Sashe 54
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
'Karfe biyar da rabi suka baro lambun shida Alhaji, da 'kafa suke tafiya suna 'dan ta6a hira anan Alhaji Baba yake 'kara yi masa Nasiha game da rayuwar mu ta yanzu, inda ya ringa buga mai misalai da dama musamman ma irin wancan abinda ya ta6a faruwa da shi har ajiyayyen ciwon sa ya tashi masa......Alhaji yace " ina fa'da maka hakane dan nasan ba kowani lokaci bane zangan ka har in gaya maka hakan, saboda bama tare da kai, yanzun ma nasan da kasamu makarantar akan lokaci nasan da zai yi wuya mu ganka...."
Sai yace
" Haba Alhaji Baba..ai da da yanzu ba 'daya bane, zan dinga zuwa akan lokaci insha Allahu....ni dama zanyi aure na anan garin ai kaga babu batun rabuwa da ku ko?"
Ya 'karashe maganar da tsokana.
Murmushi Alhaji Baba yayi tare da fa'din " aure a garin nan....?"
Kai ya 'daga masa sama yana murumshi tamkar wani yaro...sai Alhaji yace " a ina kaganta dan nasan ka ga wacce tayi maka ne shiyasa ka fa'di haka".
" Ai kaman kasani Alhaji...dama inaso in baka amanar ta kafin in tafi..."
"Da yake ni kakan kane ko...?"
" ah ah ni dai dan Allah Alhaji Baba kar kabari a aurar da ita ma wani, ina kammala karatuna zan dawo ka nema min auran ta ".
" Baka da kunya Muhammad, ni ne zan yi ma gadin wacce kake so?"
Shagwa6e fuska yayi tare da rausayar da kansa gefe yace " please....please Alhaji... in ba haka ba kuma to kawai ka tanadi likkafani ka ajiye tun yanzu!".
" Ja'irin yaro...mu ai namu shan gumba ne kawai".
" um-um dai Alhaji gara asha biki da gumban nan, ai nasan kaima baka so in mutu tun yanzu ko ba haka ba?"
Alhaji 'yar dariya yayi sannan ya sake fa'din
" idan tazo na isa in hana ne Muhammad?"
" Allah yasa mu dace...amma ni dai please Alhaji na baka amana idan ka'ki kuma zanje in bawa Ammi na kawai".
" Da yafi maka"
Alhaji ya fa'di cikin nuna halin ko in kula....Zabura Mu'een yayi yace " haba Alhaji wai da gaske kake yi ne....ni fa gaskiya kai nake so saboda kai zaka fi kulamin da kyau...kaga idan kaji za'a min sakiyar da ba ruwa sai ka shigar da magana ta kawai amma Ammi ai kullum tana gida ina zata san meke faruwa".
Shi kam Alhaji Baba sosai yake mamakin jin wannan zancen daga bakin Muhammad 'din sa....dan ya tsokane shi sai yace " to ka bari sai munyi magana Ja'afar".
" Subhanallah "
ya furta da sauri har da kame bakinsa " Uncle Ja'afar dai?
Cikin shagwa6e murya ya 'kara fa'din" Haba Alhaji Baba kanason in sha masifa ne hala, ai kasan halin Uncle Ja'afar ba sau'ki kuma wannan fa sirrine tsakanin mu dan Allah be serious mana".
Ya 'karashe maganar kamar zaiyi kuka.
Alhaji sassautawa yayi ganin dagske fa yake sai ya tambaye shi
"...to wace yarinya ce?"
Cike da farin ciki yace " yess...." harda watsa hannayen sa.
Da sauri Alhaji Baba ya kalle shi sai yace " to na fasa"
Tuni ya nutsu yace
" ah ah no yi ha'kuri Alhaji......sunan ta Amina amma anace mata Nanne...mahaifin ta kuma wai sunan sa Malam Mamman, gidan su na can 'kasan...ya 'karashe da yiwa Alhaji kwatancen gidan mu.
_Comment,Vote nd Share please_ 👏🏻
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *27*
Da yamman ranar kuwa babu islamiya da yake ranar Alhamis ne kuma bama zuwa, ranar ma ni da Nanne muka kai marka'den shinkafar wainar Ummahn mu...da kuma gya'da dayake yau d'in harda gya'da ta gyara shiyasa muka tafi mu biyu, dama ranar da duk za'ayi markaden gya'da ne muke tafiya mu biyu idan kuwa marka'da'd'iyar gya'dar Ummah bata kare ba ni ka'dai ke zuwa in marka'do mata shinkafa.
A hanyar mu ta dawowa muna tafiya muna 'yar hira, wani sa'in kuma fa'da mukeyi da ita dan ni nawi ya dame ni sosai yayin da ita kuma take faman jan 'kafa tafiyar ta kamar dan dole take yin sa.
Burina tayi sauri mu wuce gida ita kuma ta'ki a hankali take tafiyar ta kamar yanda ta saba.
Cikin shirin zuwa ball yazo ya gifta mu ban sani ba ko bai gane ni amma ni kam sau 'daya na kalle shi amma sai na gane shi.
Sai da ya wuce ne sannan Nanne tace da ni " tab amma wannan yana da kyau gaskiya".
" Waye wai wancan ?"
Na tambaye ta gami da nuna shi da bakina cuz da duk biyun hannaye na ri'ke roban dake kaina.
Nanne sai tace " ehh mana koke baki ganshi ba "
Juyawa nayi na cigaba da tafiyata sannan nace
" Na ganshi mana... 'dan gidan Alhaji Baba ne, mugunta ce dashi ingaya miki sosai".
Baki kawai Nanne ta ta6e bata 'kara magana ba, daga nan kuwa muka cigaba da tafiyar mu.
Na kanyi gaba in barta dan yanayin tafiyar mu ba 'daya bane da ita sam...ban sani bama ashe Nanne kam hankalin ta duk ya koma kan Yah Deen ne, tafiya take tana waigen sa lokaci-lokaci....ni kuwa dake gaban ta bansan hakan ba sam....bazata kawai naji karan fa'duwan abu...waigowata kawai sai naga ashe marka'den dake kan Nanne ne ya kife gaba d'aya sanadin tuntu6e da tayi.....ido na zaro na kalli marka'den sannan na kalle ta...." ta6'di Nanne marka'den wainar kika zubar?"
Sai tace dani " ai tunt6e nayi ban kula ba".
" To ki 'dauko robar mutafi gida...."
Hannu ta kai ta dago robar sai muka ga ashe itama ta face yayin da marfin ta yake nan garau jefe a gefe guda.
" ko zamu 'dan kwasa ka'dan?"
Nanne ta fa'da tana kallona" Sai nace kamamin mu sau'ke to sai in tayaki".
" ka'dan muka kwasa muka bari dan gaba d'aya ya lalace a wurin ba zai 'kara amfani ba.
Koda muka je gida kuwa Ummah bata ce komai ba jin cewa Nanne ce ta zubar kawai sai ta kar6i wanda muka kwasa 'din ta ha'da da ruwa da dama ta baiwa ragunan Baban mu suka shanye abinsu.....wannan dalilin ne ya sanya washegari bata yi waina ba harma da kunun baki d'aya.....sanadin kallon Deen da Nanne keyi wanda a lkacin ita kanta ma bazata iya shaidar ya san da zaman ta a duniya ba ko a'a duk da kuwa ha'duwar su da shi ta biyu kenan inda yau.
*****
Tsananin yanda Deen ya saka Nanne cikin zuciyar sa ya sanya kafin sati har ya nemi duk wasu bayanan da ya kamata ya sani game da ita, cikakken sunan ta da sunan mahaifin ta harma da gidan su duk ya sani amma bai ta6a zuwa ba.
Da yake da wayo yake yin tambayar ba a fili yake fitowa ya bayyana manufar sa ba...misali ranar da zai fara yin tambayar aranar wani friend 'din sa yazo wurin sa ne sai da ya daidaici 'karfe biyu tayi sai ya jashi suka fito wajen gida suka zauna kamar da gaske, daka yanzun 'karfi da yaji yake tilastawa kansa zaman waje kawai dan ya ganta yaji sanyi cikin ransa..wani sa'in ma idan ya fito sallar azahar baya ta6a komawa gida koda kuwa 'karfe nawa zai kai a wurin to bazai ta6a shigewa ba sai yaga giftawar ta...(ni kuwa nace...aiki ya kama gwari).
Suna zaune a wurin muka zo muka wuce bamu ma kula da su ba....
Ashe Deen kam hankalin sa na kanmu sai ya koma ya kishingi'da ya wani lumshe idanu bazaka ta6a yin zaton yana ganin abu a hakan ba.
Shi 'dayan abokin Deen da bai san meke faruwa bane da wucewar mu sai ya girgiza kansa yace " Allah sarki...wallahi yarinyar nan na matu'kar bani tausayi...gata haka zaka ganta kamar lafiyayya amma wallahi kar kaso kaga wurin jinyarta, hankalin kowa sai ya tashi a dangin ta, gata da masifar shiga rai".
Ya 'karashe maganar da sanyin murya.
Mu'een na jin haka sai ya gyara zaman sa da kyau da mamaki yace da shi " wace kake magana akai wai?"
Juyawa yayi ya kallomu dan shi baya ya juya mana Yah Deen ka'dai ne ke facing da hanyar da muka bi.
" Nannen Malam Mamman nake magana akai...gasu can yanzun nan suka gifta mu 'yar doguwa mai hasken....ai kai bazaka sansu ba saboda ba'a garin kake zama ba shiyasa...
Yah Deen taran shi yayi da fa'din " to wani irin suna ne kuma Nanne?"
Hannu wancan 'din ya 'dago yace kai dakata " cikakken sunan ta Amina Nannen kawai sunan gida ne".
Komawa yayi ya kishingi'da yana kallon abokin na sa kamar mai nazarin wani abu a hankali sai yace to me ke damun ta har haka da kace tana baka tausayi?"
" Ai kai de ka bari...wallahi sickler ce da ita abin tausayi yarinyar ni ai badan hakan ba wallahi sai na nemi auren ta yarinyar akwai natsuwa tun tana 'yar 'karamar ta".
Idanun sa ya miyar ya limshe su a hankali cikin ransa yace " gara hakan ai, kaga ni sai na nemi auren ta in kula da ita....."
A fili kuwa " Allah yata lafiya" kawai ya furta daga nan bai 'kara fa'din komai ba.
A ranar ne Mu'een yasan haka game da Nannen mu....to ko ranar da yaga gidan mu ma sanadin wani da suke ha'duwa a filin ball ne ya sa mu ganin gidan da yamma bayan sun tashi daga ball 'din sai hanya ta biyo da su ta wurin anan yaga Nannen mu ta fito daga ma'kwabta ta shiga gida.
Shi 'dayan bai ma kula da ita ba Yah Deen ne ka'dai ya lura da hakan.
Basarwa yayi sai da ta shige gidan kafin ya tambaye shi wai wannan gidan...gidan waye ne?"
" Gidan Malam Mamman ne...me ya faru?"
Abokin ya 'karasa da tambaya, Mu'een sai yace " bakomai".
Sai yace
" Haba Alhaji Baba..ai da da yanzu ba 'daya bane, zan dinga zuwa akan lokaci insha Allahu....ni dama zanyi aure na anan garin ai kaga babu batun rabuwa da ku ko?"
Ya 'karashe maganar da tsokana.
Murmushi Alhaji Baba yayi tare da fa'din " aure a garin nan....?"
Kai ya 'daga masa sama yana murumshi tamkar wani yaro...sai Alhaji yace " a ina kaganta dan nasan ka ga wacce tayi maka ne shiyasa ka fa'di haka".
" Ai kaman kasani Alhaji...dama inaso in baka amanar ta kafin in tafi..."
"Da yake ni kakan kane ko...?"
" ah ah ni dai dan Allah Alhaji Baba kar kabari a aurar da ita ma wani, ina kammala karatuna zan dawo ka nema min auran ta ".
" Baka da kunya Muhammad, ni ne zan yi ma gadin wacce kake so?"
Shagwa6e fuska yayi tare da rausayar da kansa gefe yace " please....please Alhaji... in ba haka ba kuma to kawai ka tanadi likkafani ka ajiye tun yanzu!".
" Ja'irin yaro...mu ai namu shan gumba ne kawai".
" um-um dai Alhaji gara asha biki da gumban nan, ai nasan kaima baka so in mutu tun yanzu ko ba haka ba?"
Alhaji 'yar dariya yayi sannan ya sake fa'din
" idan tazo na isa in hana ne Muhammad?"
" Allah yasa mu dace...amma ni dai please Alhaji na baka amana idan ka'ki kuma zanje in bawa Ammi na kawai".
" Da yafi maka"
Alhaji ya fa'di cikin nuna halin ko in kula....Zabura Mu'een yayi yace " haba Alhaji wai da gaske kake yi ne....ni fa gaskiya kai nake so saboda kai zaka fi kulamin da kyau...kaga idan kaji za'a min sakiyar da ba ruwa sai ka shigar da magana ta kawai amma Ammi ai kullum tana gida ina zata san meke faruwa".
Shi kam Alhaji Baba sosai yake mamakin jin wannan zancen daga bakin Muhammad 'din sa....dan ya tsokane shi sai yace " to ka bari sai munyi magana Ja'afar".
" Subhanallah "
ya furta da sauri har da kame bakinsa " Uncle Ja'afar dai?
Cikin shagwa6e murya ya 'kara fa'din" Haba Alhaji Baba kanason in sha masifa ne hala, ai kasan halin Uncle Ja'afar ba sau'ki kuma wannan fa sirrine tsakanin mu dan Allah be serious mana".
Ya 'karashe maganar kamar zaiyi kuka.
Alhaji sassautawa yayi ganin dagske fa yake sai ya tambaye shi
"...to wace yarinya ce?"
Cike da farin ciki yace " yess...." harda watsa hannayen sa.
Da sauri Alhaji Baba ya kalle shi sai yace " to na fasa"
Tuni ya nutsu yace
" ah ah no yi ha'kuri Alhaji......sunan ta Amina amma anace mata Nanne...mahaifin ta kuma wai sunan sa Malam Mamman, gidan su na can 'kasan...ya 'karashe da yiwa Alhaji kwatancen gidan mu.
_Comment,Vote nd Share please_ 👏🏻
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *27*
Da yamman ranar kuwa babu islamiya da yake ranar Alhamis ne kuma bama zuwa, ranar ma ni da Nanne muka kai marka'den shinkafar wainar Ummahn mu...da kuma gya'da dayake yau d'in harda gya'da ta gyara shiyasa muka tafi mu biyu, dama ranar da duk za'ayi markaden gya'da ne muke tafiya mu biyu idan kuwa marka'da'd'iyar gya'dar Ummah bata kare ba ni ka'dai ke zuwa in marka'do mata shinkafa.
A hanyar mu ta dawowa muna tafiya muna 'yar hira, wani sa'in kuma fa'da mukeyi da ita dan ni nawi ya dame ni sosai yayin da ita kuma take faman jan 'kafa tafiyar ta kamar dan dole take yin sa.
Burina tayi sauri mu wuce gida ita kuma ta'ki a hankali take tafiyar ta kamar yanda ta saba.
Cikin shirin zuwa ball yazo ya gifta mu ban sani ba ko bai gane ni amma ni kam sau 'daya na kalle shi amma sai na gane shi.
Sai da ya wuce ne sannan Nanne tace da ni " tab amma wannan yana da kyau gaskiya".
" Waye wai wancan ?"
Na tambaye ta gami da nuna shi da bakina cuz da duk biyun hannaye na ri'ke roban dake kaina.
Nanne sai tace " ehh mana koke baki ganshi ba "
Juyawa nayi na cigaba da tafiyata sannan nace
" Na ganshi mana... 'dan gidan Alhaji Baba ne, mugunta ce dashi ingaya miki sosai".
Baki kawai Nanne ta ta6e bata 'kara magana ba, daga nan kuwa muka cigaba da tafiyar mu.
Na kanyi gaba in barta dan yanayin tafiyar mu ba 'daya bane da ita sam...ban sani bama ashe Nanne kam hankalin ta duk ya koma kan Yah Deen ne, tafiya take tana waigen sa lokaci-lokaci....ni kuwa dake gaban ta bansan hakan ba sam....bazata kawai naji karan fa'duwan abu...waigowata kawai sai naga ashe marka'den dake kan Nanne ne ya kife gaba d'aya sanadin tuntu6e da tayi.....ido na zaro na kalli marka'den sannan na kalle ta...." ta6'di Nanne marka'den wainar kika zubar?"
Sai tace dani " ai tunt6e nayi ban kula ba".
" To ki 'dauko robar mutafi gida...."
Hannu ta kai ta dago robar sai muka ga ashe itama ta face yayin da marfin ta yake nan garau jefe a gefe guda.
" ko zamu 'dan kwasa ka'dan?"
Nanne ta fa'da tana kallona" Sai nace kamamin mu sau'ke to sai in tayaki".
" ka'dan muka kwasa muka bari dan gaba d'aya ya lalace a wurin ba zai 'kara amfani ba.
Koda muka je gida kuwa Ummah bata ce komai ba jin cewa Nanne ce ta zubar kawai sai ta kar6i wanda muka kwasa 'din ta ha'da da ruwa da dama ta baiwa ragunan Baban mu suka shanye abinsu.....wannan dalilin ne ya sanya washegari bata yi waina ba harma da kunun baki d'aya.....sanadin kallon Deen da Nanne keyi wanda a lkacin ita kanta ma bazata iya shaidar ya san da zaman ta a duniya ba ko a'a duk da kuwa ha'duwar su da shi ta biyu kenan inda yau.
*****
Tsananin yanda Deen ya saka Nanne cikin zuciyar sa ya sanya kafin sati har ya nemi duk wasu bayanan da ya kamata ya sani game da ita, cikakken sunan ta da sunan mahaifin ta harma da gidan su duk ya sani amma bai ta6a zuwa ba.
Da yake da wayo yake yin tambayar ba a fili yake fitowa ya bayyana manufar sa ba...misali ranar da zai fara yin tambayar aranar wani friend 'din sa yazo wurin sa ne sai da ya daidaici 'karfe biyu tayi sai ya jashi suka fito wajen gida suka zauna kamar da gaske, daka yanzun 'karfi da yaji yake tilastawa kansa zaman waje kawai dan ya ganta yaji sanyi cikin ransa..wani sa'in ma idan ya fito sallar azahar baya ta6a komawa gida koda kuwa 'karfe nawa zai kai a wurin to bazai ta6a shigewa ba sai yaga giftawar ta...(ni kuwa nace...aiki ya kama gwari).
Suna zaune a wurin muka zo muka wuce bamu ma kula da su ba....
Ashe Deen kam hankalin sa na kanmu sai ya koma ya kishingi'da ya wani lumshe idanu bazaka ta6a yin zaton yana ganin abu a hakan ba.
Shi 'dayan abokin Deen da bai san meke faruwa bane da wucewar mu sai ya girgiza kansa yace " Allah sarki...wallahi yarinyar nan na matu'kar bani tausayi...gata haka zaka ganta kamar lafiyayya amma wallahi kar kaso kaga wurin jinyarta, hankalin kowa sai ya tashi a dangin ta, gata da masifar shiga rai".
Ya 'karashe maganar da sanyin murya.
Mu'een na jin haka sai ya gyara zaman sa da kyau da mamaki yace da shi " wace kake magana akai wai?"
Juyawa yayi ya kallomu dan shi baya ya juya mana Yah Deen ka'dai ne ke facing da hanyar da muka bi.
" Nannen Malam Mamman nake magana akai...gasu can yanzun nan suka gifta mu 'yar doguwa mai hasken....ai kai bazaka sansu ba saboda ba'a garin kake zama ba shiyasa...
Yah Deen taran shi yayi da fa'din " to wani irin suna ne kuma Nanne?"
Hannu wancan 'din ya 'dago yace kai dakata " cikakken sunan ta Amina Nannen kawai sunan gida ne".
Komawa yayi ya kishingi'da yana kallon abokin na sa kamar mai nazarin wani abu a hankali sai yace to me ke damun ta har haka da kace tana baka tausayi?"
" Ai kai de ka bari...wallahi sickler ce da ita abin tausayi yarinyar ni ai badan hakan ba wallahi sai na nemi auren ta yarinyar akwai natsuwa tun tana 'yar 'karamar ta".
Idanun sa ya miyar ya limshe su a hankali cikin ransa yace " gara hakan ai, kaga ni sai na nemi auren ta in kula da ita....."
A fili kuwa " Allah yata lafiya" kawai ya furta daga nan bai 'kara fa'din komai ba.
A ranar ne Mu'een yasan haka game da Nannen mu....to ko ranar da yaga gidan mu ma sanadin wani da suke ha'duwa a filin ball ne ya sa mu ganin gidan da yamma bayan sun tashi daga ball 'din sai hanya ta biyo da su ta wurin anan yaga Nannen mu ta fito daga ma'kwabta ta shiga gida.
Shi 'dayan bai ma kula da ita ba Yah Deen ne ka'dai ya lura da hakan.
Basarwa yayi sai da ta shige gidan kafin ya tambaye shi wai wannan gidan...gidan waye ne?"
" Gidan Malam Mamman ne...me ya faru?"
Abokin ya 'karasa da tambaya, Mu'een sai yace " bakomai".