Sashe 99
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Raihanah da tuni bacci b’arawo ya saceta cikin baccin nata takejin ringing d’in waya yak’i k’arewa, ta bud’e idanunta a hankali yanda taji wayar naci gaba da ruri kuma ba’ada niyyan daina kira...
A hankali ta mik’e ta isa jikin table d’in nasa yanda ya mance wayar nashi gashi bai kashe ba... K’urama screen d’in wayar idanu tai yanda taga sunan wandake kiran ya bayyanada Partner, “Partner..” Ta nanata a hankali, nan ta shiga tunanin kalmar tana sosa idanunta da bai ida wartsakewa daga d’an baccin da tai ba, sam tunaninta bai kawo mata tace matarsa bace Partner, saima tinanin nata ya tafi wani wajen daban ta soma tunanin toh kodai work partner d’insa ne...? Toh ko dai yayi zaton a wani wajen ya mance wayar ya amshi na abokin nasa dan ya kira yaji ina ya barta bacin haka wannan kira tai yawa, bata ida tunanin ba kiran ya kuma shigowa... Still tai tana kallo wata zuciyar na cewa toh ki d’aga kiji wannan kira k’ila ba lafiya ba... A hankali tasa hannu ta d’aga wayar sallama saman bakinta ga muryar tata da sauran bacci a ciki....
Zumbur Siyama ta mik’e daga d’aya b’angaren jin mace ta amsa wayar mijinta zuciyarta na wani irin tsinkewa....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*75*
“Wacece ke...?” Kalmar da Raihana taji an fad’i kenan daga d’aya b’angaren... Tamkar wacce aka zabura haka tai zumbur ta ware idanunta, ragowar baccin taji ya watse, lokaci guda ta nemi baccin da takeji ta rasa... Kasa furta komai tayi sai raba idanu da take tamkar mage a tukunya....
Siyama da tuni jikinta ya d’auki rawa sabida tsananin tashin hankali da kishi da suka sauk’ar mata lokaci guda, cikin wani irin murya mai cikeda kaushi take kuma furta “Nace wacece ke...? Sannan mai ya had’aki da wayar mijina..?!!!”
Jin Siyama ta ambaci wayar mijinta ya kuma sa gaban Raihana fad’uwa, k’irjinta tamkar wacce aka ije mata k’aton dutse... Cikin sauri ta cire wayar daga kunnenta tana duban screen d’in, k’ara karanta sunan tai Partner... Da sauri ta rintse idanunta tana mai dafe kanta da jinjna wauta irin tata, sam bata kawo sunanta Partner matarsa ya sakawa ba... Tana jiyowa daga can b’angaren Siyama naci gaba da fad’in hello hello... Bata iya amsata ba sai katse kiran da tayi cikin sauri, ta koma mazauninta da sauri tana mai ci gaba da rarraba idanu don haka kurum muryar matar tasa ya mugun firgitata....
A can kuwa Siyama tsaye ta mik’e tana kuma neman layin Sameer but still ba’a d’agawa, k’oluluwan tashin hankali takai, a iya rayuwarta abinda take tsoro ace Sameer ya soma biye biyen mata, a yanda take da muguwar kishin mijinta tabbas tasan zata iya yin komai to keep him all alone for herself.... Aunty Lami ta kafeta da idanu kana ta d’an gyara zama had’ida matsowa kusan Siyama da gaba d’aya bata a hayyacinta kana tace “Ya mijin naki....?”
Wani irin duba Siyama ta watsa mata ba tareda tace komai ba....
Aunty Lami ta murmusa, tsaye ta mik’e ta matsoda bakinta saitin kunnen Siyama, cikin sigan rad’a take furta “Kiyi hattara da ahalin gidan nan suna gab da rabaki da Sameer, amma shawarice idan kin d’auka....” Tana ida fad’in haka ta saki murmushi kana ta fice salin alin.... Kallo Siyama tabita dashi har ta b’ace ma ganinta kafin ta fuzar da iska mai zafi...
Muryar wata Dattijuwa ce ya katseta daga duniyar tunanin neman mafitawa rayuwarsu ita da Partner da tai.....
Nabilah na rik’eda Mamani yayinda Mamani taci gaba da dogarawa tana fad’in “Wai ina kishiyar tawa takene...? Tinda kishi ya hana ta shigo ta gaidani gani nan ni zan shigo na gaidata da kaina.... Ke Mariya ina kika b’oye min kishiyar tawa ce...?”
Nabilah dake rik’eda ita tana murmusawa take furta “Kedai mu shiga daga ciki Mamani kinsan kishiyar taki taci uwar gayu tafiya ma wahala ke mata....” Ta k’arashe maganar sanda take taimakawa Mamani ta zauna saman kujerar gefen Siyama...
Banda huci da tururi Siyama bata komai, sai aikawa Nabilah kallon tsana da take, Nabilah kaw ko ajikinta murmushi ne fal fuskarta....
Gyara zama sosai Mamani tai had’ida kaikaitowa tana fuskantar Siyama, ta kuwa washe baki takai duka hannayenta biyu ta kamo hannayen Siyama, cikeda jin dad’i take furta “Allahu Akbar... Oh ni Halimatu ashe dai rana irinta yau zatazo... Ashe zanga matar Ma’aruf kafin na bar duniya... Saura kuma naga d’iyoyinsa.... Sannu kinji ‘yar nan...” Ta d’anja fasali jin Siyama ta mata dinkim bata amsata ba saima ta mujiya data zuba mata tamkar taga wani halitta daga wani planet....
Juyowa tai ta dubi Nabilah dake k’ok’arin k’unshe dariyarta Marliya na girgiza kai wa Nabilar kana Mamani tace “Ke Nabilatu Wai bata magana ne...? Kodai kishiyar tawa bihim ce... Ya ina mata magana ta zuba min wannan pici picin idanun nata kaman ni na sammata, wannan badon tsufa danai ba ma nawa idanun sunfi nata girma...”
Ta k’arashe tana mai gwalalo idanunta a fuskar Siyama wacce lamarin Mamani ya soma bata tsoro...
Daga Marliya har Nabilah kasa rik’e dariyarsu sukai...
Mamani ta juyo garesu tana fad’in “Kai bani son k’aniya... Ku fad’a min meke faruwa a nan... wacece wannan...? Idan kuma yaren da nake ne bataji kuzo ku mata wanda zataji kafin na tashi na sassab’a maku...!!”
Nabilah tai k’ok’arin saita kanta kana tace “Mamani kinsan kishiyar taki girman turai ce yawo cikin gajimare k’ila dai bata fahimtar abinda kike fad’i ne... Ki canza mata harshe...”
Mamani ta maida dubantaga Siyama wacce ta kasa d’auke idanu daga barin duban Dattijuwar kana tace “Auho kice min dangin nasara Ma’aruf ya auro... Ke kaw kinsha bamabam da Haladu yaron arziki... Da kika tashi zuwa cikin danginsa sai ki koyo yaren da suke fahimta... Fi’ilin banza da wofi, yo har ni za’a nunawa yaren jajayen kunne... Ke barikiji na fad’i miki sanda Mammadu na ke raye babu kalan hazon da bai k’etara dani ba... Yo maima kuka samu ‘yan k’arshen zamani....”
Ganin Mamani ta saki layi ta fara zuba masifa yasa Marliya duban ‘yar uwarta Nabilah da duniyar tai mata dad’i gamon da takeso Mamani da Siyama, girgiza kai kurum Marliya tai kana tace “Mamani Aunty Siyama tana saurarenki kawai dai baki bata dama tayi magana bane tintinin ke kiketa magana tin shigowarki babu ko hutawa..... Kuma zataje gaidaki kenan sai gaki nan kin shigo...”
“Ke dalla chan rufe min baki, uwar kinibibi, yo gani zabiya ko mai...? Inyi...?” Tai maganar tana mai tsare Marliya da idanu....
Cikin sauri Nabilah ta kamo Mamani tana fad’in “Mamani muje kinji zata shigo har sashenki ta gaisheki idan bata gaisheki a nan ba, wanda zai sata na dole na zuwa....” Ta k’arashe tana mai watsawa Siyama muguwar kallo....
Mamani ta mik’e tana ci gaba da sababi da yab’awa Siyama mugayen maganganu...
Suna tafe sashenta take ci gaba da fad’in “Inyi kajimin ja’irar yarinya, yo wannan badon Yayanku yace min ‘yaruwar Haladu bace sai nace babu abinda ya had’asa da wannan mai k’irar zabon, Banda Farin fata da dogon hanci banga mai Yayanku ya gani tattareda wannan mai k’irar itacen ba, ko ni nan a haka nafita kyaun gani....”
Nabilah ta gyara mata cushion tanaji Mamanin naci gaba da sababi har ta zauna kana ta umarceta ta nemo wayar salulanta ta kirawo mata Yayansu Ma’aruf gashi su Najah sunce shine yaje makaranta ya d’auki Raihanah kuma har yanzu basu dawo ba, ga wannan matar tasa mai suffan karan rake data kuma b’ata mata zuciya....
Sake kira Nabilah tai tace da ita wayar bata shiga....
Mamani ta jinjina kai tace “Ko wata duniyar yakaimin jika oho.... Kodashike jika na yaron arziki ne bazaiyi wani abu maras kyau ba, Allah sa dai lafiya suke yanda yanzu duniyar tamu ta koma....”
Nabilah ta amsada Ameen dai Mamani, k’ila kiran gaggawa akai masa daga can asibitin nasu sai ya wuce da ita....ta k’arada kinason wani abu ne...?”
D’an dubanta Mamanin tai kana tace “Kunna min talabijin na rage takaicin wancan zabuwar matar Yayan taku....”
Dariya ya kusan kufcewa Nabilah, kunna mata TV d’in tai ta silale ta fice don tanaji har lokacin sababi take....
A hankali ta mik’e ta isa jikin table d’in nasa yanda ya mance wayar nashi gashi bai kashe ba... K’urama screen d’in wayar idanu tai yanda taga sunan wandake kiran ya bayyanada Partner, “Partner..” Ta nanata a hankali, nan ta shiga tunanin kalmar tana sosa idanunta da bai ida wartsakewa daga d’an baccin da tai ba, sam tunaninta bai kawo mata tace matarsa bace Partner, saima tinanin nata ya tafi wani wajen daban ta soma tunanin toh kodai work partner d’insa ne...? Toh ko dai yayi zaton a wani wajen ya mance wayar ya amshi na abokin nasa dan ya kira yaji ina ya barta bacin haka wannan kira tai yawa, bata ida tunanin ba kiran ya kuma shigowa... Still tai tana kallo wata zuciyar na cewa toh ki d’aga kiji wannan kira k’ila ba lafiya ba... A hankali tasa hannu ta d’aga wayar sallama saman bakinta ga muryar tata da sauran bacci a ciki....
Zumbur Siyama ta mik’e daga d’aya b’angaren jin mace ta amsa wayar mijinta zuciyarta na wani irin tsinkewa....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*75*
“Wacece ke...?” Kalmar da Raihana taji an fad’i kenan daga d’aya b’angaren... Tamkar wacce aka zabura haka tai zumbur ta ware idanunta, ragowar baccin taji ya watse, lokaci guda ta nemi baccin da takeji ta rasa... Kasa furta komai tayi sai raba idanu da take tamkar mage a tukunya....
Siyama da tuni jikinta ya d’auki rawa sabida tsananin tashin hankali da kishi da suka sauk’ar mata lokaci guda, cikin wani irin murya mai cikeda kaushi take kuma furta “Nace wacece ke...? Sannan mai ya had’aki da wayar mijina..?!!!”
Jin Siyama ta ambaci wayar mijinta ya kuma sa gaban Raihana fad’uwa, k’irjinta tamkar wacce aka ije mata k’aton dutse... Cikin sauri ta cire wayar daga kunnenta tana duban screen d’in, k’ara karanta sunan tai Partner... Da sauri ta rintse idanunta tana mai dafe kanta da jinjna wauta irin tata, sam bata kawo sunanta Partner matarsa ya sakawa ba... Tana jiyowa daga can b’angaren Siyama naci gaba da fad’in hello hello... Bata iya amsata ba sai katse kiran da tayi cikin sauri, ta koma mazauninta da sauri tana mai ci gaba da rarraba idanu don haka kurum muryar matar tasa ya mugun firgitata....
A can kuwa Siyama tsaye ta mik’e tana kuma neman layin Sameer but still ba’a d’agawa, k’oluluwan tashin hankali takai, a iya rayuwarta abinda take tsoro ace Sameer ya soma biye biyen mata, a yanda take da muguwar kishin mijinta tabbas tasan zata iya yin komai to keep him all alone for herself.... Aunty Lami ta kafeta da idanu kana ta d’an gyara zama had’ida matsowa kusan Siyama da gaba d’aya bata a hayyacinta kana tace “Ya mijin naki....?”
Wani irin duba Siyama ta watsa mata ba tareda tace komai ba....
Aunty Lami ta murmusa, tsaye ta mik’e ta matsoda bakinta saitin kunnen Siyama, cikin sigan rad’a take furta “Kiyi hattara da ahalin gidan nan suna gab da rabaki da Sameer, amma shawarice idan kin d’auka....” Tana ida fad’in haka ta saki murmushi kana ta fice salin alin.... Kallo Siyama tabita dashi har ta b’ace ma ganinta kafin ta fuzar da iska mai zafi...
Muryar wata Dattijuwa ce ya katseta daga duniyar tunanin neman mafitawa rayuwarsu ita da Partner da tai.....
Nabilah na rik’eda Mamani yayinda Mamani taci gaba da dogarawa tana fad’in “Wai ina kishiyar tawa takene...? Tinda kishi ya hana ta shigo ta gaidani gani nan ni zan shigo na gaidata da kaina.... Ke Mariya ina kika b’oye min kishiyar tawa ce...?”
Nabilah dake rik’eda ita tana murmusawa take furta “Kedai mu shiga daga ciki Mamani kinsan kishiyar taki taci uwar gayu tafiya ma wahala ke mata....” Ta k’arashe maganar sanda take taimakawa Mamani ta zauna saman kujerar gefen Siyama...
Banda huci da tururi Siyama bata komai, sai aikawa Nabilah kallon tsana da take, Nabilah kaw ko ajikinta murmushi ne fal fuskarta....
Gyara zama sosai Mamani tai had’ida kaikaitowa tana fuskantar Siyama, ta kuwa washe baki takai duka hannayenta biyu ta kamo hannayen Siyama, cikeda jin dad’i take furta “Allahu Akbar... Oh ni Halimatu ashe dai rana irinta yau zatazo... Ashe zanga matar Ma’aruf kafin na bar duniya... Saura kuma naga d’iyoyinsa.... Sannu kinji ‘yar nan...” Ta d’anja fasali jin Siyama ta mata dinkim bata amsata ba saima ta mujiya data zuba mata tamkar taga wani halitta daga wani planet....
Juyowa tai ta dubi Nabilah dake k’ok’arin k’unshe dariyarta Marliya na girgiza kai wa Nabilar kana Mamani tace “Ke Nabilatu Wai bata magana ne...? Kodai kishiyar tawa bihim ce... Ya ina mata magana ta zuba min wannan pici picin idanun nata kaman ni na sammata, wannan badon tsufa danai ba ma nawa idanun sunfi nata girma...”
Ta k’arashe tana mai gwalalo idanunta a fuskar Siyama wacce lamarin Mamani ya soma bata tsoro...
Daga Marliya har Nabilah kasa rik’e dariyarsu sukai...
Mamani ta juyo garesu tana fad’in “Kai bani son k’aniya... Ku fad’a min meke faruwa a nan... wacece wannan...? Idan kuma yaren da nake ne bataji kuzo ku mata wanda zataji kafin na tashi na sassab’a maku...!!”
Nabilah tai k’ok’arin saita kanta kana tace “Mamani kinsan kishiyar taki girman turai ce yawo cikin gajimare k’ila dai bata fahimtar abinda kike fad’i ne... Ki canza mata harshe...”
Mamani ta maida dubantaga Siyama wacce ta kasa d’auke idanu daga barin duban Dattijuwar kana tace “Auho kice min dangin nasara Ma’aruf ya auro... Ke kaw kinsha bamabam da Haladu yaron arziki... Da kika tashi zuwa cikin danginsa sai ki koyo yaren da suke fahimta... Fi’ilin banza da wofi, yo har ni za’a nunawa yaren jajayen kunne... Ke barikiji na fad’i miki sanda Mammadu na ke raye babu kalan hazon da bai k’etara dani ba... Yo maima kuka samu ‘yan k’arshen zamani....”
Ganin Mamani ta saki layi ta fara zuba masifa yasa Marliya duban ‘yar uwarta Nabilah da duniyar tai mata dad’i gamon da takeso Mamani da Siyama, girgiza kai kurum Marliya tai kana tace “Mamani Aunty Siyama tana saurarenki kawai dai baki bata dama tayi magana bane tintinin ke kiketa magana tin shigowarki babu ko hutawa..... Kuma zataje gaidaki kenan sai gaki nan kin shigo...”
“Ke dalla chan rufe min baki, uwar kinibibi, yo gani zabiya ko mai...? Inyi...?” Tai maganar tana mai tsare Marliya da idanu....
Cikin sauri Nabilah ta kamo Mamani tana fad’in “Mamani muje kinji zata shigo har sashenki ta gaisheki idan bata gaisheki a nan ba, wanda zai sata na dole na zuwa....” Ta k’arashe tana mai watsawa Siyama muguwar kallo....
Mamani ta mik’e tana ci gaba da sababi da yab’awa Siyama mugayen maganganu...
Suna tafe sashenta take ci gaba da fad’in “Inyi kajimin ja’irar yarinya, yo wannan badon Yayanku yace min ‘yaruwar Haladu bace sai nace babu abinda ya had’asa da wannan mai k’irar zabon, Banda Farin fata da dogon hanci banga mai Yayanku ya gani tattareda wannan mai k’irar itacen ba, ko ni nan a haka nafita kyaun gani....”
Nabilah ta gyara mata cushion tanaji Mamanin naci gaba da sababi har ta zauna kana ta umarceta ta nemo wayar salulanta ta kirawo mata Yayansu Ma’aruf gashi su Najah sunce shine yaje makaranta ya d’auki Raihanah kuma har yanzu basu dawo ba, ga wannan matar tasa mai suffan karan rake data kuma b’ata mata zuciya....
Sake kira Nabilah tai tace da ita wayar bata shiga....
Mamani ta jinjina kai tace “Ko wata duniyar yakaimin jika oho.... Kodashike jika na yaron arziki ne bazaiyi wani abu maras kyau ba, Allah sa dai lafiya suke yanda yanzu duniyar tamu ta koma....”
Nabilah ta amsada Ameen dai Mamani, k’ila kiran gaggawa akai masa daga can asibitin nasu sai ya wuce da ita....ta k’arada kinason wani abu ne...?”
D’an dubanta Mamanin tai kana tace “Kunna min talabijin na rage takaicin wancan zabuwar matar Yayan taku....”
Dariya ya kusan kufcewa Nabilah, kunna mata TV d’in tai ta silale ta fice don tanaji har lokacin sababi take....