Sashe 31
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka har yaran ta suka girma suka zama mutane, bata kuma koma can garin iyayen ta ba saboda tana ganin tamkar yaran nata da nan suka bu'di idanu so bata so ta canja musu salon rayuwa, kuma ko dan saboda nata aikin da take yi shiyasa ma kawai suka cigaba da zaman su nan.
Suma yaran nata ba laifi suna 'ko'karin yin 'kananun sana'o'i basu zama haka nan....cikin rayuwar su babu abinda ya canza face kewar mahaifin su, karatun su ma sun cigaba da yi atare domin tsakanin su babu wani rata sosai shekaru uku ne zuwa hu'du kawai hakan yasa karatun su yake tafiya lokaci guda.
Suna kammala secondary ta basu zauna ba suka zarce da karatu Taheer BUK yatafi yayin da Ja'afar yayi karatun sa a nan cikin garin Bauchi inda ya karanci Accounting, basu samu matsala da komai ba har suka kammala kasancewarsu yara masu bada himma haza'ka da kuma 'ko'karin karatu.
Cikin sa'a kuwa suna kammala makarantar kowanen su yayi dace da samun aiki dai-dai da abinda ya karanta....inda Ja'afar yayi dacen samun aiki a banki cikin garin Bauchi, yayin da Taheer kuma ya samua gidan mai a Kano a matsayin 'kananun ma'aikata.
Duk da hakan sam ba raina ko kuma yin girma kai ba, hannu bibbiyu ya rungumi aiki gami da godewa mahallicin sa.
Samun aikin nasu ya matu'kar yi musu da'di domin kuwa suna gani cewa lokaci yayi da ya kamata mahaifiyar su ta huta.....ai kuwa gata sosai take samu daga dukkan 6angarorin biyu sai godiyan Allah ita kanta sai da tasan cewa ehh lallai haihuwa na da rana.
Sai dai kawai tayi ta binsu da addu'ar samun sa'a da kuma dacewa.
Taheer ne yaso ya 'dauke ta ma kwata-kwata daga wannan garin amma ta nuna masa ba komai ya barta a nan 'din kawai, kuma ma me yasa zata bishi bacin ba iyali ne dashi ba sai ta 'karasa da fa'din ka bari idan ka ajiye iyali sai ij bika ko kuwa?"
Shiru kawai yayi mata dan sam shi ba haka yaso ba amma dolen sa ya ha' kura tunda ta nuna bata ra'ayi ai shikenan.
Ba su shekara da fara aikin ba Zmz sai Allah ya kar6i ran mahaifiyar ta su bayan jinya (Allahu Akbar) mutum mai rai kenan.....sunci kuka sunyi takaici domin sunso mahaifiyar su ta fara cin moriyar su kafin kafin kowa yaci, amma hakan bai yiyuba Allah ya nuna ikonsa dole suka ha'kura suka yi tawakkali, domin *hukuncin Allah* ba a ja da shi...mutuwa kuma dolen kowa ce..
Bayan sun gama kar6ar gaisuwa sai duk suka koma bakin aikin su zuciyoyin su cike da alhaini.
Cikin sa'a kuwa Taheer bai wani jima da fara aikin ba ya samu 'karin girma...sun yi matu'kar farin ciki sosai, bayan hakan ne Ja'afar ya shawarce shi da cewa gara ya ajiye iyali saboda halin rayuwa kuma ma ko don cika sunnar ma'aiki (SAW).....Ya 'karashe da fa'din " kaga ni tuntuni fa kai nake jira in ba dan haka ba da tuni anyi nawa".
Washe baki Taheer yayi yana kallon sa yace" haba malam.... kace kenan dama hanya kake so in baka"!
"Ashe ka gane manufata".
Cewar Ja'afar yana dariyar shima.
Sai Taheer yace masa " kar ka damu to....ba sai ka jirani ba.....inaga ai za'a iya ha'dawa duka rana 'daya ko?"
" Gud idea...."! Ja'afar ya furta yana murmushi sannan ya 'karasa da fa'din " gaskiya shawarar ka tayi 'dan uwa, aini da banyi tunanin hakan ba sam".
" Hmm " kawai Taheer yace dan shi sam ba mai son yawan hayaniya bane, ta inda bambancin su yake kenan da 'kanin nasa.
Taheer bai yi 'kasa a gwiwa ba yaje ya tuntu6i wacce suke 'dan soyayya da ita..har yake tunanin inda hali ita zai aura.....wata matashiyar yarinya ce 'yar 'kabilar Igbo da bazata gaza 23yrs ba, mazauna garin Kano ne su....ama Kano aka haife su....duba da karamci da mutunci gami da ha'ku'ri irin na mabiya addinin muslunci da kuma mazauna garin Kanon ya sanya mahaifin su kar6an muslunci tun kafin yaran sa suyi wayo...anan matar sa ta nuna 'kin amincewar ta da wannan batun inda batare da 6ata wani lokaci ba ta tattara ta koma mahaifar ta wato Imo State.
Shi kuwa ya hanata tafiya da kowa cikin sa, dolen ta ta tafi ta tafi ta barshi da yaran nata guda uku, biyu maza da mace 'daya wacce mahaifin ta ya za6a mata suna Aishatu yayin da 'kannan ta maza biyun suka ci suna Aliyu da Umar, shikuma uban ya za6i sunan fiyayyen halitta annabi Muhammad (SAW) yace wannan ne yayi masa.
Haka suka cigaba da rayuwar su cikin haske da alfarmar addinin muslunci har yaran sa suka yi wayo, babu wanda ya 'kara ziyar tan su daga 6angaren dangin uwa har ma da na mahaifin nasu, hatta ita kanta mahaifiyar tasu ma bata sake waiwayan su ba haka shima mahaifin su bai yi gigin taka 'kafar sa zuwa can garin nasu ba domin yasan bazata 'kare musu da da'di ba.
Tunda ya kar6i addinin muslunci ya ri'ke sa da hannu bibbiyu domin koda wasa baya sakaci da islamiyar yaran sa sosai yake bada muhimmanci ga wannan 6angaren shi kansa ma neman ilimin yake bai zauna haka nan ba......shiyasa yaran nasa suka taso cikin tarbiya dai-dai gwargwado, amma bai yadda ya sake yin aure duk kuwa da malamai na nuna masa muhimmancin hakan amma sam ba bada himma ga hakan ba har girma ya kama shi.
Aishatu tayi matu'kar farin ciki da jin cewa Taheer na so iyaye su shiga maganar su... dan kuwa ba 'karamin so take yi masa dama, shi 'din ne dai yake 'dan taka mata birki da irin salon sa na shariya da basarwa.
Bata wani 6ata lokaci ba taje ta samu mahaifin ta da maganar take kuwa ya basu dama domin shima baya da burin da ya wuce yaga ya aurar da ita a lokacin.......cikin 'kan'kanin lokaci aka tsaida maganar auren su harda na Ja'afar ma.
Bayan wata uku akayi bikin su kowa ya tare da matar sa.
Tun daga nan kowa ya dasa gidan sa cikin so da kulawa da iyalin sa...kuma ba laifi suna zumuncin su dai-dai gwargwado duk da ma ba gari 'daya suke ba amma suna 'ko'karin kulawa da zumuncin dake tsakanin su.
Taheer Kano yake da zama yayin da Ja'afar yake zama Azare da matar sa dan shi anan ya samu aikin nasa tun farko.
Shekara na zagayowa Aishatu ta haifi 'dan ta namiji kyakkyawa da shi, yaro mai kyau da haiba sak Baban sa sai dai farin sa gaba 'daya na uwar sa ya kwaso har ma ya 'dan so ya zartata.
Murna gurin wannan familyn ba'a cewa komai sai wanda ya gani...domin kuwa babu wanda bai yi farin cikin da samun wannan 'karuwar ba.
Tun washe garin haihuwar Zainab matar Ja'afar ta zo shima 'din ba a barshi abaya ba domin kuwa ana gobe suna shima ya dira garin Kano dan asha shagalin suna dashi.
Ranar suna yaro yaci sunan kakan sa wato mahaifin Aishatu.... *Muhammad Taheer*, matar 'kanin baban sa Ja'afar ne ta fara ambatan sa da suna *Mu'inuddeen* ( the helper of d religion).......tace da sunan zaa 'kira shi....sosai akayi shagalin suna cikin bawa Naira kashi...kowa ya nuna bajintar sa sosai abin ba'a cewa komai.
Shi kansa mahaifin Aishatu da yaro yaci sunan sa ma ba'a barshi a baya ba wajen bada nasa manyan gudummuwan domin shima wani irin so yaji yake wa yaron na ban mamaki hakama Umar da Aliyu da suke ji tamkar su dawo zama tare da babyn.
Yaro ya taso cikin so da 'kaunar duka dangin sa musamman ma Baban sa Ja'afar da har yanzu Allah bai ba shi haihuwa ba, matar sa ko 6atan wata bata ta6a yi ba, amma bai wani 'daga hankalin sa da hakan ba domin ya san Allah shike bada haihuwa a duk lokacin da yaso haka kuma saiga wanda yaso.
Matar san ce dai take 'dan damun sa wasu lokutan amma ba laifi ya kan kwantar mata da hankali da nuna mata cewar hakan ya faru ne saboda buwayar mahallici kuma bawai dan bai san su ba a a sai dan kawai ya jarrabe su, ya kance da ita kuma ma dududu shekar su nawa da yin auren da har zata damu kanta ai komai yana da lokaci kuma hanzari ko rashin ha'kurin mu baya ta6a sawa mu samu abu face Allah ya so, mu ci gaba da addu'ah insha Allahu watarana ke ma zaki haihu".
Idan ya fa'di mata hakan kuma Alhamdulillah tana fahimtar sa.
*****
Allah cikin ikon sa haihuwar *Mu'inuddeen* sai ya zowa mahaifin sa da *wani haske*...domin sai ya ringa samun 'karin girma a hankali wurin aiki ga kuma hanyoyi da suka 'kara bu'de masa na ban mamaki, inda cikin natsuwa tattalin arzi'kin sa ya ringa bun'kasa yana 'kara girma.
Kafin shekaru uku kuwa har ya zama wani abu da shi kansa ya san cewa ya shiga sahun wasu daban masu fa'da aji ko wani bai fa'da shi 'din ya san hakan.
Manyan store ya bu'de kusan guda uku ya zuba kaya inda ya wakilta masu kula masa da shi cikin ri'kon amana da gaskiya.
Bashi da matsalar komai a yanzun illah ya kula da tarbiyar iyalan sa da hakkokin su.
A gidan Alhaji Muhammad Ugoh Chukwu (mahaifin matar sa) ya bar Mu'een lokacin da zasu tafi aikin hajji da matar sa...wanda hakan ya 'kara sanya 'ka'k'karfar so da sha'kuwa tsakanin Mu'een da kawunan nasa.
Kafin su dawo kuwa Alhaji Muhammad U.C ya bada kyautar wani babban plot 'din sa dake can Zaria road har ma ya musanya sunan an 'daura na Mu'een.
Koda suka dawo kuwa sunyi matu'kar farin ciki da jin hakan baran ma Aishatu da take 'kara jin da'din yanda mahaifin ta ke so da kula da jinin ta.
Taheer ne dai ya 'dan so yayi 'korafi amma Alhajin ya dakatar da shi da fa'din " Kyautar sa ga mai sunan sa ne shi bai ce ya sa baki ba".
Yayi maganar ne cikin karkatacciyar hausar sa da har yau bata 'dauki hanya ba da kuma murmushi kan fuskar sa.
Suma yaran nata ba laifi suna 'ko'karin yin 'kananun sana'o'i basu zama haka nan....cikin rayuwar su babu abinda ya canza face kewar mahaifin su, karatun su ma sun cigaba da yi atare domin tsakanin su babu wani rata sosai shekaru uku ne zuwa hu'du kawai hakan yasa karatun su yake tafiya lokaci guda.
Suna kammala secondary ta basu zauna ba suka zarce da karatu Taheer BUK yatafi yayin da Ja'afar yayi karatun sa a nan cikin garin Bauchi inda ya karanci Accounting, basu samu matsala da komai ba har suka kammala kasancewarsu yara masu bada himma haza'ka da kuma 'ko'karin karatu.
Cikin sa'a kuwa suna kammala makarantar kowanen su yayi dace da samun aiki dai-dai da abinda ya karanta....inda Ja'afar yayi dacen samun aiki a banki cikin garin Bauchi, yayin da Taheer kuma ya samua gidan mai a Kano a matsayin 'kananun ma'aikata.
Duk da hakan sam ba raina ko kuma yin girma kai ba, hannu bibbiyu ya rungumi aiki gami da godewa mahallicin sa.
Samun aikin nasu ya matu'kar yi musu da'di domin kuwa suna gani cewa lokaci yayi da ya kamata mahaifiyar su ta huta.....ai kuwa gata sosai take samu daga dukkan 6angarorin biyu sai godiyan Allah ita kanta sai da tasan cewa ehh lallai haihuwa na da rana.
Sai dai kawai tayi ta binsu da addu'ar samun sa'a da kuma dacewa.
Taheer ne yaso ya 'dauke ta ma kwata-kwata daga wannan garin amma ta nuna masa ba komai ya barta a nan 'din kawai, kuma ma me yasa zata bishi bacin ba iyali ne dashi ba sai ta 'karasa da fa'din ka bari idan ka ajiye iyali sai ij bika ko kuwa?"
Shiru kawai yayi mata dan sam shi ba haka yaso ba amma dolen sa ya ha' kura tunda ta nuna bata ra'ayi ai shikenan.
Ba su shekara da fara aikin ba Zmz sai Allah ya kar6i ran mahaifiyar ta su bayan jinya (Allahu Akbar) mutum mai rai kenan.....sunci kuka sunyi takaici domin sunso mahaifiyar su ta fara cin moriyar su kafin kafin kowa yaci, amma hakan bai yiyuba Allah ya nuna ikonsa dole suka ha'kura suka yi tawakkali, domin *hukuncin Allah* ba a ja da shi...mutuwa kuma dolen kowa ce..
Bayan sun gama kar6ar gaisuwa sai duk suka koma bakin aikin su zuciyoyin su cike da alhaini.
Cikin sa'a kuwa Taheer bai wani jima da fara aikin ba ya samu 'karin girma...sun yi matu'kar farin ciki sosai, bayan hakan ne Ja'afar ya shawarce shi da cewa gara ya ajiye iyali saboda halin rayuwa kuma ma ko don cika sunnar ma'aiki (SAW).....Ya 'karashe da fa'din " kaga ni tuntuni fa kai nake jira in ba dan haka ba da tuni anyi nawa".
Washe baki Taheer yayi yana kallon sa yace" haba malam.... kace kenan dama hanya kake so in baka"!
"Ashe ka gane manufata".
Cewar Ja'afar yana dariyar shima.
Sai Taheer yace masa " kar ka damu to....ba sai ka jirani ba.....inaga ai za'a iya ha'dawa duka rana 'daya ko?"
" Gud idea...."! Ja'afar ya furta yana murmushi sannan ya 'karasa da fa'din " gaskiya shawarar ka tayi 'dan uwa, aini da banyi tunanin hakan ba sam".
" Hmm " kawai Taheer yace dan shi sam ba mai son yawan hayaniya bane, ta inda bambancin su yake kenan da 'kanin nasa.
Taheer bai yi 'kasa a gwiwa ba yaje ya tuntu6i wacce suke 'dan soyayya da ita..har yake tunanin inda hali ita zai aura.....wata matashiyar yarinya ce 'yar 'kabilar Igbo da bazata gaza 23yrs ba, mazauna garin Kano ne su....ama Kano aka haife su....duba da karamci da mutunci gami da ha'ku'ri irin na mabiya addinin muslunci da kuma mazauna garin Kanon ya sanya mahaifin su kar6an muslunci tun kafin yaran sa suyi wayo...anan matar sa ta nuna 'kin amincewar ta da wannan batun inda batare da 6ata wani lokaci ba ta tattara ta koma mahaifar ta wato Imo State.
Shi kuwa ya hanata tafiya da kowa cikin sa, dolen ta ta tafi ta tafi ta barshi da yaran nata guda uku, biyu maza da mace 'daya wacce mahaifin ta ya za6a mata suna Aishatu yayin da 'kannan ta maza biyun suka ci suna Aliyu da Umar, shikuma uban ya za6i sunan fiyayyen halitta annabi Muhammad (SAW) yace wannan ne yayi masa.
Haka suka cigaba da rayuwar su cikin haske da alfarmar addinin muslunci har yaran sa suka yi wayo, babu wanda ya 'kara ziyar tan su daga 6angaren dangin uwa har ma da na mahaifin nasu, hatta ita kanta mahaifiyar tasu ma bata sake waiwayan su ba haka shima mahaifin su bai yi gigin taka 'kafar sa zuwa can garin nasu ba domin yasan bazata 'kare musu da da'di ba.
Tunda ya kar6i addinin muslunci ya ri'ke sa da hannu bibbiyu domin koda wasa baya sakaci da islamiyar yaran sa sosai yake bada muhimmanci ga wannan 6angaren shi kansa ma neman ilimin yake bai zauna haka nan ba......shiyasa yaran nasa suka taso cikin tarbiya dai-dai gwargwado, amma bai yadda ya sake yin aure duk kuwa da malamai na nuna masa muhimmancin hakan amma sam ba bada himma ga hakan ba har girma ya kama shi.
Aishatu tayi matu'kar farin ciki da jin cewa Taheer na so iyaye su shiga maganar su... dan kuwa ba 'karamin so take yi masa dama, shi 'din ne dai yake 'dan taka mata birki da irin salon sa na shariya da basarwa.
Bata wani 6ata lokaci ba taje ta samu mahaifin ta da maganar take kuwa ya basu dama domin shima baya da burin da ya wuce yaga ya aurar da ita a lokacin.......cikin 'kan'kanin lokaci aka tsaida maganar auren su harda na Ja'afar ma.
Bayan wata uku akayi bikin su kowa ya tare da matar sa.
Tun daga nan kowa ya dasa gidan sa cikin so da kulawa da iyalin sa...kuma ba laifi suna zumuncin su dai-dai gwargwado duk da ma ba gari 'daya suke ba amma suna 'ko'karin kulawa da zumuncin dake tsakanin su.
Taheer Kano yake da zama yayin da Ja'afar yake zama Azare da matar sa dan shi anan ya samu aikin nasa tun farko.
Shekara na zagayowa Aishatu ta haifi 'dan ta namiji kyakkyawa da shi, yaro mai kyau da haiba sak Baban sa sai dai farin sa gaba 'daya na uwar sa ya kwaso har ma ya 'dan so ya zartata.
Murna gurin wannan familyn ba'a cewa komai sai wanda ya gani...domin kuwa babu wanda bai yi farin cikin da samun wannan 'karuwar ba.
Tun washe garin haihuwar Zainab matar Ja'afar ta zo shima 'din ba a barshi abaya ba domin kuwa ana gobe suna shima ya dira garin Kano dan asha shagalin suna dashi.
Ranar suna yaro yaci sunan kakan sa wato mahaifin Aishatu.... *Muhammad Taheer*, matar 'kanin baban sa Ja'afar ne ta fara ambatan sa da suna *Mu'inuddeen* ( the helper of d religion).......tace da sunan zaa 'kira shi....sosai akayi shagalin suna cikin bawa Naira kashi...kowa ya nuna bajintar sa sosai abin ba'a cewa komai.
Shi kansa mahaifin Aishatu da yaro yaci sunan sa ma ba'a barshi a baya ba wajen bada nasa manyan gudummuwan domin shima wani irin so yaji yake wa yaron na ban mamaki hakama Umar da Aliyu da suke ji tamkar su dawo zama tare da babyn.
Yaro ya taso cikin so da 'kaunar duka dangin sa musamman ma Baban sa Ja'afar da har yanzu Allah bai ba shi haihuwa ba, matar sa ko 6atan wata bata ta6a yi ba, amma bai wani 'daga hankalin sa da hakan ba domin ya san Allah shike bada haihuwa a duk lokacin da yaso haka kuma saiga wanda yaso.
Matar san ce dai take 'dan damun sa wasu lokutan amma ba laifi ya kan kwantar mata da hankali da nuna mata cewar hakan ya faru ne saboda buwayar mahallici kuma bawai dan bai san su ba a a sai dan kawai ya jarrabe su, ya kance da ita kuma ma dududu shekar su nawa da yin auren da har zata damu kanta ai komai yana da lokaci kuma hanzari ko rashin ha'kurin mu baya ta6a sawa mu samu abu face Allah ya so, mu ci gaba da addu'ah insha Allahu watarana ke ma zaki haihu".
Idan ya fa'di mata hakan kuma Alhamdulillah tana fahimtar sa.
*****
Allah cikin ikon sa haihuwar *Mu'inuddeen* sai ya zowa mahaifin sa da *wani haske*...domin sai ya ringa samun 'karin girma a hankali wurin aiki ga kuma hanyoyi da suka 'kara bu'de masa na ban mamaki, inda cikin natsuwa tattalin arzi'kin sa ya ringa bun'kasa yana 'kara girma.
Kafin shekaru uku kuwa har ya zama wani abu da shi kansa ya san cewa ya shiga sahun wasu daban masu fa'da aji ko wani bai fa'da shi 'din ya san hakan.
Manyan store ya bu'de kusan guda uku ya zuba kaya inda ya wakilta masu kula masa da shi cikin ri'kon amana da gaskiya.
Bashi da matsalar komai a yanzun illah ya kula da tarbiyar iyalan sa da hakkokin su.
A gidan Alhaji Muhammad Ugoh Chukwu (mahaifin matar sa) ya bar Mu'een lokacin da zasu tafi aikin hajji da matar sa...wanda hakan ya 'kara sanya 'ka'k'karfar so da sha'kuwa tsakanin Mu'een da kawunan nasa.
Kafin su dawo kuwa Alhaji Muhammad U.C ya bada kyautar wani babban plot 'din sa dake can Zaria road har ma ya musanya sunan an 'daura na Mu'een.
Koda suka dawo kuwa sunyi matu'kar farin ciki da jin hakan baran ma Aishatu da take 'kara jin da'din yanda mahaifin ta ke so da kula da jinin ta.
Taheer ne dai ya 'dan so yayi 'korafi amma Alhajin ya dakatar da shi da fa'din " Kyautar sa ga mai sunan sa ne shi bai ce ya sa baki ba".
Yayi maganar ne cikin karkatacciyar hausar sa da har yau bata 'dauki hanya ba da kuma murmushi kan fuskar sa.