Sashe 210
Noorul Haske Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Anan gidan man Sani ya samu wata me sai da goro suka daidaita ta kuma amince da shi duk da yake tasan yana da matsalar hannu 'daya amma bata 'ki shi kamar yadda 'yan can garin su suka guje shi ba.
Sai dai bai tashi sanin wace ya aura ba sai bayan auren nasu nan ya fahimci sauran gardawan ya kwasa...bai ce da ita komai ba domin yasan duk cikin hukuncin sa ne da Allah ya tanadar masa badan hakan ba ba zai ta6a ha'da shi da ita ba balle har yaji tayi masa cikin zuciya.
Yasan alhakin Jasmine bazai ta6a barin sa ba,
kuma da yake yasan ba'a yiwa Allah wayo shiyasa be wani damu kansa ba domin yasan komai na tafiya ne bisa tsarin mahalicci, koda yace zai rabu da ita be kuma san wace kala zai sake karo da ita ba...hakan yasa dole ya watsar da komai ya ja matar sa ajiki suka yi zaman su lafiya lau dan biyayya ne da ita sosai.
*_Allah ka raba mu da kusantar Zina balle har mu aikata shi_*
Kusan lokaci guda matar Ishaq da matar Sani suka sau'ka dan tsakanin su bai fi 3weeks ba...Matar Ishaq ce ta fara haihuwa inda ta haifi 'yar ta mace mai kyan gaske...sunan Ammi Ishaq ya sanyawa Babyn inda suke 'kiran ta da Nana.
Matar Sani ma mace ta haifa shima kuma ya sanyawa Babyn sa suna Aisha amma bai sanar da kowa sunan da ya sanya ba, kunya yake ji ya furta cewa sunan Jasmine ya sanya, hakan yasa ya bar abin sa aran sa shika'dai...Baby ake ce da yarinyar Sani.
Noor ce dai shiru har yanzu..Deen tuni ya koma bakin aikin sa shima sun koma Abujan gaba 'daya da zama..zaman su suke mai cike da so da 'kaunar juna basu yadda su 6ata lokaci wajen tuno abinda ya riga ya wuce musu.
Husnah sai da ta shekara goma da aure kafin a shekarar Allah ya nufe ta da samun ciki, murna kamar zata ha'diye kanta, Hisham ma kamar ya goya ta, Husnah kam banda godiya ga Allah babu abinda take yi ga yaran Hisham duk sun yi wayo suna makaranta...Mummyn ta tafi kowa farin ciki dan abinda ta jima tana jira ne yau Allah ya bata, daga Husnah bata da kowa sai yanzu da Allah ya nufe ta da samun rabo...itama yanzu da'di take ji zata zama kaka na asali.
Koda lokacin haihuwa tayi sai ta sam6alo 'danta namiji 'katoto da shi.
Sunan mahaifin ta aka sanya wato Hamza amma Daddy suke 'kiran sa...Husnah sau da dama agaba take sa yaron tayi ta kallo tana murmushi.
*Ashe in da rai da rabo...Bai kamata 'dan Adam ya cire rai da rahamar Allah ba.*
*****
Zaune yake yayin da Noor ke kwance tayi matashi da 'kafar sa...yanzun nan ya gama cire waya a kunnan sa Anas ya 'kira shi da Albishir 'din matar sa ta haifa masa Baby girl karo na biyu...da farin ciki ya sa albarka gami da fa'din sai munzo suna yana dariya ya cire wayar a kunnan sa.
Duban ta yayi ta wani lumshe idanu...sai ya kai hannu jikin ta a 'ko'karin sa na son 'dago ta amma ta sake narkewa..." Tashi mana albishir zan yi miki fa..?"
" Na riga naji ai..Allah ya raya mana ita.."
Ta bashi amsa da idanun ta a lumshe.
" To tashi muyi magana please...nifa na fara 'kosawa...3yrs fa yanzu da dawowar ki amma shiru har yanzu..gaskiya dole ne na duba ki in san abinda ke faruwa...".
" Ni dai a a...".
" Ni kuma nace Erh...so nake nima na fara raino...kin ganin yarinyar Ishaq har ta fara 'kiran Daddy fa..gaskiya da sake dole in san abin yi...".
Har yanzun idanun ta a lumshe tace" Ka kar6o mana aron ta kawai mu zauna da ita shikenan ka samu abin rainon ka...ni kaga dama ba so nake in sake haihuwa ba..".
'Bata rai yayi nan take..da 6acin rai yace" Baki da hankali...".
" Dagaske ban so ni".
" Nuree ban son shirme..."
Zatayi magana yayi saurin dakatar da ita.
'Karfi yasa ya 'dago ta zaune sai gata daf da dashi sosai, ta firgita ma she thought marin ta zai yi sai kuma taji shiru hannun sa taji yakai 'kasan marar ta yana yawo da shi wanda hakan yasa tayi saurin bu'de idanun ta ta sau'ke su akan fuskar sa.
Murmushi taga yana yi memakon 6acin rai da taji cikin muryar sa, da mamaki sai tsaya duban sa..bakin sa ya sau'ke saman la66an ta ya sumbata gami da matsa marar tata da 'dan 'karfi sai ta saki 'kara.
A kunne ya ra'da mata" Naki albishir 'din kenan...".
" Me hakan ke nufi wai?"
Ta tambayi kanta mamaki 'karara kan fuskar ta...hannun ta ta kai kan nasa itama ta shafo cikin sai yace mata" Kinga ikon Allah ko..dama mugunta kike so kiyi min baki san Allah na so na ba...ba tun yau na fahimci kina 'dauke da ciki ba kawai gudun ruwan ki nake son gani dan naga alamar baki da mu da rashin cikin ba ke ashe ban sani ba dagaske baki 'kauna ta..".
Shiru tayi tana jin tsananin fargaba na kamata, ita fa ba wai bata son haihuwa bane kawai tsoro take ji kar labari ya sake maimaita kansa akan abinda zata kuma haifa, shiyasa ta tilastawa kanta ha'kura da haihuwa gaba 'daya.
Allah ma sai ya dubi zuciyar ta ya ja mata lokaci har cikin eanta take jin ta ha'kura da haihuwa indai zasu yi rayuwar su a hakan dashi bazata ta6a damuwa ba koda kuwa basu da 'da ko 'ya agaban su har abada..shiyasa tun yanzu take jin tausayin abinda ke cikin cikin ta.
Hawaye ne da bata shirya musu ba taji sun gangaro saman kuncin ta..Yah Deen kam tsayawa kallon ta ma yayi sosai take bashi mamaki.
Wasa-wasa Noor sosai ta 'daga hankalin ta akan cikin duk ta tashi hankalin ta ta hana shi natsuwa, sosai yake kwantar da murya ya mata nasihar amma abanza, tsakanin ta da Allah take nuna rashin son cikin, har sai ma ya rasa yadda zai yi da ita.
Ya fahimci so take ta rabu da cikin cikin ko wani irin hali, sai da ya fito a Mu'een 'din sa ya nuna mata cewa hauka zai mata idan ta kuskura ta salwantar masa da cikin sa...kafin ta 'dan rage haukan da take yi.
Amma kullum tana cikin kuka, tunda labarin cikin ya bayyana mata basu 'kara walwala a gidan ba.
Daga 'karshe sai da batun ya kaisu har wajen iyayen su, da 'kyar Noor ta ha'kura akan zata haifi cikin bayan Anty tayi mata nasiha sosai da al'kawarin da ta haifa zata 'dauke a wurin ta...misalai da dama Antyn ta bata inda tace" Ni kaina ma babban misali nake Noor idan kin bada hankali, rana guda aka 'daura auren mu da Ammin ku amma Allah cikin ikon sa har yau bai ta6a bani haihuwa ba, nayi kuka munyi Addu'ah 'karshe dole muka ha'kura muka fawwala Allah komai, yanzu haka na riga na cire raina da samun rabo shiyasa kika ga ina ruyuwa ta cike da walwala domin ban isa in ce da Allah miye dalili ba....amma ke gashi kin samu cikin sau'ki amma kina wasa da damar ki ta hanyar ki maidawa Allah babban kyautar da yayi miki, a kaf 'din rayuwa babu abinda yakai kyautar 'da da kuma lafiya da Allah yake yi mana domin duk dukiyar ka baka isa ka siya ba har sai yaga dama, godiya ya kamata kiyi baki nuna ba fushin ki ba Noor.
Banda kuka babu abinda Noor ke yi dan a ganin ta har yanzu basu fahimce ta bane shiyasa, ita da kanta tana son taga 'ya'yan ta amma bazata juri ganin ba'ka'ken ta6o ajikin su saboda uban su ba shiyasa ta ha'kura kawai, hala sun manta da abinda ya faru da Baby ne.
Ganin ta kasa kwantar da hankalin ta ne ya sanya Ammi ta hana ta komawa Abujan ta zauna da ita tana bata kulawar da ta dace...shi kansa ma hakan yafi masa dan 'daga masa hankali take yi idan tana kusa da shi.
Kwanaki na ta tafiya cikin Noor na sake girma, sai dai zuwa yanzun Alhamdulillah ta kwantar da hankalin ta sosai saboda yawan nasihar da ake yi mata, ita kanta yanzu tasan cewa kuskure ta aikata domin kuwa duk abinda Allah ya tsara kai baka isa ka canza shi ba, wayon ta bai isa ya kawar da shirin Allah ba matu'kar ya riga yace sai ya faru.
Bayan wata tara da 'yan satikai ta haifo yaranta kyawawa guda biyu mace da namiji...inda yaron yaci sunan Alhaji Baba amma ana 'kiran sa da _Affan_ macen kuma sunan Anty Zainab aka sanya mata se ake 'kiran ta da suna _Farrah_ .
Tunda ta haife su kuma saj taji 'kaunar abinta ya sake kamata, haka ta cigaba da rainon abinta bata 'kara nuna musu 'kyama ba Addu'ar ta ayanzu kawai shine Allah ubangiji ya raya mata su ya kuma basu kariya a duk inda suke...
*****
_Bayan shekaru biyu_
Tsaye take a kitchen da tu'ke'ken cikin ta hannun ta wu'ka ne tana slizing green beans a hankali dan kar ta kuskure.
Gidan shiru cuz yaranta duk basu nan, Affan na can wurin Ammi yayin da Farrah aka yi can gaba da ita wurin Anty Zainab tuni an tattara mata kayan ta can, hakan yasa banda 'karar T.v dake aiki a parlour baka jin komai sai ko kuma idan kayo hanyar kitchen kaji kwarabniyar da take yi.
Tana daga kitchen 'din tajiyo muryar sa yana 'kiran sunan ta kamar wanda akace masa bata gidan ne.
" *Nureen-Deen* !"
Ya sake anbata a karo na uku.
Noor bata amsa ba illah murmushin da take yi daga inda take tsaye tana mai cigaba da aikin ta.
Yanzun fa ya fita zuwa masallaci kuma yasan aiki take a kitchen amma yake ta fama 'kwala 'kiran sunan ta.
Kitchen 'din ya nufo sai ya tsaya daga bakin 'kofa ya wani kama kunkumi..gira ya 'dage da alamun 'kosawa yace" Ya ina ta 'kiran Nureen-Deen amma bata amsa ni ba?"
Sai dai bai tashi sanin wace ya aura ba sai bayan auren nasu nan ya fahimci sauran gardawan ya kwasa...bai ce da ita komai ba domin yasan duk cikin hukuncin sa ne da Allah ya tanadar masa badan hakan ba ba zai ta6a ha'da shi da ita ba balle har yaji tayi masa cikin zuciya.
Yasan alhakin Jasmine bazai ta6a barin sa ba,
kuma da yake yasan ba'a yiwa Allah wayo shiyasa be wani damu kansa ba domin yasan komai na tafiya ne bisa tsarin mahalicci, koda yace zai rabu da ita be kuma san wace kala zai sake karo da ita ba...hakan yasa dole ya watsar da komai ya ja matar sa ajiki suka yi zaman su lafiya lau dan biyayya ne da ita sosai.
*_Allah ka raba mu da kusantar Zina balle har mu aikata shi_*
Kusan lokaci guda matar Ishaq da matar Sani suka sau'ka dan tsakanin su bai fi 3weeks ba...Matar Ishaq ce ta fara haihuwa inda ta haifi 'yar ta mace mai kyan gaske...sunan Ammi Ishaq ya sanyawa Babyn inda suke 'kiran ta da Nana.
Matar Sani ma mace ta haifa shima kuma ya sanyawa Babyn sa suna Aisha amma bai sanar da kowa sunan da ya sanya ba, kunya yake ji ya furta cewa sunan Jasmine ya sanya, hakan yasa ya bar abin sa aran sa shika'dai...Baby ake ce da yarinyar Sani.
Noor ce dai shiru har yanzu..Deen tuni ya koma bakin aikin sa shima sun koma Abujan gaba 'daya da zama..zaman su suke mai cike da so da 'kaunar juna basu yadda su 6ata lokaci wajen tuno abinda ya riga ya wuce musu.
Husnah sai da ta shekara goma da aure kafin a shekarar Allah ya nufe ta da samun ciki, murna kamar zata ha'diye kanta, Hisham ma kamar ya goya ta, Husnah kam banda godiya ga Allah babu abinda take yi ga yaran Hisham duk sun yi wayo suna makaranta...Mummyn ta tafi kowa farin ciki dan abinda ta jima tana jira ne yau Allah ya bata, daga Husnah bata da kowa sai yanzu da Allah ya nufe ta da samun rabo...itama yanzu da'di take ji zata zama kaka na asali.
Koda lokacin haihuwa tayi sai ta sam6alo 'danta namiji 'katoto da shi.
Sunan mahaifin ta aka sanya wato Hamza amma Daddy suke 'kiran sa...Husnah sau da dama agaba take sa yaron tayi ta kallo tana murmushi.
*Ashe in da rai da rabo...Bai kamata 'dan Adam ya cire rai da rahamar Allah ba.*
*****
Zaune yake yayin da Noor ke kwance tayi matashi da 'kafar sa...yanzun nan ya gama cire waya a kunnan sa Anas ya 'kira shi da Albishir 'din matar sa ta haifa masa Baby girl karo na biyu...da farin ciki ya sa albarka gami da fa'din sai munzo suna yana dariya ya cire wayar a kunnan sa.
Duban ta yayi ta wani lumshe idanu...sai ya kai hannu jikin ta a 'ko'karin sa na son 'dago ta amma ta sake narkewa..." Tashi mana albishir zan yi miki fa..?"
" Na riga naji ai..Allah ya raya mana ita.."
Ta bashi amsa da idanun ta a lumshe.
" To tashi muyi magana please...nifa na fara 'kosawa...3yrs fa yanzu da dawowar ki amma shiru har yanzu..gaskiya dole ne na duba ki in san abinda ke faruwa...".
" Ni dai a a...".
" Ni kuma nace Erh...so nake nima na fara raino...kin ganin yarinyar Ishaq har ta fara 'kiran Daddy fa..gaskiya da sake dole in san abin yi...".
Har yanzun idanun ta a lumshe tace" Ka kar6o mana aron ta kawai mu zauna da ita shikenan ka samu abin rainon ka...ni kaga dama ba so nake in sake haihuwa ba..".
'Bata rai yayi nan take..da 6acin rai yace" Baki da hankali...".
" Dagaske ban so ni".
" Nuree ban son shirme..."
Zatayi magana yayi saurin dakatar da ita.
'Karfi yasa ya 'dago ta zaune sai gata daf da dashi sosai, ta firgita ma she thought marin ta zai yi sai kuma taji shiru hannun sa taji yakai 'kasan marar ta yana yawo da shi wanda hakan yasa tayi saurin bu'de idanun ta ta sau'ke su akan fuskar sa.
Murmushi taga yana yi memakon 6acin rai da taji cikin muryar sa, da mamaki sai tsaya duban sa..bakin sa ya sau'ke saman la66an ta ya sumbata gami da matsa marar tata da 'dan 'karfi sai ta saki 'kara.
A kunne ya ra'da mata" Naki albishir 'din kenan...".
" Me hakan ke nufi wai?"
Ta tambayi kanta mamaki 'karara kan fuskar ta...hannun ta ta kai kan nasa itama ta shafo cikin sai yace mata" Kinga ikon Allah ko..dama mugunta kike so kiyi min baki san Allah na so na ba...ba tun yau na fahimci kina 'dauke da ciki ba kawai gudun ruwan ki nake son gani dan naga alamar baki da mu da rashin cikin ba ke ashe ban sani ba dagaske baki 'kauna ta..".
Shiru tayi tana jin tsananin fargaba na kamata, ita fa ba wai bata son haihuwa bane kawai tsoro take ji kar labari ya sake maimaita kansa akan abinda zata kuma haifa, shiyasa ta tilastawa kanta ha'kura da haihuwa gaba 'daya.
Allah ma sai ya dubi zuciyar ta ya ja mata lokaci har cikin eanta take jin ta ha'kura da haihuwa indai zasu yi rayuwar su a hakan dashi bazata ta6a damuwa ba koda kuwa basu da 'da ko 'ya agaban su har abada..shiyasa tun yanzu take jin tausayin abinda ke cikin cikin ta.
Hawaye ne da bata shirya musu ba taji sun gangaro saman kuncin ta..Yah Deen kam tsayawa kallon ta ma yayi sosai take bashi mamaki.
Wasa-wasa Noor sosai ta 'daga hankalin ta akan cikin duk ta tashi hankalin ta ta hana shi natsuwa, sosai yake kwantar da murya ya mata nasihar amma abanza, tsakanin ta da Allah take nuna rashin son cikin, har sai ma ya rasa yadda zai yi da ita.
Ya fahimci so take ta rabu da cikin cikin ko wani irin hali, sai da ya fito a Mu'een 'din sa ya nuna mata cewa hauka zai mata idan ta kuskura ta salwantar masa da cikin sa...kafin ta 'dan rage haukan da take yi.
Amma kullum tana cikin kuka, tunda labarin cikin ya bayyana mata basu 'kara walwala a gidan ba.
Daga 'karshe sai da batun ya kaisu har wajen iyayen su, da 'kyar Noor ta ha'kura akan zata haifi cikin bayan Anty tayi mata nasiha sosai da al'kawarin da ta haifa zata 'dauke a wurin ta...misalai da dama Antyn ta bata inda tace" Ni kaina ma babban misali nake Noor idan kin bada hankali, rana guda aka 'daura auren mu da Ammin ku amma Allah cikin ikon sa har yau bai ta6a bani haihuwa ba, nayi kuka munyi Addu'ah 'karshe dole muka ha'kura muka fawwala Allah komai, yanzu haka na riga na cire raina da samun rabo shiyasa kika ga ina ruyuwa ta cike da walwala domin ban isa in ce da Allah miye dalili ba....amma ke gashi kin samu cikin sau'ki amma kina wasa da damar ki ta hanyar ki maidawa Allah babban kyautar da yayi miki, a kaf 'din rayuwa babu abinda yakai kyautar 'da da kuma lafiya da Allah yake yi mana domin duk dukiyar ka baka isa ka siya ba har sai yaga dama, godiya ya kamata kiyi baki nuna ba fushin ki ba Noor.
Banda kuka babu abinda Noor ke yi dan a ganin ta har yanzu basu fahimce ta bane shiyasa, ita da kanta tana son taga 'ya'yan ta amma bazata juri ganin ba'ka'ken ta6o ajikin su saboda uban su ba shiyasa ta ha'kura kawai, hala sun manta da abinda ya faru da Baby ne.
Ganin ta kasa kwantar da hankalin ta ne ya sanya Ammi ta hana ta komawa Abujan ta zauna da ita tana bata kulawar da ta dace...shi kansa ma hakan yafi masa dan 'daga masa hankali take yi idan tana kusa da shi.
Kwanaki na ta tafiya cikin Noor na sake girma, sai dai zuwa yanzun Alhamdulillah ta kwantar da hankalin ta sosai saboda yawan nasihar da ake yi mata, ita kanta yanzu tasan cewa kuskure ta aikata domin kuwa duk abinda Allah ya tsara kai baka isa ka canza shi ba, wayon ta bai isa ya kawar da shirin Allah ba matu'kar ya riga yace sai ya faru.
Bayan wata tara da 'yan satikai ta haifo yaranta kyawawa guda biyu mace da namiji...inda yaron yaci sunan Alhaji Baba amma ana 'kiran sa da _Affan_ macen kuma sunan Anty Zainab aka sanya mata se ake 'kiran ta da suna _Farrah_ .
Tunda ta haife su kuma saj taji 'kaunar abinta ya sake kamata, haka ta cigaba da rainon abinta bata 'kara nuna musu 'kyama ba Addu'ar ta ayanzu kawai shine Allah ubangiji ya raya mata su ya kuma basu kariya a duk inda suke...
*****
_Bayan shekaru biyu_
Tsaye take a kitchen da tu'ke'ken cikin ta hannun ta wu'ka ne tana slizing green beans a hankali dan kar ta kuskure.
Gidan shiru cuz yaranta duk basu nan, Affan na can wurin Ammi yayin da Farrah aka yi can gaba da ita wurin Anty Zainab tuni an tattara mata kayan ta can, hakan yasa banda 'karar T.v dake aiki a parlour baka jin komai sai ko kuma idan kayo hanyar kitchen kaji kwarabniyar da take yi.
Tana daga kitchen 'din tajiyo muryar sa yana 'kiran sunan ta kamar wanda akace masa bata gidan ne.
" *Nureen-Deen* !"
Ya sake anbata a karo na uku.
Noor bata amsa ba illah murmushin da take yi daga inda take tsaye tana mai cigaba da aikin ta.
Yanzun fa ya fita zuwa masallaci kuma yasan aiki take a kitchen amma yake ta fama 'kwala 'kiran sunan ta.
Kitchen 'din ya nufo sai ya tsaya daga bakin 'kofa ya wani kama kunkumi..gira ya 'dage da alamun 'kosawa yace" Ya ina ta 'kiran Nureen-Deen amma bata amsa ni ba?"