Sashe 37
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
〰〰〰
...... Basu sani bama ashe ko wancan case 'din da ya faru da Tahir.... Lawyern ne ya assaso shi tunda ya samu labarin binciken da Tahir yayi akan sa sai ya rasa yadda zai yi ya 'kas'kantar da shi da rayuwar sa, ya so yasa akashe shi amma sai ya fasa ganin cewa managern Oando babban aminin sa ne, dalilin haka ya sanya suka shirya deal akan hakan da zummar idan an tuhume shi kan satan fuel dole zai biya ku'din komin yawan su, wanda dalilin hakan zaisa ragowar dukiyar dake hannun sa zata sami gi6i na gaske shikenan daga ranan koda zasu nemi karawa dashi they ll not win against him dan basu da komai, rayuwar yanzu kuwa sai kana da shi ake yi da kai.
Ku'din da zasu biya 'din kuma shi manager zai ri'ke sai lawyer ya cika masa ya zama 100million shi kenan deal 'din su ya 'kare daga nan.... amma 'karfin addu'ah da kuma rashin sabo da cin amana ya sanya manager rashin natsuwa bayan sun gama shirya komai, sai gashi kafin deal 'din nasu ya kammala da kansa ya bayyana cewa an samu ku'da'den...sai dai bai sanar da kowa cewa su suka shirya hakan ba.
'Bangaren Lawyer kuwa ganin ha'kar sa bata cimma ruwa ba a karon farko ganin hakan ne ya sanya shi canza tunani zuwa plan B.
*****
Bayan wasu kwanaki sai Oando suka rin'ka damun Tahir akan ya dawo bakin aikin sa, shi kuwa gaba 'daya aiki dasu ya fice masa arai harma ya fara 'ko'karin neman wani aikin a wani wajen daban.
Itama Aishatu bata goyi bayan ya koma can 'din ba haka ma Ja'afar, sai ma tace suje Kaduna su 'dan kwana biyu daga nan su duba gidajen mahaifin ta dake can 'din daga baya sai su dawo kafin nan ko zasu rage damun sa.
bai 'ki shawarar ta ba dan ko shima 'din yana so ya 'dan kauce ko ma dan ya huta, cuz tun bayan faruwar lamarin Kano ta bar ransa kwata-kwata.
Dalilin haka ne yasa washe gari suka wuce Kaduna su biyun su batare da kowa ya sani ba da yake ma har yanzu Mu'een na Azare gun Ja'afar shiyasa ya kasance su biyu ne sukayi tafiyar.
Sunje sunyi duk abubuwan da ya dace sun kuma huta 'din kamar yadda suka yi buri duk cikin sati 'daya, harma sun fara 'ko'karin dawowa da tunanin barin Kano su koma Kaduna da zama gaba 'day musamman ma da suka ga yanayin garin yayi musu ba laifi sai suke ganin zasu dasa sabuwar rayuwa a can 'din.
Ana jibi zasu tafi ne da safe lokacin Aishatu na 'dan fama da zazza6i ko Tahir ma bai san da zancen zazza6in ba yayin da ya shiga cikin gari tun safe ya manta wayar sa a hotel 'din da suke 'din.....Aishatu kuwa zafin zazza6i da ciwon kai da take ji bai barta ta iya koda motsawa ba, tana jin wayoyin su na faman ringing amma bata iya ta 'daga ko guda 'daya ba, duk kuwa da tayi mamakin yanda wayoyin ke faman ruri lokaci guda amma hakan bai sa ta 'dauki 'kiran ba.
'Ko'karin da tayi ma shine tashin da tayi ta kakkashe wayoyin batare da tabi ta kan 'kira ko 'daya ba.
Tsawon lokaci sannan ya dawo kusan shabiyu na rana sai da ma yayi sallahr Zuhr kafin yabi ta kan wayar inda ya tarar da ita a kulle... Yaso yayi mamaki amma kuma tuna cewa Aishatu ce ka'dai zatayi hakan ya sanya shi kunnawa kawai ya bar batun mamakin.
Kunnawar sa
keda wuya kuwa sai ya tsinci 'kiran Manager cikin wayar kamar dama jira yake yi ya kunna.. ...'dauka yayi da tunanin zai masa bayani na 'karshe dan zaton sa ko har yanzu akan komawar sa bakin aiki ne dan haka cikin ransa ya shirya maganar da zai gaya masa akan cewa shi ba zai iya sake yin aiki da su ba har abada......sai dai ga mamakin sa bai kai ga furta abinda ke cikin ransa ba shima 'din hankalin sa ya tashi, cuz yanda yaji muryar Manager cikin damuwa sosai ya sanya shi shiga firgici lokaci guda.
Jikin sa sanyi yayi da ya sau'ke wayar daga kunnen sa, koda Aishatu ta tambaye shi ma bai iya yace da ita komai ba dan gudun 'daga hankalin ta.
Wannan dalilin ne ya sanya shi mantawa da duba sauran tarin missedcalls 'din da akayi masa.
Aranar ya wuce Kano batare da ta sani ba.
Manager ne yayi masa kwatancen inda zai same shi batare da 6ata lokaci ba kuwa ya wuce gurin saboda har yanzun baiji hankalin sa ya kwanta ba tun bayan da suka yi waya da manager a Kaduna.
Ba 'karamin mamaki yayi ba da yaji abinda Manager yace cikin 6oye ko wanene ke abin yayi masa bayani a ta'kaice kan cewa babban abokin sa ke neman ran Tahir 'din da iyalan sa ma gaba 'daya.
Tun jiya wai ake zarya a gidan sa har wayewar garin yau amma basu samu kowa a gidan ba kuma rashin ganin ahalin gidan ya sanya su fahimtar cewa basa kusa ne shiyasa, dan haka da safiyar yau suka sanya wa gidan wuta kuma ya 'kone 'kurmus.....
Cikin matu'kar razani Tahir ke kallon manager jin cewa an 'kona masa gidan sa a wayewar garin yau 'din nan.....kenan da bamu tafi ba da ikon Allah ne ka'dai zai iya ku6utar da mu a hannun su.
"..... Yah Rabbi.. "
Ya furta gami da dafe kansa.... Sai ga hawaye sun sau'ko masa take idanuwan sa sukayi jajur, bai san me ze ce kan wannan lamarin ba sam....musamman da yake ba sanin mai neman halaka shin yayi ba, mamakin sa kawai shine ta ina suka ha'da ala'ka yayin da tambayar abinda ya ha'da su ya tsaya masa a zuci.
Bakin sa har rawa yake yake wajen godewa Allah da ya basu ikon tafiya Kaduna cikin kwanakin nan...ya san ba komai bace hakan face kariya daga wurin sa in ba dan yaso kare su ba da babu abinda zai sasu yin tafiyar.
Duk dama ya san sun yi asara sosai a gidan wanda shi kansa ba zai iya irga su ba amma ba zai ta6a fasa furta Alhamdulillah ba.
Duk cikin zuciyar sa yake wannan tunanin yayin da hawayen sa ke sake gangara a hankali.
Manager ne ya dafa kafa'dan sa gami da cigaba da fa'din " ni kaina ina cikin matsala Tahir ta dalilin haka domin rashin samun ka ya sanya shi zargin ni na kawo maka labarin zuwan su, shiyasa ka gudu amma ban damu ba dan nasan babu wanda zai ta6a gujewa 'kaddarar sa ko a ina take shiyasa bazan 'daura ma laifi ba... Amma tun lokacin da na cire ka cikin wancen zargin ni kuma na cusa kaina ciki dumu-dumu batare da na sani ba...... Yanzu haka Tahir wannan ha'duwar tamu da kai babu wanda ya san da ita.... Na tausaya maka sosai jin cewa an 'kona gidan ka fargaba ta shine Allah yasa baka ciki domin ban samu dama na nemi yafiyar ka ba har yanzu, Tahir dan girman Allah kayi ha'kuri ka yafe min 6ata maka suna da nayi duk kuwa da nasan cewa baka da laifin komai amma naso biyewa son zuciya ta... ban cancanci kasancewa shugaba sama da kowa ba saboda na ci amana Tahir....
Sai dai gashi nima ban tsira ba domin yace naci amanar sa kuma zai 'dauki akaina.....please Tahir forgive me, sai daga baya nasan ban kyauta ba sam ban yi maka adalci ba"
Kallon sa kawai Tahir yake yi bai yi wani mamaki ba da yake tun farko ya san cewa sune suka bada report 'din a kamashi, in ma mamakin zai yi bai wuce na ji da yayi cewa shima saboda wani yayi hakan ba, babbar damuwar sa a yanzun kuwa bai wuce yaji ko waye wancen 'din ba mecece kuma ala'kar su.
Manager bai damu da shirun Tahir 'din ba sai kawai ya cigaba da maganar sa inda yace.
" Naji da'di sosai Tahir da ka kasance araye ma'ana baka 'kone cikin wannan gidan ba..... Dan haka ga wannan ka tafi can da nisa inda babu wanda zai takuraka kaje ka gina sabuwar rayuwar ka ka ingan ta rayuwar iyalin ka, nasan yanzu haka abubuwa da yawa ka rasa kuma nasan bazan iya biyan ka ba amma duk da haka bazan barka haka ba Tahir.... Ka tafi da nisa domin *Kido* ba zai barka ba matu'kar ya san kana raye. "
Yana gama fa'din hakan kawai ya cusa masa check 'din yayi gaba....
Tahir kam bai iya yace dashi komai ba.... Mutuwar tsaye yayi yana tunanin sunan da yaji manager ya fa'da.
.........Me yake nufi wai, *Kido* inkiyar Lawyern mahaifin Aishatu ne wanda suka sanshi da shi tun asali sai ma da yaje bincike ne ya samu bayanin cikakken sunan sa.....kenan barrister shine yake neman ransa?... Shine ya sa aka 'kone gidan sa? Shine.... Shine...yasa aka kama shi da laifin da bai aikata ba? Duk dan saboda dukiya ko me?
Ashe gaskiyan Aishatu ne... Gaskiyan tane da ta hana shi tunkarar sa tun abaya.... "
Har manager ya 6ace bai dawo daga tunanin da ya lula ba.
Tafiya manager yakeyi cikin sanyin jiki yana jin dad'in ya sau'ke nauyin da yake kanshi... Tsakanin sa da abokin san bai wani dameshi sosai ba duk kuwa da ya riga yasan kalan mugunta da rashin imanin sa amma yasan bai isa yayi masa abinda ba Allah bane ya tsara dan haka bai damu sosai ba.... Gudun kar Tahir ya'ki amincewa da batun tafiyan ne ma ya Sanya shi 6oye masa cewa ance ne ko ya kawo shi ko kuma shi abakin ransa..... Yaso ya kai report gun 'yan sanda amma yin hakan dai-dai yake da salwantar da rayuwar iyalan sa cuz dasu akayi masa baraza na kan kar ya yadda ya fara sako jami'an tsaro cikin lamarin.
Dan haka sai ya wuce gida kawai yana jiran yaga yadda Allah zai yi dashi.
...... Basu sani bama ashe ko wancan case 'din da ya faru da Tahir.... Lawyern ne ya assaso shi tunda ya samu labarin binciken da Tahir yayi akan sa sai ya rasa yadda zai yi ya 'kas'kantar da shi da rayuwar sa, ya so yasa akashe shi amma sai ya fasa ganin cewa managern Oando babban aminin sa ne, dalilin haka ya sanya suka shirya deal akan hakan da zummar idan an tuhume shi kan satan fuel dole zai biya ku'din komin yawan su, wanda dalilin hakan zaisa ragowar dukiyar dake hannun sa zata sami gi6i na gaske shikenan daga ranan koda zasu nemi karawa dashi they ll not win against him dan basu da komai, rayuwar yanzu kuwa sai kana da shi ake yi da kai.
Ku'din da zasu biya 'din kuma shi manager zai ri'ke sai lawyer ya cika masa ya zama 100million shi kenan deal 'din su ya 'kare daga nan.... amma 'karfin addu'ah da kuma rashin sabo da cin amana ya sanya manager rashin natsuwa bayan sun gama shirya komai, sai gashi kafin deal 'din nasu ya kammala da kansa ya bayyana cewa an samu ku'da'den...sai dai bai sanar da kowa cewa su suka shirya hakan ba.
'Bangaren Lawyer kuwa ganin ha'kar sa bata cimma ruwa ba a karon farko ganin hakan ne ya sanya shi canza tunani zuwa plan B.
*****
Bayan wasu kwanaki sai Oando suka rin'ka damun Tahir akan ya dawo bakin aikin sa, shi kuwa gaba 'daya aiki dasu ya fice masa arai harma ya fara 'ko'karin neman wani aikin a wani wajen daban.
Itama Aishatu bata goyi bayan ya koma can 'din ba haka ma Ja'afar, sai ma tace suje Kaduna su 'dan kwana biyu daga nan su duba gidajen mahaifin ta dake can 'din daga baya sai su dawo kafin nan ko zasu rage damun sa.
bai 'ki shawarar ta ba dan ko shima 'din yana so ya 'dan kauce ko ma dan ya huta, cuz tun bayan faruwar lamarin Kano ta bar ransa kwata-kwata.
Dalilin haka ne yasa washe gari suka wuce Kaduna su biyun su batare da kowa ya sani ba da yake ma har yanzu Mu'een na Azare gun Ja'afar shiyasa ya kasance su biyu ne sukayi tafiyar.
Sunje sunyi duk abubuwan da ya dace sun kuma huta 'din kamar yadda suka yi buri duk cikin sati 'daya, harma sun fara 'ko'karin dawowa da tunanin barin Kano su koma Kaduna da zama gaba 'day musamman ma da suka ga yanayin garin yayi musu ba laifi sai suke ganin zasu dasa sabuwar rayuwa a can 'din.
Ana jibi zasu tafi ne da safe lokacin Aishatu na 'dan fama da zazza6i ko Tahir ma bai san da zancen zazza6in ba yayin da ya shiga cikin gari tun safe ya manta wayar sa a hotel 'din da suke 'din.....Aishatu kuwa zafin zazza6i da ciwon kai da take ji bai barta ta iya koda motsawa ba, tana jin wayoyin su na faman ringing amma bata iya ta 'daga ko guda 'daya ba, duk kuwa da tayi mamakin yanda wayoyin ke faman ruri lokaci guda amma hakan bai sa ta 'dauki 'kiran ba.
'Ko'karin da tayi ma shine tashin da tayi ta kakkashe wayoyin batare da tabi ta kan 'kira ko 'daya ba.
Tsawon lokaci sannan ya dawo kusan shabiyu na rana sai da ma yayi sallahr Zuhr kafin yabi ta kan wayar inda ya tarar da ita a kulle... Yaso yayi mamaki amma kuma tuna cewa Aishatu ce ka'dai zatayi hakan ya sanya shi kunnawa kawai ya bar batun mamakin.
Kunnawar sa
keda wuya kuwa sai ya tsinci 'kiran Manager cikin wayar kamar dama jira yake yi ya kunna.. ...'dauka yayi da tunanin zai masa bayani na 'karshe dan zaton sa ko har yanzu akan komawar sa bakin aiki ne dan haka cikin ransa ya shirya maganar da zai gaya masa akan cewa shi ba zai iya sake yin aiki da su ba har abada......sai dai ga mamakin sa bai kai ga furta abinda ke cikin ransa ba shima 'din hankalin sa ya tashi, cuz yanda yaji muryar Manager cikin damuwa sosai ya sanya shi shiga firgici lokaci guda.
Jikin sa sanyi yayi da ya sau'ke wayar daga kunnen sa, koda Aishatu ta tambaye shi ma bai iya yace da ita komai ba dan gudun 'daga hankalin ta.
Wannan dalilin ne ya sanya shi mantawa da duba sauran tarin missedcalls 'din da akayi masa.
Aranar ya wuce Kano batare da ta sani ba.
Manager ne yayi masa kwatancen inda zai same shi batare da 6ata lokaci ba kuwa ya wuce gurin saboda har yanzun baiji hankalin sa ya kwanta ba tun bayan da suka yi waya da manager a Kaduna.
Ba 'karamin mamaki yayi ba da yaji abinda Manager yace cikin 6oye ko wanene ke abin yayi masa bayani a ta'kaice kan cewa babban abokin sa ke neman ran Tahir 'din da iyalan sa ma gaba 'daya.
Tun jiya wai ake zarya a gidan sa har wayewar garin yau amma basu samu kowa a gidan ba kuma rashin ganin ahalin gidan ya sanya su fahimtar cewa basa kusa ne shiyasa, dan haka da safiyar yau suka sanya wa gidan wuta kuma ya 'kone 'kurmus.....
Cikin matu'kar razani Tahir ke kallon manager jin cewa an 'kona masa gidan sa a wayewar garin yau 'din nan.....kenan da bamu tafi ba da ikon Allah ne ka'dai zai iya ku6utar da mu a hannun su.
"..... Yah Rabbi.. "
Ya furta gami da dafe kansa.... Sai ga hawaye sun sau'ko masa take idanuwan sa sukayi jajur, bai san me ze ce kan wannan lamarin ba sam....musamman da yake ba sanin mai neman halaka shin yayi ba, mamakin sa kawai shine ta ina suka ha'da ala'ka yayin da tambayar abinda ya ha'da su ya tsaya masa a zuci.
Bakin sa har rawa yake yake wajen godewa Allah da ya basu ikon tafiya Kaduna cikin kwanakin nan...ya san ba komai bace hakan face kariya daga wurin sa in ba dan yaso kare su ba da babu abinda zai sasu yin tafiyar.
Duk dama ya san sun yi asara sosai a gidan wanda shi kansa ba zai iya irga su ba amma ba zai ta6a fasa furta Alhamdulillah ba.
Duk cikin zuciyar sa yake wannan tunanin yayin da hawayen sa ke sake gangara a hankali.
Manager ne ya dafa kafa'dan sa gami da cigaba da fa'din " ni kaina ina cikin matsala Tahir ta dalilin haka domin rashin samun ka ya sanya shi zargin ni na kawo maka labarin zuwan su, shiyasa ka gudu amma ban damu ba dan nasan babu wanda zai ta6a gujewa 'kaddarar sa ko a ina take shiyasa bazan 'daura ma laifi ba... Amma tun lokacin da na cire ka cikin wancen zargin ni kuma na cusa kaina ciki dumu-dumu batare da na sani ba...... Yanzu haka Tahir wannan ha'duwar tamu da kai babu wanda ya san da ita.... Na tausaya maka sosai jin cewa an 'kona gidan ka fargaba ta shine Allah yasa baka ciki domin ban samu dama na nemi yafiyar ka ba har yanzu, Tahir dan girman Allah kayi ha'kuri ka yafe min 6ata maka suna da nayi duk kuwa da nasan cewa baka da laifin komai amma naso biyewa son zuciya ta... ban cancanci kasancewa shugaba sama da kowa ba saboda na ci amana Tahir....
Sai dai gashi nima ban tsira ba domin yace naci amanar sa kuma zai 'dauki akaina.....please Tahir forgive me, sai daga baya nasan ban kyauta ba sam ban yi maka adalci ba"
Kallon sa kawai Tahir yake yi bai yi wani mamaki ba da yake tun farko ya san cewa sune suka bada report 'din a kamashi, in ma mamakin zai yi bai wuce na ji da yayi cewa shima saboda wani yayi hakan ba, babbar damuwar sa a yanzun kuwa bai wuce yaji ko waye wancen 'din ba mecece kuma ala'kar su.
Manager bai damu da shirun Tahir 'din ba sai kawai ya cigaba da maganar sa inda yace.
" Naji da'di sosai Tahir da ka kasance araye ma'ana baka 'kone cikin wannan gidan ba..... Dan haka ga wannan ka tafi can da nisa inda babu wanda zai takuraka kaje ka gina sabuwar rayuwar ka ka ingan ta rayuwar iyalin ka, nasan yanzu haka abubuwa da yawa ka rasa kuma nasan bazan iya biyan ka ba amma duk da haka bazan barka haka ba Tahir.... Ka tafi da nisa domin *Kido* ba zai barka ba matu'kar ya san kana raye. "
Yana gama fa'din hakan kawai ya cusa masa check 'din yayi gaba....
Tahir kam bai iya yace dashi komai ba.... Mutuwar tsaye yayi yana tunanin sunan da yaji manager ya fa'da.
.........Me yake nufi wai, *Kido* inkiyar Lawyern mahaifin Aishatu ne wanda suka sanshi da shi tun asali sai ma da yaje bincike ne ya samu bayanin cikakken sunan sa.....kenan barrister shine yake neman ransa?... Shine ya sa aka 'kone gidan sa? Shine.... Shine...yasa aka kama shi da laifin da bai aikata ba? Duk dan saboda dukiya ko me?
Ashe gaskiyan Aishatu ne... Gaskiyan tane da ta hana shi tunkarar sa tun abaya.... "
Har manager ya 6ace bai dawo daga tunanin da ya lula ba.
Tafiya manager yakeyi cikin sanyin jiki yana jin dad'in ya sau'ke nauyin da yake kanshi... Tsakanin sa da abokin san bai wani dameshi sosai ba duk kuwa da ya riga yasan kalan mugunta da rashin imanin sa amma yasan bai isa yayi masa abinda ba Allah bane ya tsara dan haka bai damu sosai ba.... Gudun kar Tahir ya'ki amincewa da batun tafiyan ne ma ya Sanya shi 6oye masa cewa ance ne ko ya kawo shi ko kuma shi abakin ransa..... Yaso ya kai report gun 'yan sanda amma yin hakan dai-dai yake da salwantar da rayuwar iyalan sa cuz dasu akayi masa baraza na kan kar ya yadda ya fara sako jami'an tsaro cikin lamarin.
Dan haka sai ya wuce gida kawai yana jiran yaga yadda Allah zai yi dashi.