Sashe 202
Idan An Ciza Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
da ewa amman dai ba ta bashi fuska ba, yana ta bin ta sai yanzu ne ta bashi daman a takaice tana so ta yi aure kuma ba har ya je kano ya ga an'uwanta yanzu ma haka gobe a ke son a je can kano a aura auran amman ta ce a dakata mata sai ta yi magana da janin mijinta da wwar mijinta da kuma Yayanta, to azu ta yi mgana da Daddy ya ce abu ne mai kyau daman zamanta haka ba da i, Hajiya ma ta ba ta dukkan goyon baya, ita ta ma yi garaje ne tana ganin kamar in ta kawo maganar Murja ba za ta amince ba, amman har ga Allah taso Hamza ya auri murja amman tunda har ta daidaita da wani sai ba ta kawo mganar Hamza ba, ta ba ta dukkan goyon baya. Ita yanzu tana son jin ta bakinsu ba, su anta ne suna da ha in ta sanar da su kafin auran ita ta ce ma adakata amman in ta waliyyanta ne da tun zuwan farko an aura mata aure da Al ali Mustapha Tafida, matarsa aya yayansa biyar amman duka sun yi aure kawai shi dai ya na son Barrister Murja ne amman arin aure ba shi cikin tsarinsa matarsa likita ce tana aiki a wani babba asibiti anan garin Abuja. Gaba aya sun kasa mgana saboda lamarin ne ya zo musu a bazata. Ban da Dr da ya yi mirmishi kafin ya ce"Haba Mommy don za ki yi aure sai ki ce sai kin nemi yardan mu? Mun san cewa tunda Abi ya rasu wata rana za ki yi aure tunda ke ma kina bukatar Kyakyawan rayuwa anan gaba, mu ma a matsayin mu na anki hankali mu zai kwanta sanin kina ashin wanda zai kular mana da ke, sannan a kallah bayan Abi in kara samar mana gur ara kiran wani da sunan uba." Mommy sai kawai ta fashe da kuka, Hajiya ma sai da ta share kwallah tana fq in"Allah ya yi maka albarka Sulaimanu, ban ta a ganin mai hankali kamar ka, kaf cikin ayan Murja ba kamar ka, Allah ya raya maka zuru'a shi kuma babanku Allah ya ji ansa da rahama." Ya amsa da Amin ya na mirmishi kafin ya tashi ya arisa kusa da Mommy ya zauna ya na lallashinta, Mimi ta ji abun a ranta domin Abi kawai ta tuna amman ba ta jin za ta iya cewa kada Mommy ta yi aure, amman har ga zuciyanta sai ta ji zafin auran da Mommy za ta yi. Bangaren su Khadi kuwa ba wanda ya san abin da ke ransu sai da Hajiya ta kalle su kafin tace" Ku ba ku ce komai ba? Ba yardan ku ta ke nema ba, kawai dai ta gaya muku ne saboda kuna da ha in ku sani ku saka mata albarka mahaifiyarku ce ba ku da kamarta, kun dai ji kalaman yayan ku? To kuma ku yi ko yi da shi." Madiha ce ta girgiza kanta kafin ta ce"Tsaya tsaya Hajiya ni fa ban gane ba, shin Mommy za ta yi aure gobe? To menene amfanin gaya mana ba yardan mu take nema ba, tunda ko mun ce a'a ba abin da za'a fqsa. Maganar gaskiya ni ban goyo bayan wannan auran na Mommy ba, me ta nema ta rasa? Me take bukata? Abi ya rasu ko shekara biyar bai yi ba Mommy kin manta da shi za ki je ki auri wani, kuma ki sakamu mu kira shi da sunan Baba, gaskiya Mommy ba zan iya miki wannan biyayyar ba, ba da yawun bakina a wannan auran na ki ba sannan ni uba na aya ne ya rasu bayan shi ba ni da wani uban kuma." Daga haka ta mike ta fice t na kuka, Khadi ma ta na sharan kwallah ta ce" Gaskiya ba ki kyauta ba, wani irin aure kuma? Da girman ki gotai gotai da ke kice za ki yi wani aure? duka duka yaushe Abi ya rasu da har kin manta da shi za ki yi wani auren? Ni ma gaskiya ban yarda ba kuma ban amince da wannan auren ba." Itama tashi ta yi ta fice ta na kuka Sulaiman na kiranta amman ta i sauraran shi, Hajiya ta girgiza kai ba ta ce komai ba, daman ta san haka zai faru, Momny kuma tana ta kuka Mimi kuma ta kasa mgana kanta na asa amman a cikin ranta itama ba ta son auran da Mommy za ta yi amman ta kasa mgana, Hajiya ta kalli Mommy lokaci aya tana fa in" Murja ki daina kuka, su ai ba su isa su hanaki aure ba, in kika biye ma yaran nan marasa jin mgana sai dai ki are a haka, su ba'a aure suke zaune a gidan mazajasun? Ba na son iskanci da wawanci." Mommy ta ago ta na kallon Mimi kafin ta ce" Mimi ba ki ce komai ba? Ke ma kina ganin na manta da babanku ko na ci Amanar sa ne? Ganin yadda Mommy ke hawaye ya sa Mimi ta girgiza kanta kafin tace"A'a Mommy. Ni ban san me zan ce ba. Amman dai ba zan hanaki aure ba tunda kina so Allah ya sanya alheri, amman ina so ki ba ma su Khadi lokaci za su sauko daga baya.." Ta na gama fa in haka itama ta fita Mommy ta ta shi za ta bisu Sulaiman ya hana ta ya ce shi zai je ya same su, nan ya ta shi ya fita ya bar ta da Hajiya tana ba ta baki. akin da Madiha ta sauke ya iske su sun ha a kai suna kuka har da Mimi nan ya zauna ya na jawo hankalinsu da nuna musu falalan auran da Mommy za ta yi amman Madiha cikin araji ta ce" Ban amince ba, domin ban ga wata falala a auran Mommy ba, da girmanta ne sai ta yi wani auren? a she ba ta son Abi tunda har da mutuwansa ba da ewa take tunanin sake auran wani Nlnamijin." Tana fa a khadi na fa a. Sun i sauraran sulaaiman, Allah ya kawo Inna ZAINABA ta yi musu wankan tsarki ta karishe da cewa"Wato ita ba mace ba ne sai kada ta yi aure, ta zauna ta cigaba da takaban uban ku yana kabari ta are rayuwanta a lalace ko? To ba ku isa ba tunda Allah ya ba ta wannan damar wlh sai Murja sai ta yi aure ta samu natsuwa, ku na gidan auran ku ina ruwan ku da auranta? In ba'a aure ku me ya sa kuka yi? Ai mace ba ta wuce aure in ba mutuwa ta yi haka namiji, ina laifi ta zauna tsweon shekara uku ba aure, in da ace yau ita ce ta raau na tabbata in uban ku ya yi mata hallaci ta yi shekara a asa tuni zai ara aure sai mace ce a ke ganin laifinta bayan ta rasa miji ta ce za ta yi aure sai ace gotai gotai da ita ko? Shi amman namiji ko an shekara ari ne ba mai damuwa da shekarunsa sai ma a aura masa budurwa ba wanda zai ce wani abu, to bari ku ji na gaya mu ku, ko da yardan ku ko ba yardan ku wlh Murja ta gama zama matar aure a gobe in sha Allahu wanda ya ji haushi ya yanke ta kada ya sake nemanta, ku ne za ku ta e domin ita sha kudum ce tunda kuka bari ta haifeku ta zama uwarku." Haka ta ke ta fa a da Dr ya ba ta hakuri ne ta sassauta amman sai da ta ce"Raina ne ya aci Sulaiman, ku ba yara ba kowace da mijinta da yayanta amman kuma ku ce murja kada ta yi aure? To ta zauna zaman ubanku a cikin gida? Wlh ba ku da tsausayi, daman na san ko kowa bai ce wani abu ba sai kin ce baki yarda ba, tunda daman ba ki da zuciya mai kyau, To mu zuba mu gani shege ka fasa." Ta tafa hannu bayan ta gama nuna Madiha da yatsa, sannan ta yi tsaki ta fice Sulaiman kuma kalaman bakinsa sun are sai tashi ya yi shima kawai ya fita. Mimi ce mai sau i sau i itama haka su Madihan suka gama saka mata na su tunanin a ranta har ta ji itama tana jin haushin Mommy, A akin nan suka kwana ko Ummi sai da asuba Inna Zainaba ta kawo ta, ta ce ta ba ta Nono kafin ta yi mata wanka. Suna cikin akin nan ko karyawa ba su yi ba. Sai da Dr ya sake dawowa ya lallashe su amman ba su ji ba gwara Mimi ta sha tea sannan ta ci dankalin da Asmauu ta soya ko saboda goyo. Sannan ta saki fuska har ta je ta gaida Hajiya da Mommy da duk idanuwanta sun kumbura saboda kuka Hajiya ta kalli Mimi kafin tabce"Binta ka da na ji ko na gani kin biye ma sakarkarun yayyenki kin sa a ma Murja, kin ji ko?. Sai ta gya a mata Hajiya sai fa a take yi Inna Zainaba na wajen ta ce"Hajiya kyalesu sai dai su mutu aure kamar an yi an gama." Mommy daman a jiyan ta ce ita ta fasa Inna Zainanba ta dira kanta da fa a da cewa"Sai zauna ki koma baya kina bin a sai abunda suka ce aure fa ba mai tada shi na ce duk wanda ya ji haushi kada ya ara neman ki." Khadi da Madiha suka fara shirin tafiya, Sai dai misalin goma sha aya safe suka ji Inna Zainaba na sakin gu an an daura auran Mommy da wani, gaba aya sai hankalinsu ya ara ta shi, ba yadda sulaiman bai yi da su su tsaya kada su tafi ba suka i ba da asuba kafin ya wuce tunda shi ma jirgin karfe bakwai ya bi ya koma kano ya samu aurin auran Mommy. ita madiha ta samu jirgi amman Khadi motar haya ta bi zuwa Kaduna kuma ko sallama ba su yi ma Mommy ba ballantana Hajiya, Mommy ta damu Inna Zainaba ta ce kada ma ta saka a ranta su je, ma