ina 'dan 'kun'kuni.

A hanya daf da zamu sha kwana muka ci karo da manyan shanukai masu yawa ga dukkan alamu kiwo suka nufa.

Wannan karan Ma'u tafi kowa tsorata musamman da yake itace agaba .

Ihu ta tsala cike da firgici tare da komawa da baya ta ranta ana kare....duk sai muka bita da idanu da mamaki, hakan yasa kafin mu ankare sun mana 'kawanya sai ganin mu kanmu muka yi a tsakanin su.

Ganin hakan ya sanya ni daskarewa wuri guda tare da rintse idanu na da karfin gaske.

Saif kam mai zai yi in ba dariya ba, Ma'u kuwa bata tsaya ko ina da gudun ba sai gidan Yah Deen....tana tura 'kofar sai suka ci karo da shi da yake 'ko'karin fita, bata lura da shi ba har sai da suka yi wata irin gwabzuwa gaba 'daya ta fa'da jikin sa har tana shirin kayar da shi.

Jinta jikin mutun ne ya sanya ta 'kara ru'kun'kume shi da karfin gaske.

Yah Deen kam mamaki, 6acin rai da takaici ne duk suka cika shi, sai hakan basu yi wani tasiri a zuciyar sa ba fiye da yanda yaji tudun boobs 'din ta ajikin sa nan hankalin sa yafi tafiya duk da kuwa bai gane ko wacece ba balle yasan manufar ta nayin hakan.

Da 'kyar yayi 'ko'karin raba jikin sa da nata bayan shu'dewan kusan mintina uku suna a hakan jin yanda wani abu ke shirin taso masa.

Bai iya yaui mata masifa ba balle wani abu kawai sai tsintan kansa yayi da tambayar ta abinda ya faru bayan fahimtar ko wacece, cuz kallo daya yayiwa fuskar ta ya gane cewa itace suka zo da Saif mintina 'kalilan da suka wuce.

" Shanu".
Da yaji ta fa'da ne ya sanya shi matsawa ya le'ka 'kofar sai yaga ma har sun wuce sauran basu fi uku ba.

   Dawo da kansa ciki yayi batare da ya kale ta ba yana duba jikin sa ya furta" sun wuce".
Itama Ma'u le'kawa tayi sannan ta sa kai ta fice tuni farin cikin ta ya kori tsoron kaf, ganin cewa da shi ta ha'du har ma yayi mata magana cikin natsuwa ba tare da tsangwama ba.

   Tafiya take a hankali tana sakin murmushi, ita ka'dai ta san da'din da taji ayau kuma take kanji har cikin zuciyar ta, a ranta take faman maimaita kalaman da yai mata ayau 'din...tambayar ta da yayi " Me yafaru" da kuma " sun wuce " 'din da ya fa'di...sosai suka tsaya mata arai suke kuma sata nisha'di....da haka har ta isa wurin mu ni da Saif da ke ta faman yi min dariya wai dan na tsorata...sai dai ganin dawowar Ma'u ya sanya dariyar tasa ta koma kanta wai ita kuma 6acewa tayi 6at da ganin shanayen sai aka rasa ta.

Ni kam baki na tura bance da shi komai ba haka ma Ma'u kamar ha'din baki...kawai muka cigaba da tafiyar mu.

'Bangaren Yah Deen kuwa fasa fitan yayi ya koma ciki kan kujera ya zauna tare da dafe kansa a 'ko'karin sa na saita yayanin sa, amma ya kasa  daina jin tudun 'kirjin ta a jikin sa...sai daga baya ma ya fara jin haushin kansa da har ya biyewa zuciyar sa bai saisaitawa yarinyar nan zama ba....(daga baya kenan). 

Har muka rabu da ita Saif nayi mana dariyar harda ta mugunta, sai da har muka rabu da Ma'u kowa ya kama hanyar gida kafin ya tuna da 'dagun murya yace " Na manta Ma'u matsoraciya...mun gode fa ".
Ma'u batace da shi komai ba kawai ta cigaba da tafiyar ta tana ji har cikin ranta cewa batayi komai dan a gode mata ba tayi ne kawai saboda sanyin ranta wato Yah Deen.

Koda muka je gida kuwa babu wanda ya sanar da Ammi abinda ya faru duk da kuwa har a lokacin idan muka ha'da ido da Saif sai in ga yana min murmushin mugunta, da abin ya ishe ni shine naje na sanar da Ammi tamkar zanyi kuka ita kuwa tace kar ya 'kara min dariya ai tsoro halak ne ba laifi bane dan na tsorata da ganin shanaye tace ko ita ma ai tsoron nasu take ji.
   Jin abinda Ammi ta fa'di ne yasa na saki raina har ma na fara murmushi nima na jin da'din an bi baya na.

   Sai yamma Yah Deen yazo gidan anan yake ce da Ammi ta dinga tura ko mai yi mata aiki ne tana gyara can gidan saboda 'kura na yin yawa.

Hararan sa Ammi tayi sannan tace " ni na tura ka can 'din nace ka zauna ne?"

" Haba Ammi na...".
Ya fa'di yana rausayar da kansa gefe.
Ammi sai tace
" Kaida ka guje mu saboda me zan dinga wahalar da mutane a kanka?"
" Allah Ammi ba haka bane yaran kin nan ne sun fiya surutu kuma kinga ina karatu ne shiyasa".
" Kaide ka sani".
Ammi tace gami da mi'kewa ta bar shi wurin.

  Murmushi kawai yayi ya koma ya kishingi'da har Ammi ta dawo da ha'da'd'iyar juice 'din Abarba da ta ha'da 'dazu da bama nan ta kawo masa.

*****
      Ammi bata tura kowa ba har sai da aka kwana uku da maganar wanda ganin shiru ya sanya shi sake tuna mata kafin nan ta turani ni da Nana mai aikin ta muka je.

Ni kam da muka shiga gidan a varanda na tsaya ita ka'dai tayi sallama, da yace a shigo sai ta shiga, bai san ma da ni akazo ba har sai da ya fito da niyyar fita ya bar gidan sannan ya ganni tsaye a wurin ina ta wasa da hannu na.

Turus yaja ya tsaya da mamaki yace.
" ke kuma fa?"
Inda yayi maganar yana kallo na.

Take sai tsoro ya kamani na kasa ce dashi komai tamkar wacce ta ga dodo a gaban ta.

_".....A a fa Yayah...Ammi ce ta aiko mu da Hudah ita kuma wai tsoro take ji....."_ Maganar Saif ta rannan ne da ya tuna ya sashi sakin tsaki kawai yayi gaba....dan ya gano dalilin tsayuwar tawa a wurin.

Ni kam ajiyar numfashi na sauke har ina dafe 'kirjina ganin ya wuce batare da ya 'kara tanka ni ba.

Har ya kusan fita sai kuma ya tsaya sannan ya waigo ya kalle ni yace " Idan kun gama ku rufe ko'ina ki wuce min da keys 'din can gida zanje na kar6a acan".

Kai kawai na 'daga sama alamar " to" sannan nayi 'kasa da kaina.
Shi kam juyawa yayi ya fita abinsa ba tare da ya 'kara fa'din komai ba.
Chapter 69 · 0% Book details