Sashe 60
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
".....Muhammad kar de kace min shirin zuwa wurin Amina kayi yanzun?"
Shiru Mu'een yayi bai iya yace da Alhajin komai ba kamar yadda bai iya cigaba da sake massaging gwiwar Alhajin ba illah ri'ke man da yayi yana kallon gefe....cuz shima zuwa yanzun ya fara jin bugun zuciyar sa na 'karuwa, fatan sa dai Allah ya sa alkhairi ne ke tunkaro sa, fargabar sa 'daya kar ace da shi an bada auren ta ga wani wanda ba shi ba.....
" Muhammad ka zauna ka saurare ni da kyau kaji...."
Yah Deen da jin haka sai ya d'ago ya kalle shi take y'ar guntuwar fara'ar da ta rage kan fuskar sa ta kau, dan ya fahimci akwai wani 6oyayyen abin daban da Alhaji Baba ke son sanar dashi wanda shi bai sani ba.
Jin cigaban maganar Alhajin ne ya dawo masa da tunanin sa, abinda ya tsinkaya cikin kunnuwan sa kuwa shine " Amina...fa ta jima da komawa ga mahallicin ta...."
Kallon da Yah Deen ya cigaba da yi masa ne ya sanya shi 'karawa da fa'din " ...ma'ana Amina ta rasu Muhammad sanadiyyan tashin ciwon....."
Bugun zuciya mai karfi gami da fargaba ne suka ziyar ce shi lokaci guda...har ma bai san lokacin da ya 'dago hannun daman sa ya toshe bakin Alhaji Baba da shi ba....abinda kenan ya hana Alhaji Baba 'karasa maganar da yayi niyyan fa'da.
Cikin in ina yace " Dan Allah...Alhaji kar kayi....min irin wannan wasan, ba zan...iya jurewa ba....".
Ya 'karasa maganar da girgiza kansa.
Baya ka'dan Alhaji Baba yaja tare da cire hannun Mu'een daga kan bakin sa, Yah Deen sai yabi hannun sa da kallo sannan ya cigaba da kallon Alhajin wanda ya cigaba da fa'din.
" Duk da yake ina yi maka wasa Muhammad amma wannan bai kasance cikin abinda zan yaudare ka dashi ba, ai nine mahaifin ka, kai kanka kasan bazan so abinda zai ta6a rayuwar ka ba, miye ma ribar yin hakan idan nayi?....mutuwa sau 'daya tak ake yinta Muhammad kuma shi Amina tayi, and kai kanka kasan idan an mutu ba'a dawowa....kayi mata addu'ah kaji, na 6oye maka tuntuni ne saboda gudun irin halin da zaka shiga amma banyi hakan da wata manufa ko kuma dan 6ata maka ba....."
Ido kawai ya tsurawa Alhajin, bama ya fahimtar komai, tuntuni maganar Alhajin ta farko take faman amsa kuwa cikin kunnuwan sa...... _" Mutuwa 'daya tak akeyi Muhammad kuma shi Amina tayi_ "..... abinda ke nan yake ta yi masa yawo a tsakar kansa.
Bai iya ya sake motsa ko da 'dan yatsan sa ba ne, sakamakon jin kalaman Alhajin cikin tabbatar wa, take 'kirjin sa ya ri'ke shi ga bugu da zuciyar sa keyi tamkar zata fito fili, bai ankara ba sai jin sau'kan hawaye yayi saman fuskar sa.
Bai damu da hakan ba kawai ya cigaba da kallon Alhajin cikin rawar murya ya nuna kansa sannan ya bu'di baki da 'kyar yake fisgan maganar yace" Alhaji...kana nufin...Amina Amina....ta rasu... tuntuni kuma ban sani ba?"
Kai Alhajin ya jinjina masa alamar tabbatar wa.....
Take sai ya kai hannayen sa ya dafe kansa da yake jin yana juya masa ha'di da barazanar tarwatsewa, ga 'kirjin sa da ya yi masa nawi sosai jikin sa na faman kakkarwa.....kafin Alhaji yayi wani yun'kuri sai ji yayi ya saki 'kara mai 'karfi sannan ya saki kan ya dafe 'kirjin sa da duka hannuwan sa biyu hawaye na cigaba da bin kuncin sa.
~Kwana biyu kun jini shiru nima na rama ne~ 🤪
_Comment_
_Share_
_Vote_
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *31*
'Karan da yayin ne ya janyo hankalin mu gaba 'daya, Ammi da dama take kan hanyar zuwa gurin Alhajin sai tayi saurin 'karasawa ciki.
A rikice ta shigo tana tambayar Alhajin " me ke faruwa?"
Alhaji Baba ri'ke yake da hannun Deen yana 'ko'karin kwantar masa da hankali amma ina sam ya rasa nutsuwar sa.
Jin muryar Ammi da yayi ne ma ya sanya shi 'karfin halin mi'kewa cikin idanun sa cike taf da ruwan hawaye ya tsaya gaban Ammi.
Hannun ta na dama ya kamo ya 'daura saman 'kirjin sa saitin zuciyar sa yace " Ammi...kiji bugun zuciya ta, kiji irin 'ka'k'karfan soyayyar da nake yi mata...Ammi dan girman ki tausaya min kar kice min dagaske ne Amina ta rasu...Nanne ta tafi ta barni Ammi dagaske ne...?"
Sai yanzun hawayen sa suka gangaro kan kuncin sa, yana jin hakan amma bai kula ba still hankalin sa na wurin Ammi yana sauraran jin amsar bakin ta...Ammi kam duk jikin ta yayi sanyi bata ma san me zata ce da shi ba, bata san abin nasa har haka ya girmama ba, Muhammad 'din ta ne yau yake kuka da hawayen sa, kuma kukan ma akan mace.
Tsura masa idanu tayi tana kallon sa, tausayin sa na sake ratsa ta ji take tamkar ta taya shi kukan itama, amma tasan yin hakan tamkar ta fallasa asirin zuciyar ta ne.
Ganin kamar yana 'ko'karin sulalewa 'kasa ne ya sanya Alhaji saurin 'karasowa ya tallafo shi wanda sai a lokacin Ammi ma ta ankara da hakan a firgice ta ambaci sunan shi tana tallafan 'daya gefen nasa.
Kai Mu'een ya girgiza mata idanun sa lumshe batare da ya amsa sunan shin da ta 'kira ba kawai ya fara fa'din ..."..me ya..sa..zaki tafi..ki barni?...Ammi me yasa...bata jira na dawo na sanar da ita 'dumbin soyayyar da na ke yi mata ba..."
" Haba Muhammad kai fa musulmi ne, me yasa kake fa'din irin wa'dannan kalaman...bacin kasan Allah ne ke da mutuwa ba mu ba".
Alhaji Baba yayi 'karfin halin fa'din hakan yana gyara masa kansa dake jikin sa.
Wasu hawayen ne suka sake gangaro masa da gudun su...idanun sa ya bu'de ya tsayar cak akan fuskar Alhaji Baba bakin sa na rawa da alamar magana yake son yi amma ya kasa saboda azabar dam'kar da zuciyar sa tayi masa da 'kyar ya iya fuzgan " Alhaji...dagaske....ta barni...?"
Kafin Alhaji yayi wani yun'kuri sai gani yayi Mu'een ya mi'ke sumamme a jikin sa.
Ammi kam tuni ta fara kukan itama cikin ranta take fa'din " wannan wani irin masifa ne?"
Ganin yanda ya mi'ke ne ya sanya ta rikice tafara fa'din _innalillahi wa inna ilaihi raji'un_ ... _Alhaji me yafaru what's wrong with him..?"_
Cikin sanyin murya Alhaji Baba yace " ki kwantar da hankalin ki please...ba wani abu bane he just fainted".
Yana shafa cikin hannun Yah Deen ya fa'di hakan batare da ya kalli Ammi ba...shi kansa ya kasa nutsuwa gaba 'daya hankalin sa ya tashi, dama irin abinda tuntuni yake gudu kenan shiyasa ma ya kasa sanar da shi tun farkon faruwar lamarin.
Ammi na jin cewa suma yayi ta tashi da sauri ta 'debo ruwa tana 'ko'karin she'ka masa Alhaji Baba ya dakatar da ita.
Da mamaki tace " me yasa kuma Alhaji...idan ansa masa ruwan zai ta shi ai".
Kai Alhaji ya girgiza mata sannan ya bu'kaci ta bashi wayar sa.
Wayar ta 'dakko masa yayi 'kira inda ya bu'kaci ganin wani likita dake unguwar tasu ya kuma sanar dashi abubuwan da yake so ya zo dasu sannan ya cire wayar daga kunnan sa ya ajiye ta gefe.
Daga nan ya dai-dai ta kwanciyar Mu'een 'din ya kasance straight bai ko saka masa pillow ba ya barshi a hakan illah cikin hannun sa da ya cigaba da shafawa...yana tuna abinda ya ta6a gaya masa ranar da ya bashi amanar ta....".... _dan Allah Alhaji kar ka bari a aurar da ita ma wani, ina kammala karatuna zan dawo ka nema min auran ta....please...please Alhaji!, in kuma ba haka ba to kawai ka tanadi likkafani ka ajiye tun yanzu_ ..."
Allah sarki....sosai tausayin sa ya 'kara kamashi ga tsoron halin da zai iya shiga sanadin hakan, jikin Alhaji Baba har rawa yakeyi ga gumin da ke faman keto masa, shi ka'dai ya san halin da yake ciki dalilin wannan lamari.
Ammi kam zama tayi daga bakin gadon Alhaji Baba ta rafka tagumi tana share hawaye tana kallon sa....amma tunanin ya tafi wani wuri ne can daban, tunanin har yaushe Muhammad ya san soyayya, yaushe ma ya fara son Amina da har zai 'dagawa kansa hankali saboda rasuwar ta....ko cikin ahalin ta babu wanda taga ya suma saboda rashin ta, ko ni da nake ta haukan damuwa da ita ban ta6a suma saboda rashin nata ba...amma dube shi, yana matashin saurayi da shi amma ji yanda ya maida kanshi saboda macen da ba ma tasan yana son ta ba..."
Sosai abin yake damun Ammi a zuci.
Ina daga parlour ni da su Saif muna zaune munyi jigum dan tun 'dazu da mukaji 'karar Yah Deen muka rage volume na Tv muka yi shiru, babu kuma wanda ya motsa daga inda yake illah hankulan mu da duk suka zama a tashe.... sallama muka ji daga bakin 'kofar parlour.
Zaidu sai ya tashi yaje ya bu'de...gami da gaishe shi.
Likitan da ke ri'ke da 'yar jakan aikin sa sai ya bu'kaci ganin Alhaji Baba.
Sai lokacin Zaidu ya bashi hanya ya shigo jin cewa Alhaji ne ya 'kira shi, yana maida 'kofar yana rufewa sai yake bani umarnin zuwa in yiwa Alhaji Baba magana.
Banyi musu ba na tashi da sauri na isa 6angaren Alhajin na tura 'kofa a hankali da sallama a bakina...babu wanda ya amsamin illah 'dagowa da sukayi suka kalle ni bansani ba ko sun amsa min a zuci...ni kuwa tunda idanu na ya sau'ka a kansa mi'ke sai hankali na ya tashi sosai, Nannen mu kawai na tuna ranar da ta rasu a hannu na wanda ya kasance shine rana na 'karshe da na ganta..tun daga lokacin akace Nannen mu wai rasuwa tayi, da gama wannan tunanin take sai hawaye ya fara bin kuncina, kuma still ina kallon sa ban kuma iya na furta komai ba.
Shiru Mu'een yayi bai iya yace da Alhajin komai ba kamar yadda bai iya cigaba da sake massaging gwiwar Alhajin ba illah ri'ke man da yayi yana kallon gefe....cuz shima zuwa yanzun ya fara jin bugun zuciyar sa na 'karuwa, fatan sa dai Allah ya sa alkhairi ne ke tunkaro sa, fargabar sa 'daya kar ace da shi an bada auren ta ga wani wanda ba shi ba.....
" Muhammad ka zauna ka saurare ni da kyau kaji...."
Yah Deen da jin haka sai ya d'ago ya kalle shi take y'ar guntuwar fara'ar da ta rage kan fuskar sa ta kau, dan ya fahimci akwai wani 6oyayyen abin daban da Alhaji Baba ke son sanar dashi wanda shi bai sani ba.
Jin cigaban maganar Alhajin ne ya dawo masa da tunanin sa, abinda ya tsinkaya cikin kunnuwan sa kuwa shine " Amina...fa ta jima da komawa ga mahallicin ta...."
Kallon da Yah Deen ya cigaba da yi masa ne ya sanya shi 'karawa da fa'din " ...ma'ana Amina ta rasu Muhammad sanadiyyan tashin ciwon....."
Bugun zuciya mai karfi gami da fargaba ne suka ziyar ce shi lokaci guda...har ma bai san lokacin da ya 'dago hannun daman sa ya toshe bakin Alhaji Baba da shi ba....abinda kenan ya hana Alhaji Baba 'karasa maganar da yayi niyyan fa'da.
Cikin in ina yace " Dan Allah...Alhaji kar kayi....min irin wannan wasan, ba zan...iya jurewa ba....".
Ya 'karasa maganar da girgiza kansa.
Baya ka'dan Alhaji Baba yaja tare da cire hannun Mu'een daga kan bakin sa, Yah Deen sai yabi hannun sa da kallo sannan ya cigaba da kallon Alhajin wanda ya cigaba da fa'din.
" Duk da yake ina yi maka wasa Muhammad amma wannan bai kasance cikin abinda zan yaudare ka dashi ba, ai nine mahaifin ka, kai kanka kasan bazan so abinda zai ta6a rayuwar ka ba, miye ma ribar yin hakan idan nayi?....mutuwa sau 'daya tak ake yinta Muhammad kuma shi Amina tayi, and kai kanka kasan idan an mutu ba'a dawowa....kayi mata addu'ah kaji, na 6oye maka tuntuni ne saboda gudun irin halin da zaka shiga amma banyi hakan da wata manufa ko kuma dan 6ata maka ba....."
Ido kawai ya tsurawa Alhajin, bama ya fahimtar komai, tuntuni maganar Alhajin ta farko take faman amsa kuwa cikin kunnuwan sa...... _" Mutuwa 'daya tak akeyi Muhammad kuma shi Amina tayi_ "..... abinda ke nan yake ta yi masa yawo a tsakar kansa.
Bai iya ya sake motsa ko da 'dan yatsan sa ba ne, sakamakon jin kalaman Alhajin cikin tabbatar wa, take 'kirjin sa ya ri'ke shi ga bugu da zuciyar sa keyi tamkar zata fito fili, bai ankara ba sai jin sau'kan hawaye yayi saman fuskar sa.
Bai damu da hakan ba kawai ya cigaba da kallon Alhajin cikin rawar murya ya nuna kansa sannan ya bu'di baki da 'kyar yake fisgan maganar yace" Alhaji...kana nufin...Amina Amina....ta rasu... tuntuni kuma ban sani ba?"
Kai Alhajin ya jinjina masa alamar tabbatar wa.....
Take sai ya kai hannayen sa ya dafe kansa da yake jin yana juya masa ha'di da barazanar tarwatsewa, ga 'kirjin sa da ya yi masa nawi sosai jikin sa na faman kakkarwa.....kafin Alhaji yayi wani yun'kuri sai ji yayi ya saki 'kara mai 'karfi sannan ya saki kan ya dafe 'kirjin sa da duka hannuwan sa biyu hawaye na cigaba da bin kuncin sa.
~Kwana biyu kun jini shiru nima na rama ne~ 🤪
_Comment_
_Share_
_Vote_
*Salmerh ce* 😍
💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)
By
*Salmerh MD*
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
🅿 *31*
'Karan da yayin ne ya janyo hankalin mu gaba 'daya, Ammi da dama take kan hanyar zuwa gurin Alhajin sai tayi saurin 'karasawa ciki.
A rikice ta shigo tana tambayar Alhajin " me ke faruwa?"
Alhaji Baba ri'ke yake da hannun Deen yana 'ko'karin kwantar masa da hankali amma ina sam ya rasa nutsuwar sa.
Jin muryar Ammi da yayi ne ma ya sanya shi 'karfin halin mi'kewa cikin idanun sa cike taf da ruwan hawaye ya tsaya gaban Ammi.
Hannun ta na dama ya kamo ya 'daura saman 'kirjin sa saitin zuciyar sa yace " Ammi...kiji bugun zuciya ta, kiji irin 'ka'k'karfan soyayyar da nake yi mata...Ammi dan girman ki tausaya min kar kice min dagaske ne Amina ta rasu...Nanne ta tafi ta barni Ammi dagaske ne...?"
Sai yanzun hawayen sa suka gangaro kan kuncin sa, yana jin hakan amma bai kula ba still hankalin sa na wurin Ammi yana sauraran jin amsar bakin ta...Ammi kam duk jikin ta yayi sanyi bata ma san me zata ce da shi ba, bata san abin nasa har haka ya girmama ba, Muhammad 'din ta ne yau yake kuka da hawayen sa, kuma kukan ma akan mace.
Tsura masa idanu tayi tana kallon sa, tausayin sa na sake ratsa ta ji take tamkar ta taya shi kukan itama, amma tasan yin hakan tamkar ta fallasa asirin zuciyar ta ne.
Ganin kamar yana 'ko'karin sulalewa 'kasa ne ya sanya Alhaji saurin 'karasowa ya tallafo shi wanda sai a lokacin Ammi ma ta ankara da hakan a firgice ta ambaci sunan shi tana tallafan 'daya gefen nasa.
Kai Mu'een ya girgiza mata idanun sa lumshe batare da ya amsa sunan shin da ta 'kira ba kawai ya fara fa'din ..."..me ya..sa..zaki tafi..ki barni?...Ammi me yasa...bata jira na dawo na sanar da ita 'dumbin soyayyar da na ke yi mata ba..."
" Haba Muhammad kai fa musulmi ne, me yasa kake fa'din irin wa'dannan kalaman...bacin kasan Allah ne ke da mutuwa ba mu ba".
Alhaji Baba yayi 'karfin halin fa'din hakan yana gyara masa kansa dake jikin sa.
Wasu hawayen ne suka sake gangaro masa da gudun su...idanun sa ya bu'de ya tsayar cak akan fuskar Alhaji Baba bakin sa na rawa da alamar magana yake son yi amma ya kasa saboda azabar dam'kar da zuciyar sa tayi masa da 'kyar ya iya fuzgan " Alhaji...dagaske....ta barni...?"
Kafin Alhaji yayi wani yun'kuri sai gani yayi Mu'een ya mi'ke sumamme a jikin sa.
Ammi kam tuni ta fara kukan itama cikin ranta take fa'din " wannan wani irin masifa ne?"
Ganin yanda ya mi'ke ne ya sanya ta rikice tafara fa'din _innalillahi wa inna ilaihi raji'un_ ... _Alhaji me yafaru what's wrong with him..?"_
Cikin sanyin murya Alhaji Baba yace " ki kwantar da hankalin ki please...ba wani abu bane he just fainted".
Yana shafa cikin hannun Yah Deen ya fa'di hakan batare da ya kalli Ammi ba...shi kansa ya kasa nutsuwa gaba 'daya hankalin sa ya tashi, dama irin abinda tuntuni yake gudu kenan shiyasa ma ya kasa sanar da shi tun farkon faruwar lamarin.
Ammi na jin cewa suma yayi ta tashi da sauri ta 'debo ruwa tana 'ko'karin she'ka masa Alhaji Baba ya dakatar da ita.
Da mamaki tace " me yasa kuma Alhaji...idan ansa masa ruwan zai ta shi ai".
Kai Alhaji ya girgiza mata sannan ya bu'kaci ta bashi wayar sa.
Wayar ta 'dakko masa yayi 'kira inda ya bu'kaci ganin wani likita dake unguwar tasu ya kuma sanar dashi abubuwan da yake so ya zo dasu sannan ya cire wayar daga kunnan sa ya ajiye ta gefe.
Daga nan ya dai-dai ta kwanciyar Mu'een 'din ya kasance straight bai ko saka masa pillow ba ya barshi a hakan illah cikin hannun sa da ya cigaba da shafawa...yana tuna abinda ya ta6a gaya masa ranar da ya bashi amanar ta....".... _dan Allah Alhaji kar ka bari a aurar da ita ma wani, ina kammala karatuna zan dawo ka nema min auran ta....please...please Alhaji!, in kuma ba haka ba to kawai ka tanadi likkafani ka ajiye tun yanzu_ ..."
Allah sarki....sosai tausayin sa ya 'kara kamashi ga tsoron halin da zai iya shiga sanadin hakan, jikin Alhaji Baba har rawa yakeyi ga gumin da ke faman keto masa, shi ka'dai ya san halin da yake ciki dalilin wannan lamari.
Ammi kam zama tayi daga bakin gadon Alhaji Baba ta rafka tagumi tana share hawaye tana kallon sa....amma tunanin ya tafi wani wuri ne can daban, tunanin har yaushe Muhammad ya san soyayya, yaushe ma ya fara son Amina da har zai 'dagawa kansa hankali saboda rasuwar ta....ko cikin ahalin ta babu wanda taga ya suma saboda rashin ta, ko ni da nake ta haukan damuwa da ita ban ta6a suma saboda rashin nata ba...amma dube shi, yana matashin saurayi da shi amma ji yanda ya maida kanshi saboda macen da ba ma tasan yana son ta ba..."
Sosai abin yake damun Ammi a zuci.
Ina daga parlour ni da su Saif muna zaune munyi jigum dan tun 'dazu da mukaji 'karar Yah Deen muka rage volume na Tv muka yi shiru, babu kuma wanda ya motsa daga inda yake illah hankulan mu da duk suka zama a tashe.... sallama muka ji daga bakin 'kofar parlour.
Zaidu sai ya tashi yaje ya bu'de...gami da gaishe shi.
Likitan da ke ri'ke da 'yar jakan aikin sa sai ya bu'kaci ganin Alhaji Baba.
Sai lokacin Zaidu ya bashi hanya ya shigo jin cewa Alhaji ne ya 'kira shi, yana maida 'kofar yana rufewa sai yake bani umarnin zuwa in yiwa Alhaji Baba magana.
Banyi musu ba na tashi da sauri na isa 6angaren Alhajin na tura 'kofa a hankali da sallama a bakina...babu wanda ya amsamin illah 'dagowa da sukayi suka kalle ni bansani ba ko sun amsa min a zuci...ni kuwa tunda idanu na ya sau'ka a kansa mi'ke sai hankali na ya tashi sosai, Nannen mu kawai na tuna ranar da ta rasu a hannu na wanda ya kasance shine rana na 'karshe da na ganta..tun daga lokacin akace Nannen mu wai rasuwa tayi, da gama wannan tunanin take sai hawaye ya fara bin kuncina, kuma still ina kallon sa ban kuma iya na furta komai ba.